Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 24

Chapter 24

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,299 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

jin baccin,hakan ya sanya yayi tunanin ko shawara ce da ita?,baiyi qasa a gwiwa ba ya amso mata magungunan gargajiya harda na sanyi,ta amsa dai kawai ta jibge taci gaba da sha'aninta. Zuwa sannan sam abinda ke faruwa tsakanin mamanta da bbanta ya daina damunta,wani lokaci takan iya shigowa gidan ma ta taddasu sunayi tayi wucewarta daki ta kwanta abinta tahau baccinta,dukkan wadan nan sauye sauyen basu ganshi ba,ga ummanta kawai tayi mata shaidar ta koyi nunqufurci tana goyon bayan babanta,yayin da abban nata yake ganin hankali tayi ta daina damuwa da al'amarin dake faruwa. Ta bangaren fiddausi kuwa da akayi amfani da ita don cusa shahida cikin wannan harkar nasara ce a wajenta,don duk yadda aka tsara abun ya tafi dai dai,hakan yayi sanadiyyar samun kudade mai yawa daga wajen nafisa,plan dinsu na gaba shine cusa samari masu kudi 'yan duniya rayuwar shahidan,saidai duk yadda sukaso ga ganin hakan ya yiwu abun bai kasance ba,saboda sam shahidan tun asali a jininta yake,bata da kule kule,haka suka qaraci shirya plan din nasu suka gaji,hakan ya sanya suka sauya dabara,suka sake sabon shiri sabon taku da sabon tsari,wanda suke fatan shine mataki na qarshe da zai tarwatsa mu'amalar dake tsakanin anwar da shahida komai qarfinta. *_SHARRI KAYAN KWALBA_* Kusan a yanzu babu wata qawa kuma aminiya da shahida ke da ita data wuce fiddausi,kusan koda wanne lokaci suna tare,hudubar farko data soma yiwa shahida shine anwar ba son shahidan yake ba,yasha fada cewa mai zaiyi da yarinyar da iyayenta suka kasance tamkar karnuka saboda fada,sosai xancan ya daki shahida,saidai iya saninta anwar baisan badaqalar dake faruwa a gidansu ba,don tuni ta yanke yin zance dashi a gidansu bama gidansu kawai ba unguwar baki d'aya,yanzu kacokam gidan anty amina take tafiya su hadu a can,saidai kuma akace yau da gobe tafi qarfin wasa,sai maganar ta dinga tsayewa shahidan aranta,duk da cewa ko daya bata yarda ba bata gasgata ba,hakanan ba abinda ya ragu game da son anwar daga zuciyarta,duk sanda taso yin wani dogon nazari kan maganar fiddausi na kadar da hankalinta ta bata wani abun mayen sai zancan yasha ruwa. Ta gefan anwar gaba daya hankalinsa ya ta'allaqa ne kan nemawa shahida gurbin karatu cikin daya daga cikin makarantun gaba da secondry dake jahar kano tunda aka yi musu qarin albashi,bai gaya mata ba saboda yana sonne yayi mata ba zata,yaci wahala ya kashe kudi kafin komai ya kammala. Ana ya gobe zai shaida mata yana gurinta,ranar sun jima tare suna hira,sunyi hirar da suka jima basuyi irinta ba,kowanne yan jaddadawa d'an uwanshi yadda yake jinsa cikin jikinsa da zuciyarsa,sun tsokani juna sunyi raha wasa da dariya sosai,har anwar ta saka ranakun cikin daya daga cikin kundin ranakun farincikinsa da bazai taba mantawa dasu ba,ta bashi hotunan data dauka musamman sabodashi wanda ba qaramin kyau tayi cikin hotunan ba,kyanta ya fita muraran,ya qurawa hotunan idanu yaga kada kai "Wannan hotunan bazan iya maidasu enlargment ba" dubansa tayi tana narke ido tana dubanshi "Saboda banyi kyau ba ko?" Dariya ya saki yana cewa "Dama akwai wani lokaci da zaki qiyin kyau a idanuna koda wankan kashi kikayi?" Dariya sosai ya bata har shima ya tayata darawa "Dama ana wankan kashi ya anwar?" Girarsa ya dage "Eh waikoda ace anayi din...kyan da kikayi ne shahida yayi yawa,ina kishin mai aikin budawarma ya ganki" baki ta bude tana dubanshi "Ya anwar" "Shahida....kaman har yau kina kokwanton yadda nake sonki da kishinki ko?" Kai ta girgiza tana dariya "Xaki fahimta,sai ranar da aka kawoki dakina a matsayin matata" kunya ta sata sadda kai tana qiyasta ranar a ranta,gata ita dashi a matsayin miji da mata. Daya tashi tafiya saita miqo masa dari biyar bayan wata baqar leda,wadda daya bude links ne da agogo guda biyu masu matuqar kyau irin wanda tasan yana masifar so,kallonta yayi itama shi take kallo "Kada kacemin komai,na fuskanci yau miskini kake baka dako sisi(ta furta cikin sigar zolaya)"murmushi ya saki,gaskiya ta fada,don duka albashinsa ma na wajen wata uku ya qare ne wajen sama mata admission,dan abinda yaje riqewa bamai yawa bane,kudi ya dinga badawa don ta samu gurbin karatun,don yasan cikar burinta kenan shida ita,hakan bai dameshi ba ko kadan,yana jin zaiwa shahidan fiye da hakanma indai ita dince " har saika fada?"ta katse masa tunaninsa "Ina iya karantar zuciyarka ba tare daka furta abinda ke cikinta ba" ta fada cikin sanyi da taushi,sun riga da sun zama daya,sai ya saka hannu ya amsa yana murmushi "Na gode matata" kalmar data yi mata dadi sosai,cikin farinciki walwala da qaunar juna suka rabu,yana tafe yana tariyar dukka kalamanta,saiyakejin kyautar data masa tayau din daban take,hakan ya sanya ya kasa fasa kudin ya hau mota,ya taka har zuwa gida da qafa yana juya ledar data bashi gift din a ciki,gift din data bashine da sunan tayashi murnar xagayowar ranar haihuwarsa,wanda sam shi ya mance ma da yaune ranar haihuwarsa. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Qarfe biyar na yammaci da 'yan mintuna ta sauke wayar daga kunneta tana sakin ajiyar zuciya,itakam har cikin zuciyarta sam batajin zuwa ko ina,haka kawai taji batason fita.https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/video *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani DON GIRMAN ALLAH karki sharing,ga mai buqata saiya tuntubi wadan nan lambobin* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 1️⃣3️⃣ Fiddausi ce ta kirata tanason ta rakata wajen da take siyo musu kayan zaqi kamar yadda ta sawa syrup din da take baiwa shahidan suna,duk sanda shahidan ta buqata tana amsa ne kawai daga wajen fiddausin,wanda nafisa ce ta baiwa mima kudin da za'a siya a jibgewa shahidan,ita kuma mima ta baiwa fiddausi kudin ta saya ta aje din take bata,don ita bata harkar shaye shaye,barta da biye biyenta kawai,shahidan taso ta tirje don yau din anwar ya gaya mata zaizo akwai wata muhimmiyar magana da zasuyi,amma sai fiddausin taji haushi ta katse wayar sanda tace ba zata samu zuwa ba,ita dinma a karan kanta sai taga bai kamata taqi rakata ba,tunda abun nan tare suke amfana dashi,bugu da qari duk sanda takeso kyauta take bata shi ba tare dako sisinta ba. Tilas ta shiga bandaki ta sake gyara jikinta kasancewar tana al'ada ne,kuma idan tanayi din tana bleeding ba laifi,hakan ya sanya duk sanda zata fita take saka always biyu ko kuma pant biyu,yau always din tata ta qare saura daya saboda haka ta saka pant biyu duk da tana tunanin Allah yasa ya riqeta. Tsaf ta shirya ta shuga wajen umma "Umma....zan raka fiddausi gaisuwa,baban wata 'yar ajinsu ya rasu" "Ina ita fiddausin?" "Ta gidansu zan biya ai umma yafi kan hanya" "Saikun dawo" ta fada tana miqa mata dari biyu kudin mota,ta amsa ta miqe ta fice daga gidan. A qofar gida suka hadu da fiddausi "Amma karmu jima don Allah fiddausi saboda anwar kar yazo bai sameni ba,kinsan baison yawan fita" baki ta tabe cikin ranta tace "Yau za'ayi mai gaba daya ma ai" amma a fili sai tace "Sannu matar kulle,yaushe aka daura auren naku ban sani ba?" Harararta shahida tayi "Kinga banason wulaqanci,kome zakiyi ki tsaya iyani,koda ba'a daura aurenmu ba ya isane dani" "Allah ya baki haquri...shi yasa har na kira daddy A yazo ya kaimu saboda mufi sauri sai kuma nace ya barshi,don nasan halinki yanzu zakice ba zaki shiga motarsa ba" dan hade rai shahida tayi "Kinfi kowa

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});