Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 58

Chapter 58

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,291 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

motar wani ta sabbabawa rayuwarta bane,tabon da har yanzu bata daina jin dacinsa ba yana zaga jiki da rayuwarta gaba daya. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Qarfe sha biyu da minti arba'in da biyar tayi sallama falon daada,hasina 'yar gidan qanin abbanta ce zaune ta daga kai cikin mamaki da farinciki ta amsa sallamar "Mutan kano,yau a gari?,ni har nayi fushi fa,wai shahida kizo har garin nan kwanaki amma ki kasa leqani,gaba daya kin watsar dani kaman wadda ta miki wani mugun laifi?" Murmushi shahida tayi tana zama kan daya daga cikin kujerun gami da cire mayafinta ta aje gefe,iskar fankar da aka qurewa gudu cikin falon tana kadata gami da shigarta tako ina sakamakon zafin da ake zabgawa da kuma uwar rana "Kiyi haquri hasina,ba'a son raina ba wallahi,wannan tsohuwr ce ta min laifin daya shafeku,amma kiyi haquri zanzo in sha Allahu" cikin murmushi hasina ta tabe baki "Kedai bansan me ya dameki ba,koda yake an auna arziqi da aka samu ma kika ci gaba da zuwa katsinar da kika yiwa yajin aiki wajen shekaru hudu" murmushin da baikai har zuci ba shahida tayi tana cire agogon hannunta "Yanzun ma mawuyacine idan ban koma muku yajin aikin ba ai" ta qarshe fada wani abu na takore mata wuya idan ta tuna kasassabar dasu daada suka aikata mata,saidai takanji sassauci idan ta tuna tana da hope a yau,qasa qasa da murya hasina tayi "Hala ta kusa kwatanta miki abinda taso yimin kenan?" Kallonta shahida take ba tare da tace komai ba tana son jin qarin bayani "Wai in gaya miki matarnan daga zuwa mata hutu shikenan tasa aka mata kiran saurayina qafa da qafa wai ya kamata ya fito hakanan,wannan shekarar ta shirya aurar da jikokinta,wai basai ya dorawa kanshi wata dawainiya ba yayi abinda addini kawai yace masa ya wadatar Allah ya sawa auren albarka" tagumi da haba shahida tayi kawai tana jin wannan bayanin,ita kenan ta mata dakyau ma data amshi kudin aure,amma gwara hasina da ita sau dubu "Hasina kukan dadi kike,kinsan me daada tayimin?" Kai ta girgixa tana duban shahida "Kudin aurena da sadakina suka amsa gaba daya ba tare da na sani ba,kuma ba tare da nasan waye zan aura din ba,kawai don bincikensu ya basu managarcine suke ganin ya dace dani" idanu waje hasina ta fito dasu tana duban shahida,kafin tace wani abu suka jiyo maganar daada daga tsakar gida wadda ta fito da wanka ne tana fadin "Da kika shigo kika bar akwatin naki rana na duka waye zai dauke miki" dole kowanne yaja bakinsa yayi shuru harta iso falon,saita kalli idanunsu na 'yan sakanni kana ta tabe baki "Magulmatan banza da wofi" daga haka tayi wucewarta daki donta saka kaya,yayin da shahida cikin dacin rai da baqincikin daya taso mata ta fito tsakar gida ta shiga bandaki tayi fitsari sannan ta daura alwala nan bakin famfo ta shigo da akwatin nata. Qarfe daya da minti ashirin na rana tana tashi daga saman abun sallarta wayarta ta dauki tsuwwa,hasina ta miqo mata ta duba,nuradden ke kira ko bai fada ba tasan ya iso ne,gabanta taji yayi mummunar faduwa ta daga idanunta ta kalli daada data qarawa fura da nono ruwa take sha,saita kalli hasina,suka hada idanu ta mata signa sannan ta fita tsakar gida,ba jimawa ta biyo bayanta,janta tayi bakin kitchen ta gaya mata abinda ke faruwa "Tabdi,kina tunanin akwai abinda zai sauya dada?,amma arashin tayi akan bar arha,bari na gaya mata baqo zai shigo" ta juya tana komawa,kafin takai ga shiga falon yaro ya tamfatsa sallama yana rangada fadin wai ana sallama da shahida,daada dake zaune a rumfarta tayi katsu tana jiran taji wanda zaiyi magana cikinsu,shuru sukayi ba wadda ta amsa,sai daadan ta kira yaron ya qaraso bakin rumfar "Waye yake sallama da ita?" "Wani ne,wai nuradden daga kano" "Kano?" Ta sake tambayar yaron,saiya kada kai alamun eh,shuru na sakanni sannan tace "Jeka ce masa ya shigo" juyawa yaron yayi ya fice ita kuma ta kira shahida da hasina gaba daya "Xauna nan" ta nunawa shahida gefanta,ba musu ta zauna jiki a sanyaye,ta dubi hasina "Bude firinjin can ki ciro ruwa da lemo" ba musu hasinar tayi yadda tace,dada ta nuna mata shimfidar daddumar data gama salla akai bata kai ga daukewa ba tace ta dora saman nan. Cikin minti biyu kacal nuradden ya bayyana cikin falon,yaci manyan kaya yanata qamshi,bashi kadai bane shida wani abokinsa ko kuma ince amininsa ne,duk da dan uwanshi ne,cikin girmamawa suka zauna saman shimfidar suna gaida daada,ta amsa musu kadaran kadaham,yayin da idanun nuradden ke kan shahida. Tayin ruwa da lemon tayi musu,Sayyid abokinsa ya bude ya zuzzuba musu a kofi,kusan shi kadai yasha,yana sha suna dan taba jira jifa jifa da daada tana tambayarshi kano,kasancewar ta dauki shekaru masu dama rabonta da ita,tun kafin rasuwar babansu shahida. Sai da suka kammala tasa hasina ta zuba musu abinci,saidai sunce a qoshe suke,tilas ta rufe ta maida kitchen din,shuru ne ya ratsa na dan wani lokaci sannan sayyid yace "Am...daada,abinda yake tafe damu dama magana ce game da shahida da kuma abokina nura,duk da nasan bata sanar miki da zuwanmu ba" "Haka yake" a nutse sayyid ya fayyacewa daada komai,tayi gyaran murya tana dubansu "Nasan cewa kuna da labarin an bada shahidan harma an karbi sadakinta,idan ma ta boye maka bata gaya maka ba ni ya zama wajibi na gaya maka gaskiyar abinda ake ciki" "Ta fadama bata boye ba daada" "Yauwa...an riga da an karbi sadakin yaron,kuma a shekarun da Allah ya bamu bai kamata kuma ace muna magana biyu ba,uwa uba sanin kanka ne cewa haramunne neman aure akan nema,koda ciniki akan ciniki ne haramun ne bare nema kan nema,matar mutum kabarinsa,Allah ya qaddari haka tun farko shi yasa ya hukunta jinkirin zuwanka garemu,saboda haka ina mai yaba maka bisa soyayyar daka nunawa jininmu,ina kuma mai maka fatan samun dacewa da wata matar data fita,sannan ina mai dorawa da baka haquri,kayi haquri,Allah ya sawa zuciyarka dangana" sayyid ne kawai ke amsawa da amin,yayin da gaba daya jikin nuradden ya mutu murus,zufa ta dinga yanko masa tako ina "Mun gode sosai da karamcin da akayi mana" sayyid ya fada sanda suke miqewa bayan sun ajewa daada kudi "A'ah yaro...nifa bazan karba ba,zoka dauka ku wuce Allah yayi maka zabi mafi alkhairi" qememe suka qi dauka haka suka fice,daada ta juya ta kalli shahida dake zaune gefanta tana sharbar qwalla "Saikije ki sallamesu" daga haka ta miqe ta tayi wucewarta daki,sanda ta cimma qofar gidan tuni su nuradden sun wuce,sai tex daya turo mata na anjima zai kirata don yanzu baida nutsuwar tsaiwa,sulalewa tayi ta zauna gefan gadon,tana qoqarin hadiye kukanta. Shigowar daada dakin ya sanyata daga kai tana kallonta,tana daga tsaye ta soma magana "Kin kyauta sosai da kika sanyashi yazo kika toxarta mu,daa can kinsan yana sonki baki bashi dama ba har saida muka yanke hukunci a kanki?,ko kina tsammanin mu warware maganar da mukayi kaman qananun mutane?,to idan ma zaki kwantar da hankalinki ki nutsu waje guda shiya fiye miki alkhairi,ki shirya kuma ki dakaci zuwan gobe,mijinki da yardar Allah zaizo kuga juna,idan kinga dama kuma idan yazo din ki watsa mana qasa a idanu" daga haka daadan ta juya tayi ficewarta,sai kawai shahidan ta bita da kallo ranta na quntata,koma meye shi ya janyo mata,kuma shima

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});