Chapter 53
Chapter 53
ya fada yana lalubar wayarshi dake aljihun rigarsa. *_GUDUN QADDARA guzurin taddata....._* Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke wadda ta fito tun daga zuciyarta,ta sauke idanunta kan tafin hannunta tana bitar maganganun nuradden daya gama furta mata ayanzu,dauta dauko na anty zubaida data gama gaya mata jiya,kusan maganganun nasu sunyi kamanceceniya da juna,a yanzu bata da wata mafita bata da wani uzuri kaman yadda anty zubaida tace mata,imma dai ta baiwa nuradden dama wa imma ta sallameshi hakanan ya daina wahala,ko ga ummanta madai wannan karon ta matsa qwarai kan ya kamata ta tsaida manemi tayi aure,tunda dai abinda ya farun da ita bawai qarshen rayuwarta ya kawo ba,saima sabon babin rayuwa daya sake bude mata,idan ta sallami nuradden bata jin akwai wani qwaya daya cikin samari dama masu auren dake kara kaina akanta da zata iya kwatanta rayuwarta ta wanzu tare da tashi "Na amince nuradden....Allah ya zaba mana abinda yafi alkhairi" hannayensa gaba daya ya hada ya rungume a qirjinsa yana lumshe idanunsa,wani farinciki da baisan a wanne mizani zai dorashi ba ya shiga dawainiya dashi,sai kawai ya zame saman gwiwoyinsa a gabanta "Shahida,ki fadamin me kikeso na baki ladan wannan kyakkyawan albishir din naki?" Kai ta kada kawai qwalla na taruwa a idanunta,murmushi mai cakude da alamun son yin kuka na kubcewa saman fuskarta "Babu abinda zaka bani face nace kayi qoqari karka sa na sake yin nadama da dana sani a rayuwata karo na biyu" "Koda baki roqi haka ba wannan duty na ne" da ido kawai ta dinga bishi yadda ya rasa inda zai tsoma ranshi ya dinga bata mamaki,harta daina mamaki ma abun ya soma bata dariya,sai daya tabbatar ta dan saki ranta sannan yace "Yanzu yaushe za'a kai maganata katsina?,shine abu daya da zai sake sawa in samu nutsuwa a raina,in kuma tabbatar na yiwa duk wani dake da buri ko hanqoran mallakarki na masa fintikau din da dole ya haqura" murmushi ya qwace mata,tasan cewa burinsu daada kenan,tana da tabbacin indai nuradden ya isa katsina to magana ta qare,don ba wani lokaci zasu ja ba ba tare da sun bashi ita ba "Karka damu duka abun bana sauri bane,next month za'a dauki azumi,sai kayi haquri mu barwa salla" fuska yadan bata "Gaskiya yayimin nisa,saidai idan har kin yarda ne ni zan kaiki,qafarki qafata"hannu ta daga tana murmushi "Shikenan naji,sai kuma me?" "Aikin gama min komai nikam,yau nafi kowanne namiji dake fadin duniyar nan sa'a" yayi furucin a sanda yake kallon sararin samaniya cikin madaukakin farinciki. Qarfe tara ta shiga gida don bata wuce hakan a waje,duk da dama ba fita take wajen kowa ba,kusan nuradden din ne kawaima yaci qwallo da har take fita ta saurareshi,ga mamakinta saita tadda anty zubaida zaune saman kujerar falon hannunta daya tallafe da kanta,gwiwar hannunta saman hannun kujera,ba kowa falon sai ita kadai,kallon wani series da suke haskowa a mbc take,sallamar shahidan ya sakata dagowa da sauri tana dubanta "Anty,yau yana sameki a nan?" Qoqarin daidaita kanta tayi "To ya zanyi,uncle dinki yace lallai lallai naga shigowarki na tura masa ke" murmushi tayi tana zama hannun daya kujerar dake daura da anty xubaidan "Hala anty kinkai masa qarata ne kan nuradden?,to kisha kuruminki,na riga na baiwa nuradden dama,zuwa nan da qaramar sallah xai isa gasu daada in sha Allahu" ta qarashe tana duban anty zubaida,don tasan ta gama mata abinda ranta keso kenan,sai taga ta murmusa kadan "Ya za'ayi nakai qararki?,koda nakai dinma ai Allah abinda ya hukunta dole shi zai faru ko?,yanzu dai kije yana falonshi yana jiranki" sai data miqe sannan tace "Anty muje tare mana don Allah" "Ba ruwan zubaida" ta fada da hanzari,dariya ta baiwa shahidan yadda tayi maganar kamar wata baquwar uncle hisham din,saita juya ta wuce tana cewa "Ai shikenan anty". "barka da dare uncle"shahida ta furta sanda ta nutsu a gaban uncle hisham,ya sauke takardar da yake dubawa ya kalleta "barka kadai shahida,sai yaushene zakuyi hutun naku kamfanin?" "Eh to uncle gaskiya ina zaton sai sai dab da sallah,saboda wannan season ne na yawaita da kuma cunkoson custumers" kai ya jinjina sannan ya danyi shuru kamar mai nazari kafin daga bisani yace "Daada ce keda buqatar kije,to ban sani ba ko xaki samu ko weekend ne kije kiji kiran nata na meye?" "Shikenan uncle babu damuwa,yau alhamis ranar juma'a tunda da wuri muke barin kamfani saina shirya naje,idan yaso ran lahadi da yamma saina dawo" "Hakan yayi,shikenan dama kiran" "To uncle saida safe" ta fada tana miqewa "Allah ya bamu alkhairi". A inda tabar anty xubaida nan ta taras da ita,saita daga kai tana kallon shahidan,ganin babu sauyin fuska tattare da ita ya tabbatar mata uncle din bai gaya mata komai ba,zai turata ne kaman yadda dada ta buqata,sallama anty zubaidan tayi mata ta wuce wajen uncle din,tabar shahidan na sake sabon xaman ganin maimaicin wani shiri,tana mitar baccin wuri da yau su faruqu sukayi suka barta ita daya,don bata jin dadin zaman falon ita kadai. A nutse yake murza motarsa tamkar wanda baison barin titin har zuwa sanda ya isa unguwarsu anty usaina,cikin nutsuwa ya faka motar sannan ya kasheta ya fito,cikin wani irin karsashi yake takawa zuwa cikin gidan,haka kawai yake jinsa kaman mai yawo cikin farin gajimare wanda shi kansa baisan dalilin haka ba,yana shirin saka qafarsa kan step qwaya daya da zai sadashi da falon gidan ya jiyo muryar sa'ida na kiranshi,a nutse ya waiwaya,sai ya tsaya hannayensa zube a aljihun wandonsa yana dakon qarasowarta. Aladabce ta rusuna tana gaidashi ya amsa yana dubanta "Daga ina kike?" Sai data dan waiwaya sannan ta dawo da dubanta wajensa "Uncle....gidansu anty shahida,ummi ta aikeni na amso mata saqo?,kasan me uncle?" Kai ya girgiza yana dubanta "Na ganta mafa tazo wajen mamansu,uncle kaganta kuwa kaman ba ita ba...."takun data jiyo ya sanyata tsuke bakinta,cikin minti daya anty usaina ta bayyana,akwai 'yar tazara tsakaninsu kadan,ya juya ya dubi sa'idan "Wuce kafin tazo ta fara miki jajayen idanuwa" maganar ta baiwa sa'ida dariya har sai data qyalqyale da dariya sannan ta soma takawa don wucewa ciki "Wato kin dawo shine kika samu waje kika tsaya kina masa wannan dan banzan surutun naki ko?"kai ta gyada " a'ah ummi,nima fa yanzu na shigo"harararta tayi cikin ranta tana qissima lallai ya zama dole ta kwabi sa'ida,donta fuskanci kanta yana rawa tanason ta lalata mata plan "Wuce,saura kuma naga qafarki a wajen" da hanzari sa'idan ta wuce,anty usaina ta bita da kallo harsai data shige sannan ta dauke idanunta,dai dai sanda anwar yake tsaye daga inda yake,a nutse yana karantar duk wani motsi na anty usaina,murmushi ya kubce masa,ya gama ganeta tsaf,ya gama karantar tsoronta,ya kuma gane me take boye masa,saidai baisan nata shirin ba,koma meye nata shirin shi zai mata ba zatan da bata tsammata ba,idonta ta sauke a kanshi,tana tsaye har ya isketa "Yaushe kai kuma ka dawo?,daga wuni daya sai kwana har biyu?" "Tun jiya na dawo,wasu sabgogi ne suka riqeni,duk yadda naso in shigo baiyiwu ba" bata ce komai ba ta bude qofar falon ta shiga yabi bayanta. Bayan sun gama gaisawa suka shiga hirar mutanen garin daya baro ya gaya mata kowa lafiya sannan yace "Kin tambayeni lafiya na tashi zuwa katsina ba yadda na saba ba" ya fada yana duban anty usainan dake yankan farcenta "Eh ai dole,koma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96