Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 65

Chapter 65

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,300 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta sake umman tana dubanta sannan tace "Saikace qanqanuwar yarinya zaki tasani gaba kina kuka?,meye hakan?" Zamowa tayi daga saman kujerar da take kai tayin kneeldown a gaban umman ta kama hannayenta "Don girman Allah umma ki dakatar dasu,ke daya ce burina na qarshe,wallahi umma bana sonshi shima baya sona,ku aura min koma waye umma amma banda anwar?" Idanu ta saka tana kallonta,a iya saninta abinda ya faru tsakaninta da anwar ma laifi nata ne,iya abinda ta saninma baiyi zafin da zata rikice hakan ba harta rasa sukuni da walwala ba,Yayin da khadija wadda shigowarta kenan ta tsinci xancan ta dafe baki gami da zare ido cikin mamaki,har batasan sanda tayi subutar bakin cewa "Yaaya?,ya anwar ne fa?" Daga kai umma tayi tayi mata nuni data fice,haka ta fita cikin dimbin mamaki,ta zaci antyn tata zatayi farinciki da dawowar anwar rayuwarsu fiye da yadda su sukayi,amma ga sabanin hankalinta sai taga ba haka bane sam. A nutse umma ta zuba mata idanu,cikin sanyin murya wanda ke nuna har jikinta ma a sanyaye yake tace "Ashe so kike ki tona mana asiri shahida bayan lullubin sutura da Allah yayi mana?" Ta qarasa maganar wani abu na taba zuciyarta wanda ya bayyana har a muryarta "Shahida ashe baki qaunata?,ashe ba rufin asiri Allah yayi miki ba damu kanmu daya dawo miki da anwar?,meye a zuciyarki shahida?,bakison farincikina ashe da walwalata?"kai shahida ke girgizawa kuka na qwace mata "ba haka bane umma,umma bana sonshi kiyi haquri umma,wallahi banajin sonshi kwata kwata" "Shahida indai nice na haifeki ina....." "A'ah,karki qarasa don Allah umma" sukaji wata murya da sako kanta kenan dakin ta tsinci zancan shahida na qarshe da lafazin umman ta fada,dukkansu suka juya suna kallonta,anty usaina ce,ta qarso inda suke zaune,wajen shahida ta nufa kai tsaye ta kama hannayenta sannan ta zauna gab da ita,hankalin umma yadan tashi kadan don ba zataso shahida tacigaba da magana kan anwar ba,don tana da tabbacin batasan wace ita a wajenshi ba "Idan kika fadi haka kamar kin mata qarfa qarfa ne ai" tana kallon umman tayi maganar,wani sanyi shahida taji cikin ranta,tana fatan Allah yasa zuwan matar ya zame mata haske "Idan kuma tana da hujjarta fa wadda tafi taku qarfi?,ki barta aji hujjarta da dalilanta tukunna". Miqewa umma tayi " bata da wata hujja ko dalili usaina" "A'ah bari naji ta bakinta tukunna" "Koda kinji ta bakinta na riga na yanke matuqar nina haifeta ina bata umarnin auren anwar" daga haka umma ta fice daga dakin tana mamakin wauta da sakarcin da shahidan takeson tafkawa,kamar batasan meya wakana cikin rayuwarta a baya ba,bata taba tsammanin ma anwar zai sake waiwayar shahida yace zai aureta ba sabida abunda idanunshi suka gane masa a zahiri ba labarj,dama tazo mata tanason tayi wasa da ita?,koda taqi anwar din batajin zata samu kamar anwar din,mutumin da tun wancan lokacin ya samu karbuwa cikin kaf danginta na uwa da uba,badon komai ba sai kyawun halayyarsa da kyawawan dabi'un da Allah ya huwace masa. Maido dubanta kan shahida tayi bayan ficewar umma,suka hada idanu,hakanan shahidan taji gabanta ya fadi,ta dauke nata idanun tana matsar qwalla,cikin taushin murya ba tare data saki hannunta ba tace "Shahida....inason naji meye matsalarki dashi wannan din da umma tace saikin aura,indai naji dalilanki masu qarfi ne nayi alqawarin tsaya miki harsai an warware komai" shuru na 'yan sakanni ya ratsa tsakaninsu,batajin zata iya furtawa wani komai,yin hakan kamar ta dabawa cikinta wuqane,tana ji ceqa wani sirri ne agareta ga duk wanda baisan meye faru ba,a hankali ta motsa labbanta sannan tace "Kawai bana sonshi,shima kuma baya sona,hasalima mun rabu dashi a qalla shekara shida kenan,ba wanda keda muradin wani" shuru anty usaina tayi tana nazarin kalamanta,ba shakka akwai wani abu,amma dukkansu amsa kusan guda ce,jiya jiya ta titsiye anwar din kan meye sanadin rabuwarsu da shahida amma ya kasa bata amsa daya qwaqwqwara,kowannensu bayason fallasa asirin dan uwanshi,hakan na nufin akwai ragowar wani abu da yayi saura game da zukatansu qarqashin zukatansu kenan koda su basusan da hakan ba? "Amma shahida....ya akayi kikasan baya sonki?,kuma dama an taba rabuwa hakanan babu wani dalili?"tambayar taso kaita maqura saboda rashin amsa "Miji da mata ma kan iya rabuwa haka kawai ya saketa badon ta masa komai ba,saidon qarewar wa'adin zamansu da Allah ya qaddara musu" saitayi shuru tana hadiyar zuciya tana neman amsa ta biyu da zata bata wadda zata gamsar da ita,da qyar ta iya hada abun fadi bayan anty usainan tace "Uhmmm,ya akayi kikasan baya sonki?" "Duk wani abu na nuna kulawa ko xiyara da zai nuna saurayi yana son budurwa babu shi tattare dashi,sau daya ya taba zuwa wajena,shima bamuyi ganawar dadi dashi ba,ta yaya zance yana sona?" Ta qarasa maganar badon abinda ta fada ya dameta koya dadata da qasa ba,a'ah,ta fada ne kawai donta riqeshi hujjar da anty usaina zata taimaka mata ta rana wannan auren da take kallonsa a matsayin qarfen qafa mai wuyar kwantuwa a gareta. Lallai ya zama dole ta shiga alaqar shahida da anwar,tana fata nan gaba dukkansu suyi dariya,tana fatan ko meye silar shiga tsakaninsu nan gaba ya zama tarihi,rayuwarsu ta koma kamar yadda take a baya "Naji dadi da kika kasance yarinya mai biyayya wa iyayenta,ina mai miki kyakkyawan fatan ba zaki toxarta ba in sha Allahu,biyayyarki zata kai miki da ixinin ubangiji" da wannan kalaman sukayi sallama,ta fice daga gidan bayan ta samu umma ta roqeta kan karta gaya mata dangantakarta da anwar,donta tabbatar hakan zai baiwa shahidan kunya. Tun a kan hanya ta soma gwada number anwar din,saidai bata sami wayarshi ba akashe take,da alama yana muhimmin wani abune,dole ta katse kiran ta isa gida,saidai lokaci lokaci tana gwada number tashi ko xata dace ta shiga. Tana idar da sallar magariba ta soma shirin barin gidan,umma ta dubeta "Amma da kin dan jinkirta tafiyar tukunna,saboda garin a dinke yake da hadari ga iska ta soma kadawa" "Idan ya sauko bansan ranar da zai dauke ba,anty zubaida kuma zataji shurun yayi yawa,don ban gaya mata ma ina nan ba" "Shikenan,Allah yayi miki albarka,yasa albarka a rayuwarku" "Ameen" ta amsa tana maida qwallar dakeson fitowa,haka ta baro gidan tana tafiya kamar wadda batason taka qasa,wanda bai sani ba sai ya zaci salo ne ko tana sane,amma ba komai bane sai tsabar damuwa dake cinta a rai,tana jin yadda hadarin ya taso sosai sanda takai tsakiyar layin nasu,iska ta dinga kadawa tana ratsa jikinta,saidai sam bata damu ba,bata damu da ruwan ya sauko ya daketa ba,hakanan bata damu data koma gida donta samu mafaka ba. Daidai lokacin da motarsa ke tsaye qofar gidan anty usaina wadda ta buqaci ganinsa a yau basai gobe ba,yana zaune cikin motar baikai ga yiwa mai gadi horn ba bare ya bude masa,ya tsaya ne amsa waya,dukka gilasansa a rufe suke ruf kamar yadda al'adarsa take yawanci idan yana cikin mota,bugu da qari kuma ma sabida iskar dayaga ta taso sosai,wanda yasan ba za'a rasa qura ba cikinta,gefansa ya kalla kamar wanda aka fisgi hankalinsa,sai yaga kaman itace ta wuce,yaci gaba da amsa wayar yana kallon bayanta,tabbas ita dince,amma me take har war haka duhun magariba ya mamaye gari bata koma gida ba,idanunsa suka ci gaba da kallonta har lokacin data dan bada tazara daga inda yake,yana shirin janye idanunsa yaga yayyafi ya

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});