Chapter 75
Chapter 75
tana kallon mai shigowar,sa'ida ce saidai ita batasanta ba,fuskarwa a washe ta qaraso falon tana takowa a hankali tana waigawa,da alama ba'asan tayo.nan ba,dab da shahida ta zauna tana kallonta "Anty,saike kadai?,nayi nayi da ummi tabarni nazo tace a'ah zamu takura miki kina hutawa ne,da qyar na samu na sallabo" murmushi shahida tadan saki tana duban sa'ida "Ina yini anty,ya gajiyar biki" "Lafiya lau,me sunanki" "Sa'ida,'yar anty usaina ce ni,kuma qawar uncle anwar" girarta shahida ta dage duka biyun tana dubanta alamun tambaya,dorawa tayi "Wallahi kun dace sosai anty keda uncle,uncle ya samu mata me kyau" tana murmushi sosai ta fada tana kuma sake kallon fuskar shahidan data ji tana burgeta,murmushi shahidan ta kuma saki "Ko?" Tace cikin sigar tambaya,kaita kada "Qwarai kuwa,amma anty,don Allah ki kularmin da uncle dina,wallahi inason uncle anwar,yana da kirki sosai,yana sonmu shima,yana kula damu sosai da sosai,don Allah anty" saita tsaya tana sake dubanta kafin ta kuma sakin murmushi,ta dora hannunta saman hannun sa'ida "Uncle din naki nima zai iya kula dani ne sa'ida?" Dariya ta saki "Tabdi,sosai kuwa anty,kinsan uncle anwar kuwa?,ai matarshi ta caba" saitayi qasa da murya "Na zaci fa zai iya aurena harna cewa ummi ina sonshi,ranar saida na daku sosai,ashe babana ne" dariya ta kubcewa shahida da sa'idan duka,da sauran dariya a fuskar shahidan tace "Babanki ne sa'ida,amma kita addu'a Allah ya baki wanda ya fishi nagartar halaye" "Akwai wanda yafi uncle dina kuwa?" Ta fada cikin tantama da tunani,kaita jinjina "Qwarai kuwa,duk wanda kika gani kome kika gani a duniya akwai wanda ya fishi akwai wanda baikaishi ba akwai dai dai dashi" "Tohm shikenan......" Bata qarasa maganar ba suka jiyo taku ana nufowa wajen,saita fiddo idanu "Na shiga uku anty,Allah yasa ba ummi bace" riqe hannunta tayi "Karki damu,zance nina kiraki ki tayani hira" shuru sukayi suna jiran ganin wanda zai shigo din. Sallamar mutum biyu ce,ummin sai muryar anwar daga bayanta,mummunar faduwar gaban data sanya shahida maida kanta cikin mayafi ta saukar mata,ummi anty usaina ce a gaba sai anwar din daga bayanta,idanunta akan sa'ida nashi idanun nakan shahida da kanta ke sunkuye lullube da mayafi,kama baki tayi "Na shigesu ni usaina,sa'ida...sa'ida ki shiga hankalinki da wannan rawar qafar taki,dama da akacemin ba'a ganki ba nan kikayo?,to tashi ki wuce ki bama mutane guri" da sauri ta zame hannunta cikin na shahidan sannan ta miqe,duk da haka da zata gifta anwar din saida tace "Uncle,kayi kyau sosai yau,amma wallahi in gaya maka gaskiya?,anty shahida ta fika kyau ashe" anty usaina batasan sanda dariya kubce mata ba,yayin da murmushi ya subuce masa shima ya bita da kallo harta fice daga dakin,ba ruwanta hakanan take,idan taga gaskiya saita fada,kusan halayenta suna kamanceceniya dana mahaifiyarsu,duk cikin yaran anty usaina tasu tafi zuwa daya,kusan sanda aka haifi sa'ida tare sukayi rainonta shida anty usainan tun lokacin mahaifansu suna raye,idanunsa ya sake saukewa akan shahidan a hankali duk da bai ganin fuskarta,yana tsaye a wajen har anty usaina ta zauna "Zauna daga can" ta fada tana masa nuni da inda takeso ya zauna din,kujerar da shahida ke kaine,duk da cewa mai yalwa ce amma saiya zauna a hannun kujera,cikin hikima da nutsuwa ta soma magana dasu "Alhamdulillahi rabbil Aalim,komai na rayuwa a tsare yake zuwa daga wajen ubangiji mai kowa da komai,basai na tsaya wani tambaye tambaye ba don nasan ba amsa zan samu daga gareku ba,abunda nakeson na fada shine,wannan auren naku ya isheku dama sauran mutane ishara,kun rabu da juna kun guji juna ba tare da dayanku ya sake tunani Allah zaiyi ikonsa ku sake haduwa a wannan bigire ba na aure,wannan kadai ya isa ya nunawa bawa yana tashi ne Allah yana tasa,ta Allah kuma itace dai dai,saboda haka ku sanyawa zukatanku salama,ku zauna da juna cikin aminci da bin umarnin mahalicci,kada ku yiwa Allah butulci wanda ya baku aron rai da lafiya ya kawoku wannan lokacin koda cikin zukatanku bason hakan kuke ba,dubunku na nan na fatan samun kamar takun,ya sake hadaku a sanda kowannenku rayuwarsa ta sauya ta samu ci gaba,ta yuwu hikimar rabuwar daku dama don kowanne ya cimma gacinsa ne,wanda wala'alla idan kuna tare da zaku cimma wannan abun ba,ku kauda hayaniya da tashin hankali ku ajeshi idanma kun daura azamar hakan,kuyita addu'ar Allah ya baku mafita ya sanyaya zukatanku" saita waiwaya ta dubi anwar "Kai kaine babba sannan kaine shugaba,kai keda hankali fiye da mace,sabida haka fiye da rabin nauyi da yanayin yadda zamanku zai kasance ya ta'allaqa a wuyanka ne,kasan komai basak na fada maka ba,iyayenmu kafin su rasu makarantace a gareka,ka dauki matarka ku tafi daga kai sai ita,ina muku fatan alkhairi,shahida...Allah ya bamu alkhairinsa kinji" kasa magana tayi kunya na kamata,ta fuskanci hakan sabida haka tayi murmushi taga bari kawai ta murje mata kunyar a wuce wajen "Ki daina kunyata,don kincemin bakison anwar wallahi banga laifinki ko daya ba,hasalima burgeni kikayi,donko nice kw abinda zanyi kenan,kawai saika rabu dani tsahon wasu shekaru ka zagaya ta bayan fage ka aureni haka akeyi?" Ta qarashe maganar tana duban anwar gamida harararsa "Kuma ka nemi yafiyarta kukan daka sa ta dinga yi da aurenka data yi bayan bata shirya ba bata amince ba" murmushi ya qwace masa mai dan sauti,itama antyn tana murmushin ta fice ta barsu. Shuru ya ratsa dakin na wasu mintina masu dan dama,idonsa akanta da yake lullube,zuciyarsa na masa bitar wasu shekaru can baya,yasha kwana idanunsa biyu yana wassafa yaya zai kasance duk randa shahida ta zama mallakinsa,yasha raba dare yana tsara ranar da irin abubuwan da zasu faru a lokacin,ga komai yazo ga lokacin yazo saidai cikin bahagon yanayi da dabaibayi,ajiyar zuciya ya saki a bayyane sannan ya furta cikin sanyin murya "Tashi mu tafi" yi tayi kaman batajishi ba,yayi tsai yana dubanta,ya tabbatar taji,har tsahon minti guda sannan yace "Kin sani sarai tun da can banason musu da taurin kai ko?,indai zaki dauki wannan dabi'ar zakisha wuya a wajena" daga haka ya miqe yayi gaba,tasan idan ta bari yafice batasan hanya ba,dole ta miqe itama ta bishi". Bangaren ajiye motocin gidan suka isa,yasa muqulli ya bude motar ya shiga,saita soma qoqarin bude gidan baya da zummar zata shiga,lock ya sakawa qofar ba tare daya waiwayo ya dubeta ba,hakanan ta gaji da tsaiwa ya yunqurin budewar ta matso gidan gaba ta bude,a hankali ta shiga ta zauna sosai sannan ta kame jikinta waje daya bayan ta sake jan mayafinta ta rufe fuskarta,karon farko bayan wasu shekaru masu tsayi ta sake hada mazauni dashi cikin mota,gaba dayansu jinsu suke banbarakwai,kowa yanaji kamar yana tare da baqonsa ne,ya dage dukka gilasan ya kunna ac dukda sanyin dake dan kadawa a garin,ya tashi motar suka fice daga gidan. Wani tuqi yake kaman bazasu gida ba ko kuma yana lallaba kwalta,duk da titin da sukabin fetal yake babu yawaitar jama'a sai haske fitilun titi tako ina,shuru ya ratsa motar babu me cewa komai har suka isa wani waje da sukeda saida kayan ciye ciye,kama daga ice cream,burger shawarma kaza da tsire da sauransu,saida yadanyi gaba kadan inda babu mutane sannan yayi parking,ya kashe motar ya fita. Bai jima ba ya dawo hannunsa dauke da leda ya sakata a sit din baya,sannan ya tashi motar sukayi gaba,hannunsa ya saka ya kunna rediyo freedom wanda minti biyar ya rage su fara shirin siyasa na kowanne
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96