Chapter 66
Chapter 66
soma sauka ta gilashin motarsa,yaso ya dake yaso ya dauke kai ya saka motarsa cikin gidan anty usaina amma saiyaji kaman umarni,a zafafe yace "Oh god" yana zare belt din jikinsa,cikin zafin nama da kuma jin haushin kansa da kansa ya bude murfin motar ya fice. Yana kuzari da halittar ba daya bace,hakan ya sanya cikin qididdgaggun taku ya cimmata "Daga ina kike haka?" A nutse ta waiwayo tana dubansa sanda take gab da qarasa bakin titi,saita juya da niyyar ci gaba da takawa ba tare data amsa shi ba "Wai sanda zaki fita ma kin tambayeni ne?,saboda tsabar rinton zunubi?" Kalaman sun mata ciwo,wato tun yanzu yake nufin xai mulkata kenan?,hakan yasa ta tsaida tafiyar tata ta juyo ta dubeshi "Kai waye da don zan fita saina tambayeka?" "Kinfi kowa sanin ni waye ai ba buqatar na maimaita miki,banason dogon zance wuce muje na taimaka miki na saukeki,amma kafin sannan idan kina da niqab ki saka a fuskarki kar mutanen unguwa su ganmu tare su zaci nima dan harka ne" ya kai qarshen zancan yana dage girarsa duka biyun,wanda hakan ya masa kyau ainun duk da fuskarshi a murtuke take,sosai kalaman suka fusatata wanda hakan ya sanyata ta juyo gaba daya ta watsa masa idanunta da suka sake budewa saboda bacin rai,hakan ya tilasta masa dan qanqance nashi idanun gami da damqe hannayensa dake zube a aljihu "To hell with your taimako...Allah suturu buqui,har abada bana son taimakonka,sannan kuma aikin banza kake harara a duhu,da kake gudun kar a ganmu tare me ya kaika neman dauramin igiyarka,idan da gaske kake qyamata aiya kamata ka gujeni da gaske ta yadda ko qasa daya ba zaka hada dani ba bare inuwa daya,indai ka cika kai anwar ne ka aikata hakan" qaramin murmushi ya saki daya sake fitar da kyansa,ya dage dukka kafadunsa "Ba zaki taba samun yadda kikeso ba,niba qaramin yaro bane bare kalamanki su tunzurani nayi miki yadda kikeso,abu daya kawai na sani shine,na riga dana biya sadakinki,saboda haka ina da power a kanki ko kinqi ko kinso...saboda haka ki wuce muje" dogon tsaki taja wanda ya ratsa kunnuwansa,sannan ta watsa masa harara ta juya taci gaba da tafiya,bai fasa binta ba shima har suka isa titi. Adaidaitan farko data tsaida ya sallameshi da dubu daya yace yane abinsa,na biyu ma haka,na uku kuwa da yame dattijone yace masa baba kaje matata ce yaji takeson yi,na bata haquri taki haqura,nan yasa bawan Allahn ya tsaya yana mata nasiha,inda daga qarshe ya sallameshi da dubu uku ya amsa yana godiya,ta hudu kuwa ya samu sauayi maiji da tashen girma yaso masa gardama.kan saiya dauketa tunda itama tana son shiga "Kana sha'awar xaman gidan kaso kenan?" Harya karkata baki zai masa diban albarka saiya nutsu ya qarewa shigarsa kallo,tun daga takalminsa,kayan jikinsa zuwa agogonsa,aibabu shiri yaja abun hawansa ya fece,bacin rai ya taru ya rufeta ruf sanda ta kalli titin ta ganshi fayau ba wani sauran abun hawa na haya kuma nan kusa,ta waiwayo zata gasa masa magana ko xataji sanyi,kadan ya rage fuskarsu ta gwaru,sam batasan yana bayanta ba a tsaye,da alama kuma duk tsahon lokacin kallonta yake,baya yaja yana bata fuska "Ke baki da kunya ne?,akan titi kike neman ki rungumeni?,toki maida qwalamarki,ni ba naki bane" kawai saita fashe da kuka ba tare data shirya ba,saboda ya gama cutarta,bata ga wani kalma da zata fada masa ba wadda zata rama abinda ya gaya mata,minti biyu kacal ruwan sama ya soma sauka,ya kalli sama sannan ya kalleta "A karo na qarshe nake gaya miki ki wuce mu tafi" baya taja saman wasu tayoyi da masu faci suka tashi suka barsu a wajen ta zauna,ta gwammace ruwan yayi mata koma meye data bishi kota shiga motarshi,ganin ta zauna dafa'an ya sanyashi juyawa ya koma cikin layin don dauko motartashi zuwa nan bakin titin dukda yadda ruwa yake dukansa. Yana isowa wajen yaga tashinta cikin adaidaita sahu,qaramin murmushi ya sube masa,wato dama tana da taurin kai kenan?,saiya sake baiwa motar wuta harsai daya je daya side din na adaidaitan,ya tabbatar ta ganshi sannan ya barsu suka wuceshi,a baya yaci gaba da binsu har xuwa sanda yaga shigarta gida sannan ya karya kan motar ya koma gidan anty usaina. Sanda ta shiga gida baqinciki da takaici ya sake cikata ganin yadda gidan har baqi yadan samu,hakanan ga kayan amsar lefe a kammale gobe kawai suke jira,hasina ma ba'a barta a baya ba,ganun zata saka mata ciwon kai da tsokanarta yasa tayi zarcewarta daki ko tsayawa a wajen batayi ba bare ta zauna,gaban mudubinta ta tsaya tana kallon yadda ta jiqe gaba dayanta,haushinsa ya sake cikata,taji kaman ta sake fashewa da wani kukan,duk shi yaja mata,da ta shiga adaidatan a lokacin daya dace da duk hakan bata faru da ita ba,haka ta ringa cire kayanta daya bayan daya ta daura babban towel ta shige bandakinta ta hada ruwa mai zafi tayi wanka. https://youtu.be/alR4jOvvQUc *Alqawarin Allah* 3️⃣3️⃣ Washegari da wuri tabar gidan fiye da yadda ta saba fita,ko a kamfaninma masu gadi kawai ta taras,ta bude office dinta ta shiga ta zaun donko mai maita shara ma bata iso ba. Sanda aka tashi ta tsaya tunanin inda zata,don tasan wala'alla dai dai lokacinne ma gidan yake a cike,yankewa kawai tayi ta tafi gidan oga rayyan,ba bata lokaci ta gayawa mai adaidaitanta ya wuce can da ita. Sosai taji dadin zuwa gidan,a rayuwa gidan yana burgeta qwarai,yanayin mu'amalar jama'an gidan,nan wajen raihana ta zauna suka sha hira sosai,sai bayan sallar magariba sannan tayi haramar tafiya,nan ta cikata da turaruka tana cewa "Gashi amarya,naji oga yace kin kusa shiga daga ciki,ki fara amfani da wadan nan kafin lokacin xan kawo miki na amare" "Hmmm" kawai tace tana dan fitar da murmushin da baikai zuci ba daga fuskarta. Tun daga harabar gidan zaka san cewa ansha baqi a gidan,bata yarda tabi ta qofar falo ba saita bi ta qofar baya tayi shigewarta dakinta,kayan hannunta ta aje ta rage kayan jikinta ta shiga wanka,bayan ta fito ta murza manta mai qamshi ta saka riga mara nauyi,ta ciro wayarta daga jaka kenan taga miscal din zunnurah,sai fuskarta ta washe da fara'a,ba bata lokaci tabi kiran,bugu biyu ta daga,abu na farko data fara shine guda ta sakar mata,bacin rai ya bijirowa shahidan,wato kiranta tayi donta tsokaneta kenan?,sai kawai ta yanke kiran,ta nufi gadonta ta hau ta kwanta rub da ciki tana lumshe idanunta,dai dai nan hasina ta turo qofar "Au yaushe kika shigo?" Banza tayi da ita kamar bata ji ba,hakanan taqi bude idanunta,don tasan qarshenta itama tention xata qara mata kawai "Shahida" hasina ta sake fada tana matsowa dab da gadon,ta dora hannunta saman filon tadan daka,sai a sannan ta ware idanunta tana dubanta "Bacci nakeji,don Allah ki barni na huta" murmushi hasina ta saki "Amma na miki jaje da zaki kwana bakiga kayanki ba wallahi,kallo ya barki" qur ta mata da idanu kafin taja qaramin tsaki ta maida kanta daya barin tana rufe idanunta,dariya ta sheqe sosai da ita sannan ta juya ta fice tana waqar amarya. Da sauri ta diro daga saman gadon ta isa bakin qofar ta saka key ta kulle sannan ta sake dawowa ta kwanta,tana gyara kwanciyar tata tana mita ita daya gami da jan tsaki lokaci lokaci,rigingine ta kwanta tana kallon roofing din dakin,idanunta a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96