Chapter 29
Chapter 29
fita shahida!. Ki fita nace!" Kai ta kada cikin tashin hankali tanason taji qarshen zancan daya dauko,daga sanda ya ganta me?,ya ganta ne sanda suka tafi siyan syrup?,koko yana tsaye sanda matashin saurayin ya fiddo ta daga motar? "Ba inda zani...kome zaka yimin ba inda zani" bata ankara ba taji ya damqi hannunta,karon farko a tarihin rayuwarsu,bai barta ba saida sukaje soron qarshe bakin qofar gidan sannan ya turata wanda hakan yayi sanadiyyar da tayi taga taga ta kusa faduwa Allah yasa ta turje "Bana sonki shahida" kalmar data hadu da qarar rufe qofar gidan garam da yayi ta bada wata tsawa tsakiyar kanta data sanya komai nata ya tsaya cak na wucin gadi,da taimakon ambaton sunan Allah data soma yi ne ta samu nutsuwarta ta dawo. A hankali ta dinga takawa kamar wadda tasha wani abun,kalaman anwar suka soma amsa kuwwa cikin kunnuwanta,wani irin bushewar zuciya taji,dukkan wani tashin hankali ta nemeshi ta rasa,ba abinda takeji sai kalaman anwar a kunneta,bata ankara ba taji ana "Subhanallahi....sannu...amma bakiji ciwo ba ko?" Sai a sannan ta daga kanta tana duban mutanen dake magana kamar wata doluwa,ashe qatuwar kwalbatin da ake haqawa unguwar ta fada,da qyar da taimakon wasu 'yammata da sukazo wucewa ta samu ta fito sunata mata sannu,taci gaba datakawa ba tare data tsaya duba ciwon data ji ba,burinta kawai ta isa gida,burinta Allah yasa ace mafarki take. Bata tabbatar da cewa komai da gaske yake faruwa ba saida dare ya tsala,taji idanunta tarwai kaman yanzu ta tashi daga baccin wata uku,siya zuciyarta ta dinga yi irin wanda bata tajin irinsa ba,cikin qaramin lokaci qirjinta ya soma ciwo,numfashinta ya dinga fita da qyar,haka ta tsinci kanta har asuba ta risketa,sanda ummanta ke yunqurin tadata tayi sallah a lokacin taga halin da take ciki,basuyi wata wata ba suka wuce da ita asibiti. Gwajin farko likitan yaga jininta yayi mugun hawa,don dab yake da yakai dari biyu,dole suka soma mata allurar bacci kafin sauran treatment su biyo baya,ba qaramin tashin hankali abba da umman suka shiga ba,don duk ga zatonsu iya halin da suka tsundumata ne kawai yayi sanadiyyar faruwar haka,duk da cewa shi dinma ya taka tashi muhimmiyar rawar. Daga bangaren anwar tunda ya maida qofar gidan ya rufe da qyar ya kaishi daki ya zube saman kujerar falon qwalqwalwarsa na daukan zafi,yana maijin ciwo da zafin dukkan wani abu daya faru tun daga kwanaki uku da suka wuce kawo yau,ji yake kaman ya budi idanun yaga mafarki yake,yana jin bugu wanda yasan bazai wuce muhsin ba amma bazai iya tashi ba,bashi da sha'awar ma kowa ya rabeshi,daga bisani wayarshi ta dauki qara,ya qura mata idanu yana kallonta hartayi ta gana ta tsinke,sannan ya miqa hannunshi ya daukota,ba tare daya damu da duba mai kiran ba ya bude bayan wayar ya ciro layin wayar ya karyashi ya watsa tsakar gida sannan ya cilla wayar da batiranta gefe guda,a ranar yadda yaga rana haka yaga dare,dukkan laifukan kuma na wuyan shahida ita ta haifar da komai,haka ya dinga sintiri yana zarya,gaba daya duniyar jinta yake sama ta koma qasa. Da qyar da sudin goshi ya samu bacci yayi awon gaba dashi. Cikin watanni qalilan yaji gaba daya rayuwar ta juya masa baya,baya jin dadin komai,komai ya daina burgeshi,komai kuma ya tsaya masa cak,duk yadda yayi qoqarin moving forward ga aje komai hakan ya gagareshi,dalili na farko da yasa ya tattara dukkan abunda ya danganci shahida wanda idan ya ganshi zai iya tuna mishi da ita ya killace a muhalli daya,duk yadda yaso ga qonasu ko zubarwa hakanan ya kasa,abu na biyu ya aje aikin kamfanin da yake,domin kuwa duk sanda zai tafin saiya tuna mishi da ita,abinda sam ko kusa ko alama baida buqatarsa. Ta bangaren shahida kuwa sanda ta farka kalamansa ne abu na farko da suka soma dawo mata aka,ji ta dinga yi kaman zatayi hauka,ta ina zata iya rayuwar da babu anwar,yadda ta koma din ya sake daga hankalin abba da umma,yayin da tarin damuwa da nadamar abinda suka aikata ya sanya ciwo ya shigi abban,ya dinga fama dashi shi kadai yana cinsa kadan kadan. Abubuwa sai suka taru suka yiwa umman yawa,ga shahida har yau bata gane kanta,ga abbansu ciwo nason kayar dashi,sannu sannu lamuran suka ci gaba da kwabe mata da tafi mata a haka,har zuwa rana mafi muni da tashin hankali a garesu,ranar da ciwo ya yiwa abbansu shahidan farat daya aka tadda gawarsa cikin daki,fadin irin tashin hankalin da suka tsinci kansu ma bata baki ne,shahida kam tunda ta suma bata farfado ba sai datayi kwana biyar,wata iriyar dakiya ta dinga shiganta,ta yadda tabbas wani tashin hankalin baida misali,yadda take jin kanta da rayuwarta ta zama wata mara gane komai,zaqi ko d'aci,baqinciki ko farinciki,murmushi ko kuka,ta koma kamar mutum mutumi,tana jin tamkar ita ta kashe mahaifinta,tana jin alhakin mutuwarsa na bisa wuyanta,abinda ta aikata ba shakka shi ya kashe mata mahaifi,awannan halin anty zubaida ta cimmasu,don dukkan abinda ya farun ya faru ne basa qasar ita da uncle hisham. Kuka umma ta zauna tayi sosai a gabanta,tana fatan ta samu wasu shawarwarin da zasu kawo silar warwarewar matsalarta,bata boyewa anty zubaidan komai ba,labarin dukkan abinda ya biyo bayan yayi masifar girgizata,tana qaunat shahida har cikin ranta,tasan kuma Allah ne ya sallada wannan qaunar a tsakaninsu "Ba shakka kun tafka kura kurai arayuwarku duk da cewa shi tashi ta riga data wuce kaman yadda kika shaidan yabar wasiyyar neman afuwa a gareku gaba daya saidai muyita masa addu'ar samun dacewa,cece kuce ko fada gaban 'ya'ya babu abinda baya haifarwa ku kunga irin naku sakamakon dayazo dashi,daga ciki yana haifar da qiyayyar uwa kota uba,saboda kan yara zai rarrabu,kowa da wanda yake goyawa baya,daga haka zakiga an samu jam'iyyu daban daban,wanda kowanne yaja tinga ne yana taya gwaninsa nashi fadan,walau yana taya uwa ko uba,wannan sai yasa hatta a tsakaninsu 'yan uwan junan ma basa jituwa saboda wani baya ra'ayin bangaren da wani yake,bugu da qari idan da namiji gareku kai uba kana koya mishi ko ya tara iyali haka zai mu'amalanci iyalinsa?,ke uwa kuma kin koyawa diyarki haka akewa miji,illoli ne masu tarin yawa da qalubake kala daban daban,yanzun kunyi silar jefa diyarku ga tafarkin shaye shaye sabida tashin hankalin da take shiga sanda kuke yaqar juna harta gwammace ta zama ko yaushe out of sense yadda ba zatasan meke faruwa cikin ahalinta ba..."dan shuru anty zubaida tayi abun na mata ciwo "Yanzu bazanyi kaffara ba cewa kun korarwa diyarku manemi...saboda halin data fada ya isa kunnenshi...wala'alla abaya yana mata kallon managarciya yanzu ya sameta kan wannan turbar,kowanne namiji burinsa shine zabawa yaransa uwa ta gari kun bata wannan kyakkyawar shaidar daga kan shahida...inajin ciwo...inajin ciwon abinda ya samu shahida...amma nayi alqawari bazan bar rayuwarta ta gurgunta ba" daga haka ta miqe zuwa dakin shahida cikin bacin rai amma kafin ta shiga sai tayi qoqarin dai daita yanayinta sannan ta daga labulen a hankali ta saka kai cikin dakin da babu kowa ciki sai shahidan qwal ita kadai.*Zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani don GIRMAN ALLAH karki sharing,ga mai buqata ki tuntubi wannan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos *Alqawarin Allah* 1️⃣6️⃣ Daga kai tayi ta dubi anty zubaidan maimakon yadda ta saba yi mata a baya duk sanda ta ganta,takan tashu cikin farinciki tana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96