Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 63

Chapter 63

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,301 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sanda labarin ya shiga kunnenta,qyaleta tayi bata bi ta kanta ba,ta barta ta gama kukan zuciyarta ta huce tukunna. Tamkar zata zauce haka taji,ta kai ta kawo ta kasa zama kamar wadda ta hadiyi tabarya,wannan wacce iriyar masifaffiyar shahida ce?,wanne irin mayen anwar ne?,ace duk yadda takai ga rabasu haqanta ya gaza cimma ruwa?,iya abinda ya kamata tayi don rabasu tayi amma ace bayan shekaru shidda sun sake dawowa sun jone?,idan ma kisa ba batasan me zatayi don rabasu ba,wayarta ta rarumo ta kira number mima,saidai hartayi quginta ta katse bata daga ba,haka ta dinga kira ba qaqqautawa amma bata daga ba,cillar da wayar tayi cikin muryar kuka mai cike da bacin rai da qunan zuciya tace "Shegiya mahaukaciya,wai ina kika shiga ne?!" Ta qarasa fada cikin qaraji wanda banda sautin tv dake aiki ba abinda zai hana momyn jiyo sautinta. Haka ta dinga qaramin hauka ita kadai cikin dakin har sha biyu saura na dare sanda wayarta tahau kuka,ta daukota da hanzari tana tsammanin mima ce,maimakon mima anwar ne,aje wayar tayi kawai tana kallonta harta qaraci kukanta ta gama,sai daya kira sau uku bata daga ba tana zaune da kallon wayar ruwan hawaye na fita daga idanunta,tana ganin hakan da zatayi kawai shine zaisa anwar din ya janye qudurinsa ya haqura shahidan. Washegari qarfe goma na safe tana gaban mudubi a zaune tana kallon yadda fuskarta ta qojale saboda kukan data kwana tana yi wayar ta sake burari,wannan karonma anwar ne a maimakon mima,bata da mafita tilas ta daga wayar ta sake gaya masa kalaman da zasu tabbatar masa da cewa ta rabu dashi kp hakan zai tsoratashi ya janye nufinsa "Karka sake kirana matsawar kana kan qudurinka na hada aurena da wata macen daban,na gaya maka tun jiya nikam nafisa bazan aureka ba anwar muddin kana a matsayin mijin mace biyu,na haqura dakai har abada" daga haka ta yanke kiran,saiya furzar da numfashi daga bakinsa ya baiwa banza ajiyarta,ya aje wayarshi yaci gaba da shirinsa,shikam ya yankema ransa babu sauran wata mace da zata sake bashi wahala,bazai sake son wata ba bare ta gasa mishi zuciya yadda ya faru dashi a baya,ya saki qaramin murmushi sanda ya tuna cewa da sonta yake da tuni yanzu yana cikin tashin hankali da dimuwa a sanda tace bata sonshi,yanzun kam hankalinshi kwance yake jinsa,saidai kuma wani bari na zuciyarsa yana dan jin damuwa,musamman idan ya tuna da mahaifanta yadda zasu dauki maganar,da wannan tunanin ya gama shirinsa ko abinci yau bai saurara ba ya dauki muqullinsa ya fito,kafin ya tashi motarsa ya tsaya ya turawa anty usaina yadda sukayi da nafisan,don baison kiranta ma bare ta bijiro da wani abun da zai hanashi uzurinsa nayau. ***** ****** ****** ***** "Wannan sakarcin banza ne ai sakarcin wofi,ta isa ta haramta abinda Allah ya halatta?" Alhj abba mahaifin nafisa ya fada cikin fushi da bacin rai yana duban mummy mahaifiyarta,kai ta gyada itama,sau tari tana mamakin halayen nafisan,ta rasa inda take debo wasu baqaqen halayen,abubuwa da yawa ita dai ta sani ba halayyarta bace kota mahaifinta ba "Atoh,nayi mata magana daxun da safe ta nunamin tana kan bakanta" mummy ta baiwa alhj abba amsa,shikam anwar yana daga gefe kanshi a qasa cikin girmamawa yana saurarensu,baice komai ba sai a sannan "Kuyi mata uzuri,duba da yadda zancan ya sameta a qurarren lokacin da bata zata ba,ni kaina bani da masaniyar abun zai kasance haka sai gab da zanyi tafiya,sai naga yafi kyau idan na dawo na shaida mata mu fahimci juna,to sai kuma aka samu sabanin fahimta" "Qarancin hankali da tunani dai,ita zata zauna maka da ita?,ko ita haqqin kula da ita yake kanta?,bilki....kiramin ita maza" a nutse hajiyan ta miqe ta fice zuwa dakin nafisan. Kwance take rub da ciki tana aikin kuka,tana son anwar tana tsoron rabuwa dashi,tana tsoron yaqi janye qudurinsa,don itakam ba abinda zai sata ta sauka daga kan bakanta,matsawar ta yarda ta aureshi to yaqin da tayi shekara da shekaru tana yi,kudinta data kashe,lokacinta data fansar duka sun tashi a babin badinuhu bataci riba ba kenan "Kin hadu da aiki kuma kin gama kanki da wahala wallahi,tunda kin daukama kanki aqidar banza da wofi,ki tashi kije mahaifinki nason ganinki" cewar mummy daga haka bata qara ba ta juya tayi ficewarta. Sanda ta isa falon anwar ta soma gani,kishinsa ya sake lullubeta ganin yadda kamar ma sake kyau da fresh yayi abinsa tsakanin kwanakin da ita take fama da quncin zuciya,gefan abban nata ta zauna ya dubeta "Nafi,wanne irin shashanci da sakalci kike shirin aikatawa haka?,saboda Allah ya halatta masa auren daga daya zuwa hudu saikice ba zaki aureshi ba saboda haka?,zaki sauya hukuncin Allah kenan?,koke kikayi kanki?to kar naji karna gani,banason wannan shirmen banza,yana da damarma yace biyu zaiyi kece ata uku" Kuka ta saki sosai "Abba...wallahi bazan aureshi ba,bazan iya zama dashi da wata ba"baki bude alhj abba ya watsa mata daquwa "Kinci gidanku,kajimin fitinanniyar yarinya?,to saikin aureshin naga wanda ya isa ya hana" miqewa tayi cikin kuka "Wallahi abba zan gudu,zan barku idan aka aura min shi" mummy na shirin kai mata duka saboda takaici ta fice a guje daga falon. Shuru ne ya ratsa falon,kunya da takaici na kama alhj abba da hajiya bilkisu,sai suka rasa ta inda zasu kama zancan,sunsan halin nafisa sarai sai addu'a,karta aikata wani abu da zai zama musu illa nan gaba,anwar ya fahimci shurunsu saboda haka yace "Alhj,karka damu,Dukkaninmu ni da kai da mummy bamu da ikon da zamu sauya mata ra'ayi,sannan duk yadda mukaso abin itace zata zauna,dole saida gamsuwarta sannan komai zai tafi yadda ake buqata"ajiyar zuciya suka saki dukansu kusan a tare cikin bacin rai da takaici "Yarone ka haifeshi baka haifi halinsa ba,kayi haquri anwar" cewar alhj abba yana jin babu dadi har cikin ransa,yana jin kaman ya muzanta "Haka Allah ya qaddara" anwar din ya furta kanshi a qasa,shima yana jin babu dadi saboda yadda sukejin laifin kaman a kansu yake. Tana zaune har yanzu inda ta zauna tana rusar kuka a haka mummy ta tura qofar dakin ta sameta,da hanzari ta daga kai cikin fargaba da razani tare da taraddin furucin da zai fito daga bakin mummyn,tana son anwar tana fata ace ya karbi muradinta "Shikenan ko?,burinki ya cika?,saikije ki samo wani mijin wanda yafi anwar" daga haka ta juya abinta ta fice tabar mata dakin,cikin tashin hankali ta miqe kaman zata bi bayan mommy don samun qarin bayani,sai kuma ta dawo da baya qwaqwalwarta na gaya mata ma'anar maganar mummyn,anwar ya barta?,anwar ya zabi shahida akanta?,wahalarta ta tashi a banza kenan?,kai ta shiga girgizawa tana fadin bazaiyiwu ba,ta dauki wayarta ta soma kiran layin mima ba qaqqautawa don tana da buqatarta a yau fiye da kullum,saidai amsar dai daya ce wayar a kashe take. A qalla ta kwashi awa kusan biyu a haka,bata da wata mafita ayanzu banda ta kira anwar,ta soma laluben number dinsa ta kira. Fitowarsa kenan daga kitchen dauke da cup na coffe wanda ya shiga ya hada da kansa,cikin mamaki yake duban mai kiran,saiya samu daya daga cikin kujerun falon ya zauna yana amsa wayar "Ni zaka yiwa haka anwar?,ni nafisa zaka gujewa saboda wata banzar shahida da bata kama qafata wajen qaunarka ba?,idan baki sani ba bari yau na fada maka,ni nafisa nice silar duk wani arzqinka,nice silar duk

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});