Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 27

Chapter 27

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,294 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

waje yaci karo da mutum uku cikin maqotansa "Yauwa malam nuraini...dama yanzu muke neman yaron da zai mana sallama dakai" qoqarin dai daita fuskarshi yayi ya basu hannu suka gaisa "Ashe haka abu ya faru?,wallahi sam bamuji dadi ba,yarinyar da kowa ke mata kallon hankali da nutsuwa" daya daga cikin maqotan nashi da ake kira da malam sallau ya fada "Wallahi kuwa malam sallau,amma nidai ina kyautata zaton sharrin qawaye ne tunda kowa ya shaidi nutsuwar yarinyar....amma cire ciki aiba qaramin abu bane,sanda haruna ke gayan qaryatashi nayi saida yatabbatar min da kunnensa yaji saurayin yana fada" a hautsine abban shahida ya dago yana musu wani bahagon kallo,kusan bai fahimci me suke fada ba gaba daya "Yata shahida ce tayi ciki harta cire?" Sai suka koma kallon kallo tsakaninsu,malam sallau ya dubi abban "Errrhmmm malam nuraini kodai mata sun maka irin halin nasu ne an boye maka bakasa me yake faruwa cikin gidanka ba?,banda haka wannan zancan ai ya karade unguwarnan daga daren jiya zuwa safiyar yau" "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un" ya dinga maimaitawa yana dafe da kanshi,me yayi jama'ar unguwarsu haka sa cikin qanqanin lokaci zasu jefi diyar cikinsa da wannan sharrin,kansa ya dafe da yaji ya soma juya mishi sai kawai ya juya zuwa cikin gida "Allah ya tsare gaba ya kiyaye" ya juyo malam sallau yana fada cikin daga murya,dai dai sanda shahida data fito don shiga bayi ta kama ruwa ta saki butar hannunta cikin tsananin tashin hankali ta koma dakinta,dukka jikinta rawa yake,tana tariyar kalaman da saurayin ya dinga fada bayan ya saketa a qofar gidan,kenan duk abinda ya fada sun yarda dashi?,kenan yanzu kallon da kowa zai dinga mata?,innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,Allahumma ajirni fi musibati wa akhlifni khairan minha"shine abinda ta dinga maimaitawa kenan. Cikin kwana biyu kacal ta rame ta fige ta fita a hayyacinta,bata taba tunanin akwai tashin hankalin daya wuce na fadan iyayenta ba saiga wanda ya ninkashi ya risketa,duk ta silar kaucewa wancan bacin ran ashe zata fada wanda yafi wancan tsanani rusa farinciki dama ruguza rayuwa gaba daya. Ba ita kadaiba gidanma gaba daya ya zama shuru,baya ga abinda ya faru abbanta ya kwanta ciwo sosai tun randa su sallau sukazo masa jaje,wanda ba komai bane ya taba ranshi irin maganar da suka furta,qarshe da aka aunashi jininsa ne yayi mugun hawa,hakan ya saga hankalin ummanta itama ta shiga wani sabon tashin hankalin da firgici. Kwana uku amma shahidar jinta take akwai ya babu,gata nan dai kawai amma komai ya fice mata aka,ranar kwana na ukun da yammaci wani yaro yayi sallama tsakar gidan nasu dauke da takarda wanda yace gashi a baiwa shahidan. Mubina ce ta bita har cikin daki a sannan tana kwance saman abun sallah ta miqa mata,saita saka hannu kawai ta amsa ta aje saman kanta tana ci gaba da lazuminta,wanda kusa fiye da rabi istigfari take da salatin annabi. Sai data idar sannan ta dauko envalope din,tana daga kwance ta farketa,takarda ce qwaya daya a cikinta ta fado,sai wata azurfarta guda biyu data siya ta baiwa anwar ajiya,da sauri tasoma warware takardar tana zumudin jin daga gareshi,don tunda abun ya faru taji dif daga bangarensa,tana zaton wala'alla yazo ance mishi bata da lafiya,don bata da maraba da mai lalurar,ita kuma wani kunya da nauyin kiranshi take,gani take kaman daga muryarta zai karanci komai,zai karanci halin data fada,wasiqace cikin rubutun anwar din mai tsari _Basai nayi miki sallama ba don baki cancanceta ba,saqo nake son isar miki dama ba wani mai tsaho ko yawa ba,shahida,sam baki dace dani ba,kuma sam bakiyi dai dai da rayuwata ba,tuntuni ina zaune dake ne kawai don bani da abinyi kuma bani da wata qwaqwaqwarar sana'a,gashi ina da buqatar macen da zan di ga rage dare a wajenta,to zuwa yanzu al'amura son suma yimin kyau,bana jin zan iya ci gaba da zama dake,ki sani ni muhammad anwar ban taba sonki ko qaunarki ba,na miki alfarma ne kawai a baya,kuma ki saka a ranki cewa baki taba soyayya da wani mai kama dani ko suna na bar har qarshen rayuwarki,wasiqar na tafe da guzurin sabuwar masoyiyita wadda nake da tabbacin ta fiki komai,idan nace komai ina nufin komai da komai da kikasan diya mace na mallaka_ Cikin rawar jiki ta miqe zaune dungurgur,sannan ta jawo envalope din ta sake lalubawa ciki,saiga hotuna guda shida rigis sun fado,dukkaninsu anwar ne cikin hotunan da wata matashiyar budurwa cikin kyakkyawar shiga ta alfarma,kana musu kallon farko zaka tabbatarwa kanka lallai masoya ne da sukayi zurfin cikin qaunar juna,saboda yadda kowanne ke kallon danuwanshi cikin fara'a da shauqi,sosai ta tsurawa fuskar yarinyar ido zuciyarta na wani qara gudu tamkar zata faso qirjinta,suya zuciyar tata take mata tanason yin kuka amma bataji koda alamarsa ba bare yazo,nazarin fuskar yarinyar take take ta tuno inda ta santa,ranar bikin umaima,ranar bikin umma zaune gaban motar daya amso don ya kaita ya daukota,saita saki hoton tana girgiza kai tare da laluben wayarta duka lokaci daya,tamkar tababba take zancan a fili ita kadai "Nasan wasa kake min ya anwar ba zamu taba rabuwa....nasan wani ya kaima labarin abinda ya faru dani,ranka ya baci ka furta min wannan kalaman saboda kishina da kake" maganar tata ta katse sanda wayar ta shiga ta soma ringing. Wata murya daban ta dauka,cikin matuqar sauri da zaquwa tace "Don girman Allah ka taimakeni ka bawa anwar" dan jimmm yayi cikin tunani,don a yanzun bayajin anwar din zai iya wata dogon magana,tunda Allah yasa suka miqashi asibiti yayi kwanaki biyunsa cur ya farfado yace a dawo dashi gida yazo ya dauke wata envalope dashi kansa muhsin baisan meye a ciki ba ya adana yake zaune waje daya,kana kallon yanayin fuskarsa kasan ya dulmiya cikin wani qunci,iein quncin dake kama zukata ya riqe tamau ya dinga yankarta a hankali yana saka rudani damuwa da baqinciki mai yawa a rayuwa,irin baqincikin dake tasiri kadan kadan daga ruhi zuwa gangar jiki ya illata mutum ta farat daya ba tare da an ankara ba. Miqa masa wayar yayi,sai daya daga idanunsa da suke nuna alamun gajiyawa da damuwa ya dubi muhsin sannan ya maida kan wayar,hannu ya saka a hankali ya masa,muhsin ya sakar masa yana tashi gami da cewa "Bari naje gida na dauko wayata na barta a chargy" kai kawai ya iya gyada masa yana kara wayar a kunnensa. Abu na farko da tayi kuka ta sakar masa,wanda yake bayyana rauninta qarara,gajiyawa da rashin samun madafa,idanunsa ya runtse yana jin zuciyarsa cikin wani inji ana hautsinata sama da qasa ko zata faso qirjinsa ta fito. *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani DON GIRMAN ALLAH karki sharing,idan kina buqatar siya ki tuntubi wannan number* 07067124863 *ko kuma* 09032345899https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani DON GIRMAN ALLAH karki sharing,idan kina da buqata ki nemi wadan nan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 1️⃣5️⃣ Tamkar ana hautsinashi shi kanshi,wani irin abu ya dinga ji mai kama da tsana qyamata da haushi cike fal a zuciyarsa,wannan runtse idanun da yayi ba abinda ke gilmawa cikin idanunsa sai hotunan daya gani kwanaki hudu baya da suka shude "Dama akwai wani wani lokaci da zaizo da zaka daina sona ka juyamin baya ya anwar?" Shuru yayi ba tare daya ce komai ba,duk sanda yayi yunqurin cewa wani abu

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});