Chapter 6
Chapter 6
qaramin lokaci,banda anty hasanan duk duniya baiga wanda zai tsaya ya soko masa zancanta ba tare daya kauda shi daga gabanshi ba "Ka taba kwanciya dai dai da rana daya ka tariyo alkhairanta a gareka?,ka taba xama ka banbance aya da tsakuwa kuwa?" Kalamanta na masa wani irin suya ne a qirji bashi da jarumatar ci gaba da sauraronta saboda haka ya qarasa ficewa cikin sassarfa daga falon,ya fada motarshi ya tashe da gaggawa ya fice daga gidan. Ta jima tsaye a wajen,dukkan wata laka ta jikinta tayi sanyi qalau,wannan wanne irin abune?,ko a mafarko ba wanda ya taba tunanin wannan kyakkyawar alaqa tarayya da abota zata juye watan watarana ta zama irin haka,jikinta ba qwari ta koma ciki ta samu d'aya daga cikin kujerun falon ta zauna tana tuna wasu daga abubuwan da suka shude cikin rayuwar muhammad da rahama. "Ita ta rusa dukkan komai,ita ta kawo dukkan wata damuwa da baqinciki da nake kwana nake tashi da ita,ita ta butulcewa ni'imar Allah ta wulaqanta rayuwar da Allah yayi mata baiwarta" kalaman daya dinga fada kenan a sandaya samu qasan daya daga cikin bishiyoyin dake jere reras a harabar kamfanin ya faka motarsa,ya kashe wajen awa guda cur yana ciki yana qoqarin controlling kansa,yana ganin wayoyin jama'ar da suke da appointment dashi amma ya kasa daga ko guda daya,baisan me yasa yake iya dealing da duk wani daya tunkaroshi ba cikin qanqanin lokaci,amma akan wannan sabgar har yau ya kasa maida kansa jarumi,ya kasa daina jin ciwon dukkan abubuwan da suka jima da shudewq,ya kasa daina jin tsanarta,ya kasa tsayawa yayi mata adalcin dako yaushe antyn da zuciyarsa ke qoqarin gaya masa yayi mata. Sai daya shafe awanni biyu sannan ya iya fitowa bayan ya rufe motar,ya dinga takawa ahankali zuwa babban ginin kamfanin daya mamaye iya kallon mai kallo,sauran mutane dake dakon jiranshi suka yo masa caa,yayi qoqarin ganin ya dawo da mode dinsa duk da yadda yake jin kwanyarsa a birkice. Tsaki taja bayan ta kammala karanta saqon,kafin daga bisani ta cilla wayar gefanta,dawowarta kenan daga makaranta a matuqar gajiya ta zauna a falon,bata ma kai ga qarasawa dakinta ba saboda gajiya,gaba d'aya ta gundura da wannan d'an banzan shirye shirye da hukumar makarantarsu keyi na zuwa shugabanta,wanda ita a ganinta ko president ne zai kawo musu ziyara iyaka kenan,ta k'agu yazo ya tafi a wuce wajen,saiga saqon nuraddeen kuma wanda ta tsani gani kamar yadda ta tsani mutuwarta,batasan sai yaushe zai gaji da halin shakulaton b'angaron da take yi dashi yayi zuciya ya barta ta rayu ita d'aya ba kamar yadda ta sama ranta. Sun riga sunyi waya da anty zubaida tasan ta fita yau bata nan,don haka girkin gidan na yau na wuyanta,ga huda da suka dawo tare tasan yunwa takeji,don ma ta siya mata cake da lemo a makaranta kafin su iso gida. D'aki ta shiga ta tube ta fada wanka,bayan ta fito ta sanya huda itama ta shiga tayi don yau babu islamiyya,a gurguje ta shirya tayi sallar azahar sannan ta shiga kitchen. Indomie ta soma dora musu sannan ta dora girki a dayan wajen "Anty kin gama?" Huda data shigo yanzu ta fada tana qarasowa inda shahida ke zaune sosai qasan kitchen din tana gyara kayan miya,don ta duba nasu markadadden da suke ajewa ya qare "Sauran kadan hudallah....dadina dake bakya juriyar yunwa" "Anty yunwa bata da hankali,haka d'an almajiri fa yake cewa" murmushi shahida tayi wanda ya qara kyawun fuskarta,hakanan ya bayyana wushiryarta,kafin tace wani abu hudan ta sake cewa "Anty...dama d'an wake kika yi mana,inason d'an wake" a hankali ta juya ta dubi yarinyar saboda tuna mata wani abu da tayi,yana matuqar son d'an wake a rayuwarshi,a duk sanda taga abincin ko taji an ambaceshi saita tuna dashi.*ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH)KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *KO KUMA* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don samun shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi* https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos *AA* 0️⃣4️⃣ Kasa cewa komai tayi,maganar hudan ta cillata tunanin wata duniya can baya,wanda duk yadda takai ga hana kanta batasan sanda ta fada ba. Sai data sallami huda sannan taci gaba da sabgar girkinta,batasan me yasa ba sam batajin yunwa,ko zancan da huda tayi ne ya cushe mata cikinta gaba daya ya sanya har walwalarta ta ragu. Tana tsaka da kwashe abincin cikin coolers huda ta shigo da sauri hannunta dauke da wayar shahida tana fadin "Anty ana kiranki,zata katse" ta fada tana miqa mata,bata amsa ba ta kalli screen din wayar dake hannun huda,nuraddeen ne,saita dauke kai taci gaba da juye abincin tana cewa "Ajiyeta kawai huda,aiki nake" juyawa yarinyar tayi ta fice da wayar zuwa falo da gudu don kada cartoon din da take kallo ya wuceta. Tana cikin kintsa wajen sallamar anty zubaida ta karade falon sannan ta taddata cikin kitchen din "Sannu da dawowa maman huda" "Yauwa sannunki shahida,kin ganni sai yanzu ko?,wallahi layi yau na samu....me aka dafa mana ne yau da yunwa na dawo" nuni shahida tayi mata da food flask din dake jere a wajen,ta qarasa tana budawa "Hmmmmm,kice yau na musamman ne abincin,bari wannan sai nayi wanka zan zauna sosai tukunna na kwashi dabge" qaramin murmushi shahida tayi mai fitar da d'an sauti tana duban anty zubaidan,har takai bakin qofa ta dawo "Au....ni kuwa kinsan nuradden na qofar gida zaune cikin mota yana jiranki?" Asanyaye ta daga kai ta dubi anty zubaidan,sai ta sadda kanta tana goge plates din data wanke zata jerasu a muhallinsu,hakan da tayi shi ya tabbatarwa anty zubaida ya kira bata daga ba kenan "Shahida.....wannan wacce irin rayuwa ce kika daukarma ranki?,mai sonka fa ya wuce ka wulqantashi,laifin wani dama yana shafar wani?" Shuru ta sake zabar tayi,saboda tana ganin sun gaza fahimtarta ne gaba daya,ta yiwa soyayya hidima,ta yiwa soyayya halacci,ta yiwa soyayya dukkan wata kara da alkunya,qarshe data tashi ita mai ta bata?,data tashi da wanne sakamako tazo mata?,sunfi kowa sani saboda haka sunfi kowa amsar dukka tambayoyinta,ko daya bata tsinci komai cikin soyayya ba face tsantsar butulci mummunan sakamako da kuma mummunar makoma,shin ta yiwa kanta a dalci kenan idan ta sake cusa kanta a wannan bigiren? "Nidai ya roqeni alfarma,saboda haka idan na isa dake ki leqa ko gaisawa ne kuyi" zancan anty zubaida ya katse tunaninta,daga haka bata sake cewa komai ba ta ida ficewa daga kitchen din,tana jinta sanda ta kira huda suka haye sama tare,tasan kuma tayi hakanne don sanin halinta,ba qaramin aikinta bane ta fita ta baro masa huda ta cikashi da surutu wanda idan ya gaji da zama yake sallamar huda shima ya wuce nashi guri. Anty zubaidan tafi qarfin komai a wajenta,don haka ta dauraye hannayenta ta wuce dakinta,ta zari hijabi ta saka ta sanya slipper dinta ta wuce qofar gidan. Kamar kowanne lokaci yana zaune cikin motar,bayanshi jingine da seat din kujerar dayake kai,da alama ya jima zaune a wajen,duk da haka ganin fitowarta bai hanashi miqewa ba yana sakar mata murmushi harta qaraso "Barka na tunda na samu kin fito" ya fada tamkar wanda baiyi zaman jiranta ba "Inda kayi aiki da shawarata tun a karon farko da duk bamu kawo wannan matsayin da muke kai yanzu ba" ta fada kanta tsaye tana dubanshi,kafin daga bisani ta janye idanunta,har ga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96