Chapter 34
Chapter 34
Allah ki shuru" ajiyar zuciya dukkansu suka sauke wanda su kansu basu san ta fito sarari ba saida suka hada ido da juna suka tabbatar anwar din yaji sai kuma sukaji kunya,hakan shi ya tabbatarwa da anwar suma zancan na ransu,basason tararsa ko tauyeshi ko tilastashi kan abinda bashi da niyya ko ra'ayi. Wannan abun daya faru sai ya zama kamar wani lasisi nafisa ta samu na nuwa anwar soyayya ko a gaban waye,wanda hakan ya sanya babu shiri ya qara qaimi wajen gyaran gidansa,don yana ganin matyqar yaci gaba da zama a gidansu akwai matsala,don nafisan kaman ta soma fitsare sawayenta,duk da yadda hajiya bilkisu ke taka mata burki amma sam bataji,hudubar mima gani take itace dai dai don itace dai dai da ra'ayinta. Ta dage sosai wajen farauto zuciyarsa,da yake Allah shike sanya soyayya cikin zukatan bayinsa duk irin kulawa da kyautatawar da take masa bai taba jin wani abu mai kama da qaunarta ba cikin zuciyarsa,yana mata kallon qanwa tana kuma da qima a idanunsa darajar mahaifanta da yadda suke sonshi. Shekara biyu cur rayuwar anwar ta sauya,kai baka ce shine wannan anwar din ba,kamanni yanayin rayuwa da komai nashi,saida zuciyar nan na nan,zuciyar dai itace babu wani abu daya sauyata,a sannan alhj abba ya shirya bikin yaye wasu daga ma'aikatansa wanda su suka buqaci haka don suci gashin kansu,ciki harda anwar wanda tun dacan dama bai sha'awar zama qarqashin wani,yafison duk wahala yaci gashin kansa,a lokacin da alhj abba ya yayesu ya danqawa kowanne kudin sallama,saidai kudin anwar yafi na kowa yawa,ya zauna da alhj abban ya gaya masa zai amsa ya qara cikin kudadensa,amma in sha Allahu zai dawo da dukka kudin da aka bashi,aljh abba yace sam wannan kudin kyautane kawai saboda bauta da wahalar da suka yiwa kamfani, a nutse anwar ya fahimtar dashi manufarsa,shidai yace yaje kawai ya kafa kanshi din. Komai na rayuwa wato yana da lokacinsa,hakanan rabon kwado bai hawa sama,anwar ya tsaya tsayin daka,babu dare ba rana,babu lokacin bacci bana hutu sai daya tabbatar ya kafu,ya fidda kudin alhj abba ya maida masa,shi kansa alhj abban yayi mamakin yadda anwar din yayi kafuwar da aqalla kayi shekara goma sha bakayi irinta ba,saidai yasan komai yassarewace ta ubangiji,shi kansa anwar yasan cewa qarfin addu'ar iyaye tsayawa kai da fata kan gaskiya da riqe Allah da yayi shi ya kaishi fa wannan matakin,tuni ya tamfatsawa anty usaina gida,saidai a sanda yace ta zabi unguwa saita zabi unguwarsu shahida,farkon layinsu wasu gidaje da suka tashi suka saida,daya tambayeta dalili tace ba ruwansa,ba yadda ya iya haka yayi mata yadda tace tana so,saidai har aka kammala ginin bai taba taka qafarshi unguwar ba,data koma kuma sai zuwan ya zame masa dan zani shima,sai daya sanya aka sake fasa qofa ta bayan layinsu yake shiga ta nan. Ganin lokaci yana ja anwar yaqi soma maganar aurensu babban burin daya rage mata a duniya yasa ta soma masa shagube,qwarai ya fahimta saidai har yanzu baiji nutsuwar zama da nafisa a matsayin matar aurensa ba,duk da ya sani tunda ya furta dole ya cika amma har yanzu zuciyarsa taqi karban hakan,abinda yaketa yaqi akai kenan,ita kuma tasan cewa iyayenta ba zasu taba yi masa batun ba,mutum daya ce nan duniya zata ce yayi ya zame masa dole yayi anty husaina,dalili kenan da yasa ta wanki qafa bisa shawarar mima taje mata da batun,wanda a yanzu haka akan qadamin da suke kai kenan yanzu haka(idan baku manta ba a baya kunji inda anty usainan ke masa maganar kar suji kunya kan nafisan). Ta bangaren shahida ma kwanaki watanni zuwa shekaru sun soma tafiya,tuni ta kammala degree dinta wanda ta samu gamasu da qananun shekarun da kowa ya kalleta sai yayi mamaki,hakanan ta dora da masters shima Allah ya taimaketa ta kammalashi cike da nasara mai tarin yawa,a sanda sakamakonta ya fito uncle hisham yaso ta amshi tayin lacturing da jami'o'i suka yi mata tace sam bata ra'ayi,ya tura takardunta kamfanoni da dama ta samu aiki daga wajensu nanma tace ba zatayi ba ciki harda kamfaninsu,ba yadda ya iya hakanan ya qyaleta. Sanda tazo masa da zancan koyarwa a *NOOR INTERNATIONAL* sai daya cire gilashinsa ya kalleta don ya tabbatar da wasa take koda gaske,hakanan taji kawai bata da burin daya wuce itama yaran talaka su amfana da karatu ilimi da baiwar da Allah ya bata,ba haka yaso ba sam,saboda tayi karatu kai kyai wanda ya dace ta tsaya ta moreshi tayi amfani dashi ta hanyar yin aiki a gurbi da kuma bigiren daya dace,hanatayi kai tsaye yace maida kai baya ne,ta nace ta dage wansa ya sanyashi dole ya amince,amma bisa wasu sharudan. Duk sanda suka mata wani abu da bai gamsheshi ba to ba shakka ta gama koyarwa a makatantar,kai tsaye ta amince don bata ga ma abinda zai gamota dasu ba bare wani abun ya faru,kan wannan sharadin ta soma koyarwa cikin makarantar,ta kuma samu karbuwa daga wajen dalibai har malamai,zama cikin makarantar kuma yayi mata,hakanan yana mata dadi qwarai. Wannan shine labarin taurarinmu guda biyu da abinda ya zama sanadiyyar rabuwarsu ba tare dakowannensu yasan cewa MAQARQASHIYA CE ba. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Zaman bitar rayuwarsu ita da anwar din data tsaya yi daren jiya ba qaramin taba zuciya ruhi da kuma gangar jikinta yayi ba,tayi kuka irin wanda ta jima ta jefashi kwandon shara tare da yiwa kanta alqawarin ta daina har abada,dalilin daya sanyata makara kenan bata kwanta da wuri ba,hakan ya sanyata bata tashi farkawa ba sai qarfe bakwai na safe,ko sallar asuba ta qwace mata kenan,cikin hanzari ta sauko daga saman gadonta duk da yadda jikinta yake a matuqar mace,hakanan ya mata nauyi tun daga gangar jikinta zuwa kanta. Tana idar da sallar da ake binta tana cikin yin azkar dinta na safiya huda tayi knocking ta turo qofar,ta shirya tsaf cikin wankakku kuma gogaggun unifoarm dinta,kai kace yau ne zata soma zuwa makarantar,fuskarta qunshe fal da walwala da farinciki,saidai tana ganin alamun shahidan bata shirya ba ta turo baki kaman zatayi kuka "Anty...bakishirya ba,yaune fa?" Murmushi ta saki tana qarashe salatin annbi guda goma da takeyi ta shafa sannan tace "Banajin dadine yau huda" "Amman zaki ko?" Ta tambayeta da sauri cikin fargabar kada tace ba zata samu zuwan ba "Zanje huda...amma inajin zamu makara da yawa fa" qafa ta soma bubbugawa shahidan ta gane me take nufi "Kinga...ki shirya a soma kaiki,idan yaso in ya dawo daga kaiki ni saiya kaini,saimu hadu a hall din hakan yayi?" Kaita kada tana murmushi "Bari naje naci abinci to" ta fadi tana juyawa a guje ta fita a dakin,sai data bacewa ganinta sannan ta dauke kanta tana sauke nannauyar ajiyar zuciya,tanajin inama ace itace hudan,quruciya abu ne mai dadi,baka da matsala baka da damuwa,dukka ka tsere musu. A nutse ta cire kayanta ta shige bandaki ta tara ruwan dumi ta soma wanka,saboda yanayin jikin nata da batajin dadinsa yasa komai nata ma cikin nawaa take yinsa,hakan ya sanya ta kashe kusan awa guda a wanka da shiryawa. Ta jima gaban mudubi tana kallon fuskarta kaman yadda ta saba koda yaushe,dukda idanunta sun dan sauya saboda kukan da tayi daren jiya amma sai taga fuskarta tayi wasai,farar affaya mai taushi data nade jikinta ta amsheta qwarai,akwai adon golden jikinta,hakanan taji kaman ta cireta,me yasa ma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96