Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 57

Chapter 57

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,291 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zaka yiwa fuskarta kaga yadda ta fada,ta dashe hakanan tayi fayau,duk yadda anty zubaida taso ga kwantar mata da hankali kan lamarin hakanan taji hankalinta ya kasa kwanciya,tana ji ba auren dole za'a mata ba,a'ah nata ya xarce wannan ya koma auren qarfa qarfa. Tunda ya hangota ya fito ya tsaya yana jiran qarasowarta,ji yake kamar ya isketa ya tarbeta,tana isowa suka hada idanu sai taji zuciyarta ta karye gaba daya,tausayin nuradden din ya kamata fiye da ita kanta,don dama ita tuni ta sallamawa soyayya bare tayi mata kamun da zata jigata aduk sanda ta tashi gwada izzarta,saidai ko babu komai sabo mugun abu ne hakanan turken wawa ne,da hanzari ya zaga ya bude mata daya seat din ya kalleta "Shiga ki zauna,kar tsaiwar tayi miki yawa" karon farko ba musu cikin kasala ta zagaya ta shiga din,saidai duka qafafunta na waje,shima saiya zagaya ya shiga mazaunin direba yabar qofar a bude. Idanu ya zuba nata gaba daya yana hasaso ta ina zai soma daukar rashinta,sam yana jin bazai iya ba,a hankali ta bude baki zatayi magana ya daga mata hannu ya tsaidata "Karkice komai shahida,maganar gaskiya bazan iya rabuwa dake ba,bazan iya rabuwa dake ba shahida matuqar ba aure aka daura miki ba,zanci gaba kuma da yaqi tuquru don ganin na sameki,koda hakan na nufin zanje wajen daada da kaina na roqeta tabarmu tare ne" da hanzari ta bude baki "Ina nan ina gwada sa'ata,kuma ina saka ran samun nasara,idan hakan ya cimma tura zan sadaka da ita daadan taci daga bakinka" ajiyar zuciya ya sauke yana kallon shahidan,wani qaunarta yake sakeji,baya fata ko sau daya ya sakejin kalmar rabuwa a tsakaninsu. Tsahon mintina ashirin suna tare suna baiwa juna baki kafin yayi mata sallama yace zai wuce amma ta dakaceshi a waya,hakanan suka rabu kowa jiki babu qwari musamman nuradden din. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Cikin satittikan da suka biyo baya suka fara zama watanni shahida tayi dukkan iya yinta don ganin daada ta janye qudirinta,an maidawa koma waye kudinsa da suka amsa amma abun yaci tura,bata taba ganin daadar ta dage kan abun haka ba irin wannan,sannu a hankali taji ta soma tsanar kona waye wannan,da wanne irin abu haka yazo da tashin farko za'a dauketa sukutum da guda a bashi ita?,sannan ta kowanne fanni kowa ya cije yace sai anyi?,hatta da anty zubaida ma yanzu ta soma bin layi,balle ummanta data ga kamar ma tafi kowa murna da farincikinda abun,don ko rannan data je gida bacin rai da baqinciki ya hanata wuni,wai umman har tarin biki take mata,hakanan su mubina har sun fidda anko,ita bata ma sani ba,sai 'yan uwanta 'yammatan dake sa'anninta daketa kiranta kan zasu sayi anko akwai a gida wajen umma?,ko sau daya ta kasa amsa musu saidai taja tsaki ta kashe wayar. Batun ya tsaya mata qwarai a rai,harta lura ta soma ramewa,bacin ranta da har zuwa lokacin wanda ake budurin a kansa bai gabatar da kanshi a gareta ba barema tasan waye,hakan ke nuna ma bata da wani daraja ko muhimmanci a wajensa kenan?. A haka aka shiga azumin ramadana,Allah ya taimaketa batayi sake da kwanakin ba,ta tsawaita ta kuma nace da addu'ar neman mafita wajen ubangiji babu dare ba rana,duk ta zama wata sukuku da ita,sauqinta daya wurin aiki sun bata hutu data tura cewa bata da lafiya,ba zata koma ba har sai bayan sallah,ko daya taqi samun nutsuwa cikin ranta,bacin rai fargaba da qunci da batasan na meye ba gaba daya sun cikata. Da sallah kuwa tana ganin su mubina dasu faruqu suka shirya tafiya katsina tace saisun dawo bata zuwa,ita lallai sai daada ta fuskanci fushi take da ita,daadan dako a jikinta wai an mintsini kakkausa,hakan na sake qona ran shahida,an shiga wata na biyu har ya cimma qarewa a yadda ma taji suna fada biki saura sati biyar amma bata yaba sashi a qwayar idanunta ba?,itakam taga yadda za'ayi wannan abu haka take yawaita fada cikin ranta,saitakejin ma abun kamar wasa,kamar bamai yiwuwa bane,hakan ya sanya ta sake baiwa nuradden qwarin gwiwa da kyautatan zaton lamarin bazai dore ba. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 *_SO DANGIN MUTUWA_* Satu guda cif cif da sallah ranar litinin daada ta buqaci shahidan tazo ranar juma'a mai zuwa,qememe tace bata zuwa ba inda zata,mubina ce 'yar isar da saqon data ji abinda tace bata ce komai ba harta gama wuninta tayi tafiyarta gida. Qarfe tara da rabi na dare suna gama waya da nuradden ta maida wayar chargy ta dawo tana cire hijabin jikinta don taji dadin kwanciya tana son saurarar littafin JARRABI na huguma (littafin da nan gaba kadan zaizo muku a SAUTIN HIKIMA TV dake youtube,idan baki subscribe ba ki hanzarta zuwa kiyi don kar a fara babu ke) ta gyara daurin dankwalinta don tafijin dadin kwanciya,sosai salon labarin ya qayatar da ita shi yasa da an dora sabon shiri a sautin hikima bata missing. Anty zubaida ce ta turo qofar dakin ta shigo itama da hijab har qasa a jikinta,da alama kayan baccine a jikinta "Baki kwanta ba?" "Shirin kwanciyar nake dai,jarrabi nakeson in saurara kafin na kwanta din" murmushi kadan anty zubaida tayi "Kin ganni nima kundin qaddarata nake saurara,ya zamemin jiki kullum saina saurari sabon episode idan sukayi updating" "Na koya miki ko anty?" Shahida ta fada tana dariya "A'ah,ai littafanne idan kika fara saurara baki da zaman lafiya saikinji qarshen kowanne labari" "Gaskiya kam", zama anty zubaida tayi kan kujerar mudubin shahidan " dazu mubina tazo tace miki daada tace kije daga ran talata zuwa juma'a shine kika ce ba zakije ba?"yanayin fuskar shahida yadan sauya,sam ita yanzu ko zancan katsjna ma bataso ayi mata "Anty to me zanje nayi mata kuma?,bayan ta gama tsara duk yadda ranta yakeso?" "Amma bai kyautu ta kiraki kiqi zuwa bako?,tunda kinsan cewa koma meye daada ba maqiyiyarki bace masoyiyarki ce,kome zata yi zatayishi ne sabida tana sinki ba don ki cutu ba" shuru sukayi gaba daya,anty zubaidan na karantar shahida,yayin da shahidan ta shiga tunanin me zata je ta yiwa daada?,amma tana ganin kuma wannan kamar wata dama ce da zata kaimata nuradden ya gwada sa'arshi ko Allah zaisa haqarsa ya cimma ruwa,kai ta kada "Shikenan,zanje ran alhamis" "Yauwa,dadai yafi" ta fadi tana miqewa "Anty don Allah idan kin fita ki cewa faruqu yayimin transfer din data,data din nan satinta daya da ita nakejin littafin,donma ba cirar data din ake ba ai da tuni ta qare" "Yana falon uncle,zan masa magana" ta amsa mata tana fita a dakin. _kuyi manage da wannan_ https://youtu.be/_XVqJSBXVPI *Alqawarin Allah* 2️⃣9️⃣ Da hanzari ta koma jikin wayarta ta cirota,ta koma gefan gado ta rubuta saqo ta tura masa,saita kashe wayar don ta tabbatar ta barta akunne nuradden bazai barta tayi barci ba,tunda damar da yake nema kenan gashi ya samu. Washegari tana kunna wayartata kuwa kiransa ne abu na farko daya soma shigowa,yadda taji muryarshi ya kasa zaune ya kasa tsaye kaman ance masa an bashi ita dinne,tun a ranar suka shirya yadda tafiyar zata kaya,ya nemi su tafi tare tace sam,ya sameta kawai a can ran alhamis din,murmushi ya saka mai sauti "Bakison hawa motata kwata kwata shahida,don know why....koda yake babu komai saura qiris in sha Allahu,Allah yakai damo ga harawa dai" murmushi kawai ta saki tana yanke kiran,bazai gane bane,baisan irin illa tabo da masifar da shiga

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});