Chapter 19
Chapter 19
kashewa ne,sannan ta cire wani abu a ciki tace wannan ya kaiwa anty usaina ita yafi cancanta ta sanya albarka,next month kuma idan ya sake amsa to ya fara ajiya saboda lalurorin yau da kullum,duk sai data gama kasafin ya cakude kudaden waje daya sannan yace "Qurun qus kin gama tatsuniyar taki?,toni ba haka nakeso ayi ba,da safe me mike ci idan zaki makaranta?"baki tadan cuno "Kome meye ya samu" "Good" ya fada yana cire wasu kudi ya aje "Indomie da qwai nakeson ki koma ci" idanu ta zaro tana kallonshi baki bude "Honey...me kake fada ne?" "Abunda kunnuwanki suka jiyr miki.....wannan kuma kudin kashewarki na wata gud....." "Kaga...don Allah ka tsaya ka daina wannan lissafin mana" nan sa'insa ta kaure tsakaninsu,da qyar ya yadda da nata lissafin bayan ta masa alqawarin wata na gaba ta yadda za'a sata cikin kasafin,saidai duk da haka yayi cancel kudin kashewarsa ya bata dole ta amsa saboda ya kafa mata sharadi. Koda ya kaiwa anty usaina ma itama cewa tayi ba zata soma amsa yanzu ba,ya aje wajensa zata masa magana idan lokacin daya dace yayi,haka ya dawo dasu ya miqawa shahida "Shikenan...zan saya banki na dinga tara maka,duk sanda kake da buqata saika amsa" washegari kuwa ta sayi bankin ta zuba masa harda kudin daya bata,ta nuna masa sannan ta roqeshi "Don qaunar da kakemin kada kace a'ah,za'a tara ne ka siya abun hawa ko keke ne,ko baka fadimin ba nasan tafiyar qafa kake" da qyar ya amince da shawararta,donshi a son ranta tayi hidimar gabanta kawai dasu. Wata hudu cif da fara aikinsa komai ya soma tafiya babu laifi,ta wanni fannin abubuwa da dama sun soma sauqi,cikin godiyar Allah da yadda da cewa komai lokaci ne. Cikin haka aka fitar da ankon bikin umaima,wadda take cousin ce a wajenta,ranar data kawo musu ankon wuni tayi a gidansu,har dare tana nan,sanda ta tashi tafiya anwar yazo shahidan na wajensa,mubina ce ta rakota tana nanata mata idan ta tashi dawowa ta kawo mata alawarta,qarasawa tayi wajensu shahidan tana mata sallama daga bisani tace "Ina zuba ido saikinzo siyan ankon,kuma wlh baki isa ba ba wani daya da zaki duka biyun zakiyi" "To ummata" ta fada tana hararta,don batason ta tada zancan a gaban anwar din,sun riga da sun gama maganar su tun cikin gida,da haka sukayi sallama umaima ta wuce. "Wai ina bankin nan kuwa?" "Yana cikin gida" "Idan yana kusa daukomin shi idan yana kusa" bata ce komai ba ta shige gidan ta fito dashi,bankin qasa ne ya amsa saiya sakeshi ya fadi take ya fashe kudin ciki ya bayyana,baki ta bude tana zaton itace bata bashi dai dai ba ya riqe ya fadi haka,sai taji yace "Yauwa yayi dai dai,tayani qirgawa" cikin mamaki ta duqa ta soma tayashi hada kudin,bayan sun gama hadawa ya miqa mata yace ta irga,cikin murna da mamaki tace "Da gaske ne kudi wawayene....ban zaci zasu kai haka ba wallahi" murmushi shima ya saki,walwalar da take kawai ta isheshi farinciki "Kije ki sayi ankon ko kala nawa ne,saura kiyi dinki,idan ba zasu isa ba kiyimin magana" ranta ta ba'ta sannan tace "Me kake fada ne?,kudin keken naka zaka bani kace nayi anko bayan sunkai kudin keke sabo harda canji?,kuma ma tuni umma tace zatamin daya abba guda daya" "Duk bansan wannan ba....abinda kawai na sani shahidana zata saka kaya kamar yadda kowacce mace zata saka...kada kice zakimin musu indai baso kike raina ya baci" kaita duqar "Allah ya baka haquri" dole ta fidda kudin ta sayi ankon kala biyu mayafi da abun daurawa,cikin sati uku suka shiga hidimar biki amma hakan bai hanata ganin anwar ba,shima hakan ya masa dama tunaninsa rashin ganinta. Ranar da za'ayi dinner tun safe suna gidan kwalliya,qarfe biyar da rabi na yammaci ya kirata yazo ganinta tana ina,itama yana ranta don jiya basu samu ganin juna ba basa unguwar kwata kwata suna can aikin snacks,ta kwatanta masa gidan kwalliyar,ya gane gidan saboda cikin anguwarsu ne. Sanda ya iso tuni an gama mata tata,zata wuce kuma gidan bikin ta saka kayanta kafin a soma dibansu zuwa wajen da za'a gudanar da shagalin. Dan kwalinta a hannu ta fito soron gidan don kada ya bata mata kwalliyarta,dubansa tayi yadda yayi mata kyau cikin wani sabon yadi blue black,wanda aka yiwa dinki irin na matasan zamani,bata mancewa da ita yayi shawara kafin ya sayi yadin ta kuma zabar masa dinkin qarshen wata sanda aka biya salary ya cira a ciki yayi,anwar nada wata baiwa ta daban,idan yayi dressing kai kace shi din wani ne,daga kai yayi daga danna wayarsa da yake yana dubanta,subhanallah ya fada a sarari,wani azababben kyau yaga ta qara masa,kai kace ba shahidarsa bace,sai yayi sak yana ci gaba da dubanta,abun ba qaramin dariya ya baiwa shahida ba har sai data d'an dara "Yaya anwar wucewa zanyi fa ana jirana.....tun daxun kake kallona sannan kuma kai baka ce komai ba" ta fada a shagwabe tana langabe wuya,ajiyar zuciya ya sauke sannan ya dubeta "Ba inda zan barki ki fita a haka shahida....gaskiya zuciyata ba zata iya jurewa wasu su kalleki a haka ba a filin Allah wajen bikin dake cakude da maza da mata" "To a yaya kakeso na fita?" Ta fada tana cuno baki wanda hakan ya sake tafiya da imaninsa,dan qaramin bakinta mai dauke da pink din labba yasha maroon din jambaki "Mafita kawai ki wanke fuskarki" idanu ta zaro tana dubanshi "Haba yaa anwar....haba don Allah" ta fada kaman zatayi kuka tana dan buga qafarta,fuskarsa ya hade sosai,harga Allah yana da wani irin kishi akan shahidan,yana jin kaman zai mutu idan wani ya zuba mata idanu bare akai ga batun furta yana sonta "Ashe kuwa zaki shekara a soron nan,don na rantse ba zaki matsa ko inaba indai fuskarki da wannan kwalliyar" tasan cewa da gaske yake saita rasa ya zata masa,hakan yasa ta juya ciki ta yiwa amarya umaima magana,ita tazo ta roqa mata alfarma wanda daga qarshe yace saidai ta cire eye lashes din da aka qara mata don nata ma ya isheta,sannan kuma a goge wasu abubuwan da aka sa mata a fuska,saida akayi hakan sannan ya qyaleta,duk da haka a gaba ya sakata tana gaba yana bayanta,sai faman sakin ajiyar zuciya yake,duk da an rage kwalliyar gani yake kowa ma kallonta yake,adaidaita ya tare mata bai barta ba sai daya rakata har qofar gidan bikin,yana mata sallama zai juya itama ta tubure kan dole yaje wajen bikin,yasan da biyu tayi hakan don bai fiya zuwa wajen fate fate ba,to amma abinda bata sani ba gata tayi masa,don har yanzu hankalinsa bai aminta ba da zuwanta wajen ita kadai,gani yake tafi kowacce mace kyau,hakanan idanun kowanne namiji yana akanta "Zanje na dawo,idan kun gama shiryawa kimin magana" tana masa dariyar cin galaba ta shige ciki. Qarfe shida aka soma daukan 'yammatan,a sannan tuni ta yiwa anwar waya,shida da rabi ya kirata yace ta fito yazo,su biyu ne ita da 'yar anty umma yayar ummanta,ga mamakinta yana jingine jikin wata qaramar mota mai kyau qirar kia,ya sauya shigar jikinsa,wannan dinma yadine wanda tare ya siyesu da wancan,saidai wannan ruwan madara ne lallausa,shima bamai tsada bane amma sai taga kaf mazan wajen ba wanda ya kamoshi a kyau duk dacewa jayan jikinsu yafi nashi tsada nesa ba kusa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96