Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 11

Chapter 11

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,308 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya sanyashi kada kanshi yana ci gaba da jifanta da murmushi "Eh zuciyarki nakeso" cikin mintina qalilan kwanyarta ta hakaito mata abinda yake nufi,wata iriyar kunya da nauyi suka kamata,ta rasa tudun dafaww,saboda haka saita juya gudu gudu sauri sauri ta shige gida,yana tsaya mana amma ina ba zata iya ba,bata taba zaton a shekarunta sha biyar akwai saurayin da zai gaya mata wai yana sonta ba,kalmar tayi mata nauyi da yawa. Murmushin jin dadi ya saki,ya zauna dakalin dake daura da gidansu,abinka da d'an makaranta ba'a rabashi da takarda,sai ya ciro qaramar jotter din dake aljihun wandonshi wanda ya gama duba wani karatu da ita yayi rubutu da basu wuce layi goma ba ya jefa cikin botikin,ya kira yaro ya bashi botikin shi kuma ya wuce. *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *KO KUMA* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARINGπŸ™πŸ½* πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½ https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *KO KUMA* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARINGπŸ™πŸ½* πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½ https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos *Alqawarin Allah* 0️⃣7️⃣ Saida umma ta dinga qwala mata kira kan ta fito ta wanke kwanukan ta dauki abincinta taci kada lokacin islamiyya ya wuce sannan ta taso daga rub da cikin da tayi saman katifarta,ta harhada kwanukan ta kada ruwan kumfa ta soma sabesu,tanayi tana tunanin kalmar daya furta mata,ashe kalma ce mai nauyu da dadi haka,lokaci lokaci ta dinga sakin murmushi ita daya,harta zubawa botikin ruwa ta zubda ruwan sai taga takardar,ta tsame hannunta cikin kumfar ta dauki takardar sannan ta bude. Soma fahimta da tayi takardar meye yasa tayi sauri ta shige dakinta,ta samu kebantaccen waje ta budeta inda zata sha iska ta bushe sosai sannan ta dawo taci gaba da wanke wankenta. Kafin ta kammala shirin islamiyyarta saiga qawarta zunnurah ta iso cikin unifoarm din islamiyya "Yauwa,dama banason cin abincin nan ni kadai,don Allah bari na dauko ki tayani" cewar shahida tana nufar kitchen ta fito da kwanon abincinta ta aje a qasa ta zauna dirshan "Sauko malama muci" "Ke nifa a qoshe nake wallahi ba abincin da zan iya ci" "Ni zakima wulaqanci ko?,zaki sake cewa naci abinci a gidanku" tq fada tana saka hannu tayi bismillah ta soma ci zunnurah na mata dariya,wai ita zata cewa tana cin abincin gidansu,matar da nata abincin ma sai ya huce bata ci ba,hira suke jifa jifa shahida nacin abincin tana kuma duba lokaci kada a fito saga sallah a shiga aji basu tafi ba,saidai rabi da rabin hankalinta nakan takardarta dake shan iska "Yauwa shahida....wai waye wanda yake rakoki ne kullum daga wajen sadaka" tsaida lomar da zata saka a bakinta tayi tana duban zunnuran "Au har kin samu labari kema?" Harara ta watsa mata "Uwar labari na samu,waye baya ganinku a tare wai kwana hudu kenan,tunda ansan baki kula kowa...." "K'nnnn...nima ban sanshi ba wallahi zunnurah,acan nake ganinsa" dariya zunnurah ta saki "Qawata nasan halinki sarai,duk yadda akai wannan din na dabanne tunda har kika kasa gwada masa halinki" murmushi ta saka,ita kanta tasan na daban dinne nasai zunnurah ta fada ba,tun kallon farko taji yakai mata ko ina,ganin farko taji wani qaqqarfan lamari dangane dashi,takan iya raba dare tana tunaninsa,kowanne second nata da tunaninsa take rayuwa "Amma fa kinsan shaik hafiz zai shiga wani hali?" Dagowa tayi tana duban zunnurah kafin ta galla mata harara "Kamar yaya?,sonshi nake?,ko ce miki yayi yana sona" nan ta zauna tsaf ta kwashe mata yadda dukkan dalibai suka lura da soyayyar da yake mata,baki ta tabe tana miqewa daga gaban kwanon,don ita dai tasan ko doguwar magana bata hadata dashi bare kuma wani abu daban can,fita tayi ta wanke hannunta ta dawo tana ware gogaggen hijabinta "Qawata baki da mutunci fa,shaik ke kanki kinsan yammatan makaranta rububinsa suke,kuma kema kanki qaryarki kice baki san yana sonki ba,maimakon kiyi murna sainaga ke ko a jikinki labarin bai faranta miki ba ko d'aya" "Don Allah zunnurah ki qyaleni da zancansa,sai....." Maganar tata ta katse jin sallamar fiddausi,yarinyar da tsakanin gidansu shahida da nasu gidan layi biyu ne,tun zuwanta islamiyyarsu shahida takeson qawance da ita,tun shahidan na janyewa harta saki jiki da ita,saboda ta lura yarinyar itama nada hankali,yawan shuru shuru da rashin son hayaniya. Tuni zunnurah ta hade rai,hakanan a duniya taji sam fiddausi bata yi mata ba,ko kadan jininsu ya kasa haduwa,shahida ta rasa dalili,tun tana sharewa har tazo tanawa zunnurah fadan ta daina haka,wulaqanta dan adam babu kyau,yarinyar na sonsu hakanan bata da wata matsala meye abun sha mata qamshi da take "Hakanan wallahi nidai naji batayimin ba" amsar da zunnurah ta baiwa shahida kenan. A tsakar gida fiddausi ta duqa ta gaida umma cikin ladabi,ta amsa ba tare data tsaya ta mata wani cikakken kallo ba taci gaba da sabgoginta(babban kuskure na biyu da ummanta ta sake tafkawa bayan fada da miji gaban 'ya'ya),fiddausi ta shige dakin shahida,cikin fara'a suka gaisa ita da shahida,yayin da xunnurah ta kauda kai ta amsawa fiddausin sama sama,dif zunnurah tayi sai shahidan da fiddausi dake hira sama sama,har shahida ta gama shiryawa suka fice daga gidan. Suna gab da shiga gate din makarantar xunnurah ta kamo hannun shahida tayi baya da ita,duk sai suka tsaya ta hade gira tace da fiddausi "Me kike jira?,magana zamuyi da ita" sum sum fiddausi ta juya ta wuce ciki "Wai me yasa kikeson koyon halin daba naki ba zunnurah me fiddausi tayi miki?" "Shahida,ba haka kawai naji banson yarinyar nan ba,an bani labari fiddausi tana taba shaye shaye..." Rufe bakinta shahida tayi da hannu tana kallon zunnurah gami da zaro ido "Haba zunnurah,haba,zato fa ance zunubi ne,ya zaki jefeta da wannan mummunan kalmar don kawai tana son mu'amala damu?" "Da gaske nake miki shahida,daga bakin namiji na samu wannan labarin,kinsan kuwa su basu fiye munafunci kosa ido ba bare kice,sannan kuma idan zaki lura da kyau zaki ga yanayin fiddausi ba irin namu bane,yawan bacci da kasala kawai alamune na mutum yana taba shaye shaye,zaman kadaici rashin so magana da yawa" zame hannunta shahida tayi daga na zunnurah,don sosai taji babu dadi ta kuma ji ranta ya baci "Duk abinda kika fada zunnurah baki da tabbaci a kanshi,karki fadi abinda zaki jawo a tsaidaki a miki hisabi ran gobe qiyama,ni fiddausi ta gayamin bata da cikakkiyar lafiya,tana da sicklier shi yasa take yawan bacci" kada kai zunnurah tayi "Shikenan shahida tunda baki yadda dani ba,kinfi kowa amma sanin halina,nidai ina baki shawara kibi a hankali,don bazanso abinda zai cutar dake ba" "Babu abinda zai faru in sha Allahu" daga wannan suka rankaya suka shige cikin makarantar. Washegari da wuri taje wajen bada sadaka ba kamar yadda ta saba zuwa ba,hakanan takejin wani nauyi da kunya tunda ta karanta kalaman da yarubuta mata jikin takarda,niyyarta tayi da wuri ta koma gida ba tare daya sameta ba,saidai abinda bata sani ba tuni ya rugata ma zuwa,saboda gaba daya ya rasa nutsuwarshi Allah Allah yake gari ya waye yamma tayi yaje ya ganta,bai taba tsintar kansa cikin irin wannan

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});