Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 40

Chapter 40

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,309 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya baci anty,za'ayi duk yadda kikeso,zanje da kaina na samu kawu abdulkarim na shaida musu,Allah yayi mana jagora" ajiyar zuciya ta sauke sannan tace amin Allah yasa ayi a sa'a,ko kadan batason iyayen nafisa su kallesu amatsayin butulu marasa cika alqawari,marasa kuma rama alkhairi da alkhairi,daga wannan magana ya miqe "Har zaka wuce?" "Eh...ina da aiki da yawa kwana uku ban samu shiga company ba" "To Allah ya taimaka....amm dama inason gaya maka,cikin satin nan nakeso na shiga katsina mu gaisa dasu baba furai'ah,ya dace kaima ka ware lokaci kaje ku gaisa,don ba qaramin jimawa kayi rabonka dasu,tun suna qorafin kayi kudi ka watsar dasu sai aike har sun haqura ma sun daina" bawai zuwanne wajensu baya sonyi ba,katsinarce baya son shiga,shi duk wani abu daya jibanci tuna mishi da ita baya qaunarsa "Zanyi qoqari in sha Allah" tana zaune daga nan har ya isa inda ya aje motarsa tana kallonsa,ya bude ya shiga ya tayar da ita yabar gidan. Ajiyar zuciya ta sauke bayan ya bacewa ganinta,ta fada dogon tunani,abinda yake dojewa dai yake nuna tsantsar qinsa shine ke wahalar dashi,lamarin da yake qaryatawa shike dawainiya dashi,itakam a duniya kaf bataga matar data dace dashi irin shahida ba,har yau yaqu furta nata meye sanadi?,meye dalilin rabuwarsu,har cikin zuciyarta tana qaunar yarinyar,ta zabi gida kusa dasu ne don tana saka ran wataran ta dawo mishi da ita cikin rayuwarshi,tarihin soyayyarsu,yadda tayi tambari ta kuma yi suna bai kyautu ace ta qare a haka a banza ba,ta sani cewa ko yaqi ko yaso koya nuna koya boye shahidan wani bangare ce na rayuwarshi,ta jima tsahon shekaru tana addu'a tare da fatan Allah ya shige mata gaba yasa taci galaba duk sanda ta tasamma tunkarar lamarin,domin cire qiyayya daga zuciyar da ada take cike da soyayya ba qanqanin abu bane,saidai a jikinta da xuciyarta duka tana jin lokaci yayi daya dace ta tashi ta gwada tabuka wani abu,koda zaiyi kuka da ita gaba tana da tabbacin zaya gode mata,duk da batasan meye yayi silar ruguxa wannan kyakkyawar alaqar da aka ginata cikin fahimtar juna ba. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Cikin lokaci kadan ta soma jin cewa zuciyarta ta karbi canjin da tazo mata dashi,ba'a dauki dogon lokaci ba uncle hisham yazo mata da upper ta daukan aiki a companyn *TRIPLE R GEM* kamfanin dake sarrafa duwatsu masu daraja da tsada zuwa kayan ado da qawa na mata ,irinsu sarqoqi,dan kunnaye,zobuna,abun hannu,munduwa da sauransu,mallakin *RAYYAN* miji ga *RUMANA DA RAIHANA* (DANGANTAKAR ZUCI). Sun bata matsayin accountant na wajen gaba daya saboda yarda da amincin uncle hisham da rayyan yayi yasa ya bashi cigiyar wanda zai riqa masa wannan matsayin,matsayin da aka bata sai taji yayi mata girma,har taso tace ba zata amsa ba,uncle hisham ya zauna yayi mata bayani da kyau ya kuma nuna mata Allah ne ya bata,fatanshi kada ta bashi kunya ta kumayi aiki tuquru,tace in sha Allah. Duk wani abu da ake baiwa sabon ma'aikaci mai matsayi irin nata sun bata,saidai taqi amsar gida da mota da suke bayarwa,tace bata da ra'ayinsu,ganin haka sai suka qara mata kudi kan wanda ya kamata a bata. Uncle hisham da kanshi ya kaita gidan shugaba kuma mamallakin kamfanin gaba daya don tayi musu godiya,gida mai dauke da matan aure biyu kuma aminan juna,gida na farko data ji yanayin rayuwarsu ya burgeta bayan gidan anty zubaida,haduwar farko jininta ya hadu dana raihana,yanayin rayuwarta nutsuwarta da komai nata,haduwar farko ta karanci yadda ta iya tattalin miji cikin wani yanayi mai sanyi da kuma mu'amala,rumana uwargida,mace mai fara'a da saurin sabo itama sunsha hira da ita,wanda daga qarshe ta tattara kan yara tace zasuje siyayya ne ta barsu da raihana,yaran da shahida ta kasa tantance wanne ne yaran rumana wanne ne na raihana?. Cikin qanqanin lokaci ta kama aikinta sosai,ta kama mutuncinta haka nan tsakaninta da ma'aikatan sai gaisuwar mutunci da girmama juna,ita kanta idan ka kalleta zakaga sauyi mai yawa tattare da ita sabanin baya,ta sake fresh hakan fatarta ta qara kyau da gogewa,kwanciyar hankali da nutsuwa sun samu tare da ita,ta soma shimfida sabuwar rayuwa,tayi wancakali da dukkan wani qalubale da bacin ran rayuwa. _yanzu aka soma,muje zuwa masu karatu_ *Alqawarin Allah* 2️⃣1️⃣ *BAYAN SHEKARA DAYA* Komai na duniya baya ga qaddara yana tafe ne da lokaci,wanda wannan lokacin shike qunshe da komai,yake tattare da faruwar komai,shike bayyana komai hakanan shike haifar da komai din,cikin shekara guda shaheedan ta samu sauyi da canje canje masu tarin yawa,tayi qoqarin binne duk wani qalubale data taba samu cikin rayuwarta,ta kaucewa dukkan wani abu da zai tuna mata dashi fiye da baya,ta fannin rayuwarta kuwa shahidan ta sake zama wata mace mai aji,irin macen da kana mata kallon farko zakasan ta goge,bawai gogewa ta budewar ido ba,gogewa ta kyau,gogewa ta iya ado da mu'amala sakamon mu'amala da take da mutane kala daban daban daga sashe daban daban na qasashen afrika,ta qara wani kyau da kwarjini,hakanan ta murje,ta gefe guda kuwa a yanzu nuraddeen ya samu kanta babu laifi,aduk sanda ya kirata zata daga su taba hira,hakanan duk sanda yazo wajenta a gida takanyi qoqarin fita,wani lokaci ma yakan bita wajen aiki da niyyar daukota,anan ta dakatar dashi,don babu abinda ta tsana a duniya a yanzu irin shiga motar wani d'a namiji,duk sanda ta saka kai zata shiga sai abun ya fado mata,wannan moments din ya kasa barin qwaqwalwarta,shine kuma abu mafi muni cikin dukkan abinda ya faru da ita,tana mamakin me ta yiwa wannan mutumin daya watsota qofar gidansu cikin cin mutunci da wulaqanci?,me ta yiwa fiddausi wadda har yau bata bi ta kanta ba ko neman inda take,hasalima bata sake ganinta ba,to me zatayi mata?,me zata buqata daga gareta?,koma meye tana roqon Allah yayi hukuncin daya dace. To ko cikin company ma da baqin dakanzo siyayya kamfanin masoyane suka mata rubdugu,wani lokaci har haushi kan kamata na yadda ba'a cikakken kwananki uku wani bai ganta yace yana so ba,ta rasa meye a jikinta haka?,me take dashi wanda yake jan hankalinsu?,da tasan wannan abun ba shakka data cireshi ta jefar kota huta da shegen binbinin da suke ma rayuwarta "Kin hadu ne shahida,kina da komai Allah ya miki baiwar komai,ba zaki gane abinda nake nufi ba shahida,amma kinyi tako ina,ki bani dama don Allah" ta tuno kalaman wani alhj wanda tunda yazo kamfanin siyawa matarsa sarqoqi gift na birthday dinta ya dafewa shahidan,a sannan ta sauko zata je cin abinci,baima san ma'aikaciyarsu bace. Gefe daya ta sake yalwata rayuwar ummanta da qannenta,hakan ta yiwa gidansu gyara ta sake qawatashi,ita kanta a yanzu jin dadin rayuwarta take,abu daya ne data fuskanci umman nata ta tsiro dashi shine son shahidan tayi aure,don zancan da ake mubina na ss two ne,kuma ta samu wanda yake sonta,dama yakeso a bashi yaje can wajen dangin mahaifinsu dake katsina ya gabatar da kanshi. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Qarfe hudu suka tashi daga aiki yau,cikin sauri saboda kar lokaci ya qwace mata ta shiga adaidaita sahun da yake nata ne yake kaita aiki ko wata unguwa da takeson zuwa,a sanda kuma ya ajeta yaje yayi haya dashi. Saloon din da take zuwa kitso ya sauketa,ta dubeshi "Ka dan jirani yau ba dadewa zanyi ba" "To hajiya" ya fadi yana kashe adaidaitan,ta juya cikin takun nutsuwa zuwa bakin saloon din. Yanayin wajen kaman tsarin ciki da falo aka yi masa,duk da

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});