Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 90

Chapter 90

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,304 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

fuskar nafisa ta gilma mata a idanu,yadda ya cillota da girman kalaman daya sossoka mata saitaga gaba daya yayi mata baqi a ido,koren shaidan tayi sannan tayi bismillah taci gaba da takawa ta tura qofar falon ta shiga. *Alqawarin Allah* 43 Wani irin murdawa mararshi tayi wanda hakan ya sanyashi duqawa riqe da cikinsa,ya tako a haka a hankali zuwa gefan gadon,idanu ta zaro jikinta ya dauki rawa,ta tako ta tsaya daga bayanshi amma ta kasa cewa komai,da qyar cikin rawar murya tace "Sannu,baka da lafiya" kallonta kawai da yayi da qwayar idanunsa da suka kada zuwa launin jaa ya tabbatar mata da bashi da lafiyar kenan,ta juya zata futa da niyyar ta kira anty usaina ta shaida mata,saiya dakatar da ita "Jirani na shirya,zanje naga likita". Hannu likitan ya saka ya cire abun abun awon jini daya sanya a dantsen anwar din yana kallonshi "kamar yadda na tsammata ne,jininka yahau sosai,kamarma yahau fiye da kowanne lokaci,gaskiya anwar bazan boye maka ba,wani lokaci sai naga kamar kana wasa da lafiyarka ne,bansan meya hanaka kwantar da hankalinka ba ka samu jinin nan ya sauka gaba daya,sai yayi kaman ya sauka saiya sake hawa,bansan daga inda matsalar take ba" murmushin qarfin hali yasaki,ya lumshe idanunsa kana ya bude "Share kawai khalid" likitan mai sunan khalid ya waiwaya ya dubi shahida wadda ke zaune wata kujerar daban,hannayenta rungume a qirjinta,ta zubawa anwar ido ba tare da yasani ba,kallon mamaki take masa na bayanan da taji daga bakin dr khalid,wanne irin hawan jini?,yaushe anwar din yasamu hawan jini?,iya saninta dashi kaf tarayyarsu anwar baida hawan jinin,yaushe ya gamu da wannan matsalar? "Madam" ya kirata wanda hakan yaja hankalinta zuwa kanshi "Bayan hawan jini gaskiya abokina na buqatar kulawa,don Allah ki kulamana dashi,nasan kinfi kowa sanin mutumin kirki ne,lalurarshi ba zata yiwa mutane da yawa dadi ba" kai ta gyada likitan ya miqe yana cewa "Ruwa naso indan saka maka,amma nasan hali ba zaka taba yarda ka zauna ba,bari na rubuta maka wasu magungunan na bayar a karbo maka,madam sai a kula da bashi akan lokaci" kai ta sake gyadawa tana duban anwar din,saita kauda kai sanda taga ya waiwayo suna shirin hada idanu. Suna tafe a hanya motar ta dauki shuru,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarsa,tambayar ta yiwa shahida tsaye a rai na hawan jinin anwar,yayin data gefan anwar din maganganun dr khalil suka dinga kai kawo a qwaqwalwarsa,tabbas ba shakka shine mutum na farko da zaifi kowa son rabuwa da cutar,zaifi kowa son ganin ya cire kome cikin ransa,zaiso ace ya goge kome dake damunsa,amma saidai shi kansa yasan hakan bame yiwuwa bane,shahida ce,idan da wata macen ce daban ha tabbatar da tuni ya cireta daga rayuwarshi irin fitar da mai rai kanyi daga duniya wanda har abadan bazai dawo cikinta ba,amma akan shahidam hakan ya gaza,ya sani cewa koda zai fada a baki koda zai nuna a aikace shahidan bata dameshi ba yayiwa kanshi qarya,karon farko dayakejin inama inama,inama ace bai kalli hotunan ba,inama ace ranar baije gidansu zance ba bare yaga abinda ya gani,inama ace shahidan bata fada halin data fada ba a baya,da wannan tunanin suka isa gida,da kanshi wannan karon yasha maganin sannan ya shiga bedroom dinsa ya kwanta kozai samu relief. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 A kasalance yake shiryawa cikin farar shadda,riga iya gwiwa mai gajeran hannu da dogon wando,kana ganin yadda yake shiryawar kasan cewa ba wani dadin jikinsa yake ji sosai ba,yana daura agogon hannunshi ta turo qofar dakin da sallama,hannunta riqe wata butar shayi me kyau,da mamaki take dan dubanshi saidai bata tanka ba ta aje butar "Ya jikin?" Ta tambaya a taqaice,daga kai yayi ya dubeta yadda ta juya baya ya maida kansa yaci gaba da daura agogonsa sannan yace "Alhamdulillah" tadanyi taku biyu sannan ta sake tsaiwa,ya fuskanci akwai magana a bakinta saiya amsa "Tun jiya akwai alqawari. Haduwarmu dashi,jiya banjin dadi,so yau nakeson nacika" yana gama fadi ta taka ta sauka daga saman,dama tanson jin fitar zaiyi amma tanajin nauyin tambaya. Tun jiya take zuba idanun ganinsa,ta kasa zaune ta kasa tsaye,tun bakwai na dare take zirya tsakanin harabar gidan,falon abbansu zuwa nasu falon da dakinta ma gaba daya,ganin goma na dare tayi hankalinta yayi mummunan tashi,Allah yasa abba bai gane ba,Allah yasa anwar bai kira abba ba ya sanar masa yaji yana nemansa ba abba kuma yace bashi bane,daga daren zuwa safiyar ranar ji tayi kaman ta zare,duk motsin shiga da fitar mota a gidan yana kan idanunta,saida dare yayi ta tabbatar babu wani sauran wanda ka iya zuwa a wannan lokacin sannan ta haqura. Da safema haka ta dasa abun zama cike da fata da kuma buri,qarfe goma da rabi da minti takwas aka saki horn mai gadi ya doshi qofar don ya bude,gabanta wani mugun faduwa yake haka tamiqe tsaye tana duban qofar gidan,kusan shidewa tayi sanda taga fitowarsa daga motar,idanunta qur akanshi yana sake burgeta duk wani motsi da yayi,tana kallon aka masa iso cikin falon daddyn,cikin wani mugun hanzari ta diba tayi cikin gida kai tsaye ta wuce dakinta,hijabi ta lalubo ta zira saman kanta sannanta sake fitowa da hanzari don kada lokaci ya qwace mata. Sanda ta shiga mummynta na tare da daddyn,hakan yayi masifar yi mata dadi,sait tayi qoqarin daidaita nutsuwarta ta taka zuwa cikin falon da sallama. Dukkaninsu suka amsa mata,ta isa gefan daddyn inda anwar ke zaune qasan carfet saboda girmamawa suna gaisawa,nan ta duqa kan duka gwiwoyinta,ta saki kuka sosai wanda ya karade ilahirin falon,duka sakin baki sukayi suna kallonta,mummy ce cikin hade rai tace "Kewai meye haka?,wanne irin shashancine wannan kawai zaki shigo kisa mutane a gaba da kuka?" Cikin muryar kuka tace "Don girman Allah mummy ku yafemin,ku yafemin,ku roqamin ya anwar shima ya yafemin" "Me ya dawo da wannan maganar data riga tawuce kuma nafi?" "Gafarar ya anwar nake nema" gaba daya kanshi ya kunce,shi sam.bai dauki abunda tayi a matsayin wata matsala ko abun bacin rai ba,tuni ya riga daya wuce wajen,tun a lokacin da abun ya faru shiya tattara komai daya shafi wannan fannin ya ajeshi a gefe,baison zancan yayi tsaho saboda haka yace "Ya riga ya wuce har abada" ranta taji yayi,wani mugun sanyi,alamun nasara na tabbata kenan a gareta,saita sake sunkuyar da kanta qasa sosai sannan tace "Bansan cewa nayi wauta ba kuma nayi kwaba saida na rabu dakai,nakai kukana ga abba da mummy amma kowannensu yaqi mara min baya ka dawo cikin rayuwata,sunce idan ka amince suna murna da hakan,saboda sunsan cewa idan sukayi maka magana ko bakaso zakace eh,gani a gabanka anwar don girman Allah inason ka sake dawowa rayuwata karo na biyu,ka yiwa iyayena dake shauqin son ganin haka alfarma wanda alkunya da kawaici yasa suka kasa gaya maka" "Ke nafi!" Abbanta ya dakatar da ita ta hanyar daka mata tsaw,a,bataji komai ba don idanunta da zuciyarta sunyi nisa wajen son ganin cikar muradi da burinta,saita daga kai ta dubi abban sannan ta sake sunkuyarwa "Abba na fadi masa gaskiyar abinda yake faruwa ne,na tabbatar da zaka iya da kaine xaka nemi ya aureni karo na biyu....anwar,ka duba wannan alkunya da kara ta iyayena gami da girman soyayyar da nake maka" baqinciki ya kama mummy na yadda sam halayen nafisan suke wadansu irin mabanbanta daban,ta kawo mata duka anwar ya dakatar da mummyn cikin

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});