Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 44

Chapter 44

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,310 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

dan uzuri ya riqeni" "Toh uncle" daga haka dukkansu suka kashe kiran,tunani ya shiga sosai,sai salon tuqin nasa ya koma slow kaman bazashi gida ba,tunaninta ne ya dawo masa sosai tun farko alaqarsu irin wanda bai taba tsintar kansa a ciki ba. Sai daya kashe wasu mintoci kafin ya isa gida,a gajiye ya isa falonshi ya fada saman kujera yana lumshe idanunshi kafin ya budesu,yanason manta komai amma abubuwan nata zarya bisa qwaqwalwarsa,sai kawai ya miqe zuwa bedroom dinshi,ya cire kayanshi ya daura towel ya shige toilet ya sakarwa kansa ruwan sanyi sosai. Ya jima zaune gefan gadonshi yana neman bacci ya sureshi amma abun yaci tura,saiya miqe zuwa wani safe na musamman dake dakin,ya saka lambobin sirri ya budeshi,envalope din daya tsani gani yau da kanshi ya daukota,ya bude abubuwan dake ciki gaba daya,hotunan ciki suka bayyana,take kanshi ya soma daukan zafi,idanunsa suka kada jazur dasu,saiya kasa ci gaba da kalla ya soma tattaresu yana tuhumar shahida cikin ranshi "Me yasa shahida me yasa?,me yasa za k iyi haka,me yasa kika tarwatsani,me yasa kika tarwatsa duk wani buri da fata na?" Ya qarashe maganar yana cilla envalope din cikin abun ya maida ya rufe,saiya fada saman gadonshi yana maida numfashi gami da ambatar "Hasbunallahu wa ni'imal wakil" *WASHEGARI* Qarfe goma da minti arba'in ya isa gidan cikin dinkin shadda wadda tayi masifar masa kyau da fito da kyawunshi. Dukkansu suna falo suna karyawa "Uncle sannu da zuwa,ina kwana" suka dinga fada daya bayan daya,fuska a sake yake amsa musu yana tambayar lafiyar kowa suna amsa mishi "Ina ummin taku?" "Tana sama tana wanka" sa'ida ta bashi amsa bakinta fal da zance,turarenta ya ciro ya miqa mata tasa hannu biyu ta amsa cikin Murna "Uncle na gode,na gode" "Yauwa" ya amsa yana duban tashar da suke kallo,hijra tv waqoqi suke sanyowa na mawaqa daban,sa'ida ce ta tashi daga cin abincin da take ta dawo kan kujerar da anwar yake kai "Uncle" ta fada qasa qasa,waiwayo yayi yana kallonta "Uhmmm" "Maganarmu ta jiya...." Shuru tayi ta ganin saukowar anty usaina,suna hada ido tahau rarraba idanu,miqewa tayi tsaye kafin ta iso,ta jefa mata harara "Ku kwashe farantan nan kukai kitchen,munaya ki hadasu ki wanke,ke kuma uwar zance ki bita ki daura abincin rana,kafin ki gama laqaqin naki kin gama" duka suka miqe falon ya zama daga ita saishi,ta zauna tana dubanshi "Jiya sai kuma na jika shuru,sa'ida tace ba zaka samu shigowa ba" yana shafa kanshi yace "Wallahi,jiyan na taho wani uzuri ya tsaidani" "To Allah ya rufa asiri" a mutunce ya gaisheta ta amsa masa cikin kulawa sannan daga bisani tace "Ko a hado maka abincin kari?" "Eh to...amma bada wani yawa ba" dauke idanunta tayi daga kanshi ta mayar qofar kitchen din ta kira sa'ida tace ta hado mishi. Yana karyawan suna taba hiran,a hankali shurunsa yafi maganarsa yawa,hankalinsa ya karkata kan hijra tv da suka sako waqar jarumar mata,saita dinga taba ranshi kadan kadan,tana tuna mishi wani lokaci can baya,a nutse ya dauki remote din dake aje kusa dashi ya sauya tasha,dai dai sanda anty usaina tace "Anwar....ya kamata fa ace ka soma shiri,biki saura sati hudu amma banga alamun hakan tattare dakai ba"sai daya hadiye abincin bakinsa sannan yace "to me zanyi anty bayan wanda nayi" "Kamar ya me zakayi?,haka zaka aurar musu diya babu maganar lefe babu komai?" Aje cokalin hannunsa yayu sannan yace "Nifa anty,da zaki yadda da maganata ayi haquri a qara min wasu watanni" "Saboda baka da gidan sakata ko baka da kudin yi mata lefan?,ko sadaki ne baka dashi?" Murmushi ne ya subuce masa ba tare daya shirya ba "Au dariya ma nake baka ko anwar?"kai ya girgixa dariyar na kubce masa "ni na isa antyna,kawai dai....naga kina yin nafisa ne da yawa" zamanta ta gyara sosai,alamun maganar da zata masa nada muhimmanci "Ba haka bane anwar,ka fahimceni,mutanen nan suna da kawaici da dauke kai,basu da son zuciya ko tilasta mutum,da wasu ne su yadda suke ganin sun isa dakai dinnan kawai zasu baka umarnin ka auri diyarsu ne,su saka kuma ranar biki da komai baka data cewa,uwa uba ina gudun halayyarku ta maza kafa kazo ka murje ido kace ka fasa ka barmu da kunya" murmushi yayi yana kallon qasa,shikam dama bayajin zai dauki irin wadan nan abubuwan,dalili kenan da tun farko ya zabi yaci gashin kansa,bai qasan wani bare ya tilastashi koya tauyeshi,rama halacci dai wannan yasan abune mai kyau,kuma shine hujja daya,dalili daya da zai sakashi ya haqura ya auri nafisa "Anty kiyimin kyakkyawan zato,ba abinda zai faru da yardar Allah indai daga bangarena ne,abinda kawai yasa na buqaci qarin shine,akwai wata 'yar tafiya da zanyi ta wata uku,kinga zaifi kyau naje na dawo,hankalina ya hadu waje guda,duk abinda za'ayin ma sai ayin,zan baki kudin da zai isa a hada lefan kafin wucewata da sauran abubuwan da aka sabayi na al'ada" ajiyar zuciya ta saki "Shikenan,yanzu ya za'ayi ka shaida musu?" "Wannan duk ba damuwa bace,zan samu alhj da kaina,baida matsala,yasan da tafiyar tawa dama" "Shikenan,Allah yayi mana jagora ya bada sa'a" "Amin anty" daga haka suka shiga hirar data shafesu,sai wajejen shabiyu na rana ya baro gidan shima ganin haduwar hadarine,baya n ya tambayesu ya tabbatar basu da wata damuwa. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Cikin harabar gidan yake zaune cikin motarsa,murfin motar side din da yake a bude yake,hakanan ya ziro qafarsa daya waje,iska mai dadi dake kadawa tana shigowa har inda yake,iskar na masa dadi qwarai,,dalilin kenan daya sanya idanunsa lumshewa yana shaqarta har tsakiyar kanshi,knocking glass din motar yaji anyi,ya ware idanunsa a hankali suka sauka kan fuskar nafisa dake tsaye cikin kwalliya tana dubanshi daga sama har qasa,duk da fuskarta qawace take da kwalliya amma annurin cikinta kadan ne,shigarsa take kallo,yayi kyau cikin qananun kaya baqaqe qafarshi saye cikin wani booth mai bala'in kyau,quruciyarshi da kyanshi muraran suka bayyana,sai taji sonshi na sake shigarta,baqinciki da bacin ran daga bikinsu ya sake mamayeta har hakan ya bayyana kan fuskarta "Whats wrong with you" ya tambayeta idanunsa qyar a kanta,saitayi narai narai da idanu,qwayar idonta cike da qwalla,,da alama gab take da sakin kuka,shuru tayi ba tare data amsa ba,fitowa yayi gaba daya daga motar ya rufe sannan ya jingina da ita hannayensa shima harde a qirji "Me ya sameki kuma?" "Au..baka ma sani ba zaka cemin?" Hannayensa ya watsa yana harde qafafunsa sannan ya soka hannayensa a aljihun wandonsa "Eh to,xai iya yiwuwa ni abinda nake tunanin shi zai saki kuka ke a wajenki bashi bane" "Me yasa anwar me yasa har qarin watanni uku bayan wata gudan dake gabanmu" girarshi biyun ya dage yana murmushi "Au,kice ke kukan aure kike,to saurin na meye?,wata hudu kawai saiya zama damuwa?" Langabe kai tayi tana dubanshi "Ni sai ya zama damuwa mana a wajena idan har wajenka bai zama damuwa ba,dama ni na damu dakai ai na sani" murmushi ya kuma saki,yadan tafa hannunshi kadan "Abinda ya faru ya riga ya faru,sai a jira zuwan lokaci" "Ai shikenan,yana iya"agogo ya kalla sannan yace "Zan wuce" idanu ta zaro "Duka duka yaushe kazo?,haba ya anwar mana don Allah,hajiyama fa tace ka shigo kaci abinci" "Sauri nake nafisa,amma idan na samu chance anjima zan dawo,idan ban dawo ba kuma sai gobe" ya qarashe maganar yana bude motar,sai daya shiga sannan ta mayar masa da

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});