Chapter 60
Chapter 60
daya,haka soyayya take?,haka masoyi yakewa masoyinsa?,sai taji ya sake sireta,daya zama mai dogon nazari da dukka abubuwan da suka faru yanzu basu faru ba Ranta ya ninka bacin da yayi,hankalinta taji ya tashi,da qyar ta bude baki cikin muryar kuka tace "Mugu azzalumi,ba ruwanka da kowa sai kanka,ba ruwanka da damuwar wani sai taka,ka tanadi mugun nufi akaina kan abinda baka da cikakkiyar hujja a kai...." "Wacce huja nake nema baya ga wanda na samu....!" Ya juyo a fusace ya fada idanunshi da suka kada zuwa jaa suna kanta "Ba hujjar kake nema ba,kanayin komaine don ka wulaqantani dama,ka shirya komai ne donka tozartani,to Allah ya fika,ba zaka taba samun nasara a kaina ba,nuradden kuma idan Allah yaga dama kai baka isa ka rabani dashi ba"itama ta fada cikin tunzura fushi da bacin rai "kome zaki fada dai dai ne,duk yadda kika fassara lamarin a ranki ko a bakinki kisa a ranki haka ne,any ways ma ni nasan na taimaki rayuwarki ne,ko kina tunanin wancan wawan idan yaji wace ke a baya zaici gaba da haukan da yake a kanki?,kinga 'yammata....koki sawa ranki sauqi ko kar kisa duk uwar ubansu daya" kai take gyadawa bacin rai na cinta,idanunta fes cikin nashi,ji take kaman ta shaqe anwar din,a yanzu babu halittar data ji ta tsana sama dashi "Zan saka salamar duk da bakayimin fatanta ko burin samunta,amma ka sani....tsugune bata qare ba,don babu abinda zanyi da masoyi irinka nawar!,ka shirya tarbar duk wani abu da zai tunkaroka!" Tayi lafazin da alama wani abu ya motsa ranta qwarai,duk da murta na a raunane amma amma fuskarta da qwayar idanunta na bayyana jarumtarta,wani malalacin murmushi ya saki ya sake matsowa inda take,wannan karon har qamshin turarensan nan data sanshi dashi yana busowa zuwa hancinta,ya kafeta da idanunsa,muryarsa can qasa kamar mai shirin furta kalaman soyayya a gareta yace "A shirye nake,kece zan gayawa ki shirya zama dani idanma ba'a shirye kike ba,yaushe kikeso wasan ya fara?" Ya fadi cikin halin ko in kula,ganin kallon da yake mata bacin rai ya sanya ta fashewa da kuka sosai ta zube saman kujerar tana rufe fuskarta da tafin hannunta,saiya tabe baki yana isa inda hularsa take yasa hannu ya dauka yana cewa "Ashe raguwa ce ta gaske,tun yanzu?,wasan namu kuwa zaiyi iri qarkon da nakeso?" Ya dora hularshi saman kansa sanda ya qarashe maganar,saiya sanya hannunsa cikin aljihunsa ya ciro kudade sabbabi masu dan yawa ya aje hannun kujerar da take kai yana cewa "Ga kudin zance nan,kuma bance a sayi abunda za'a bugu da kudina na,idan aka siya Allah ya isa na" sosai maganar ta doketa,tana niyyar daga kai ta dubeshi ta fuskanci ya juya zai fita ne,har yakai bakin qofa sai yasake cewa "Ammmm..." Yana dawowa da baya,kanta yazo ya tsaya hannunsa daya a aljihun wandonsa dayan kuma yana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa "Karki manta da sadakina akanki,shaidu kawai za'a tara a daura,ban lamince ki kula kowanne dan iska ba,ciki harda wannan looser din,idan kuma kikayi hakan shima Allah ya isa ban yafe ba" saiya sassauta murya ya sauko da kansa qasa qasa gab da ita "Ina fata har yanzu wasu daga halayen anwar basu bace miki ba daga kanki,mutum ne mai kishi,ina da kishi kan mace koba wadda ban biya sadakinta ba bare wadda na cire halalina sa nasha wahalar nema zafi da sanyi nabiya" a fusace ta bude fuskarta saboda yadda maganganunshi suka isheta,saita ganshi dab da fuskarta,cikin bacin rai da muryar kuka take cewa "Sadakinka din banza da wofi,idan kana son nunan kudinka wata tsiya ce kaje ka karbi sadakinka idan har ka isa cikakken namiji" tsaf ya karanci bacin ran dake kwance muraran saman fuskarta,saidai yadda yake jin quna yana tunanin bata jin haka,duk sanda zai kalli fuskarta yana tuna sanda aka sauketa ne a gabanshi,cikin maye,cikin jini,pant dinta a gabanshi aka cilloshi,wani ya riqe zuwa jikinsa gaban idanunsa,saiya runtse idanunsa kana ya bata baya ya soma takawa "Idan kin isa ke kije ki karbo kin kiga idan ban amsa ba,dama taimako nayi kuma na fuskanci ke bakiga hakan ba" daga haka ya qarasa ficewa daga dakin,sake rushewa da kuka tayi,ta tsani kalmar taimakon nan,wannan wanne irin cutace?,ita zai taimaka. Cikin gida ya qarasa,daada na rumfarta a zaune ita da hasina,saiya cire takalmansa ya zauna saman tabarmar dake shimfide qasan inuwar bishiyar dake tsakar gidan,daadan tayi tayi dashi ya shigo amma yace wucewa zaiyi,dole ta fito ta zauna daga gefan tabarmar itama "Zan wuce daada,ina tunanin rana ita yau za'a kawo lefe,to bansan inda za'a kai ba,can wajen umma,ko nan garin ko kuma gidan uncle hisham?" "Babu damuwa akai can hidan hashimun tunda acan za'a yi duka bikin,muma can zamu tattara ai mu tafi" "To daada,Allah ya saka da alkhairi ya qara girma" ya furta yana dan sadda kanshi qasa alamun girmamawa "Ina kuma ta shiga?" Daada ta tambaya,ya fuskanci shahida take magana,saiya saki murmushin daya qwata fuskarshi duk da baikai masa qasan ranshi ba "Tana daki tana kukan bata sona can na barota" kama baki daada tayi tana salati harta baiwa anwar dariya,harya miqe ya aje mata kudi ma sam bata kula ba tana ta jajjabi tare da sillewa shahidan hasina na dariya,sai daya sanya takalmansa sannan ya kalli hasina "Taimaka kije ki fito da ita daga dakin karta rube" dariya hasina ta saki sosai,abun saiya qayatar da ita,ya yiwa daada sallama suka fice zuwa soron gidan shida hasina. Bakin qofar dakin ya coge ya yaye labulen bayan hasina ta shiga dakin,ta isa inda take dunqule tana gursheqen kuka "Saikace yau akace za'a kaiki?,taso da Allah karki tara mana jama'a" hannun hasina ta buge tana jin takaici yana cikata,duk maganganunsu da daada tana jinsa,tamkar ma ya raina mata wayo ne,ko yana tunanin 'yar qaramar shahida daya sani a baya ce wannan? "Matsa hasina barta,bari na rage miki aikin na dauketa zuwa qofar soro saiki qarasa shiga da ita ciki,da sauri ta bude fuskarta,idanunta da sukayi jawur zuwa fuskarta ta kalleshi dasu "wallahi wallahi ka sake ka tabani sai kayi dana sani!" Ta fada a kausashe "Meye hakane shahida?" Hasina ta tambayeta tana dubanta cikin mamakin kausasa lafazin da tayi,dubanta yake sosai,yana son yace shine farau?,amma idanun hasina yasa ya maida amsarsa "Wallahi wallahi kinji nima na rantse matsawar baki tashi kin shige ba ko abinda yafi danasani zanyi saina dangana dake har rumfar daada" saiya maida dubansa ga hasina dake tsaye tana kallon dramer "Ina cikin mota a qofar gida,minti biyar na bata idan ta dara hakan bata tashi ba ki fito ki gayamin" kai ta gyada ya saki labulen ya taka a sannu ya fice daga soron. Bata buqatar duk wani abu da zai kawo wani kusanci tsakaninta dashi,so take ya tafi yabar gidan saboda haka ta miqe tana hada hanya,hasina ta dauki kudin dake aje inda ta tashi ta bita dasu a baya,ko kallon dada dake tsakar gida tana mita batayi ba ta shige rumfar daadan ta zube saman kujera,saita dora hannu aka ta fashe da ihun kuka ko zataji salamar radadin da take ji cikin ranta,hasina kallonta take idanu a waje cikin rudewa tace "Meyw haka ne shahida kike kamar wata 'yar shekara goma,ya zaki tara mana jama'a?" Takai qarshan maganar sanda daada ta runtumo cikin dakin tana tambayar ba'asi "Au ihu kike?"
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96