Chapter 8
Chapter 8
kai kaman bata jishi ba,murmushi mai sanyi shahida ta saki ta juya tana ci gaba da tafiya "Allah ya dawo dasu lafiya" "Amin" ya amsa,huda kam ta kasa zaune ta kasa tsaye,yayun nata kamar qawaye suke a wajenta,ita daya ce mace banda zuwan shahida gidan itama idan suka koma makarantar ita kadai ke watangaririya a gidan,saidai idan ta gaji ta gudu gidan kakanninta na wajen uwa. πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ A nutse yake kai abincin bakinsa,yayin da rabin hankalinsa ke kan wayarsa dake aje gefan plate dim abincin,zaune take kan kujerar dake fuskantar tasa,tasha kwalliya iyaka,kai kace zata je wajen wata dinner dinne,cikin dinkin lace riga da skert take,hannayenta gaba daya biyun ta tallafe kumatunta dasu,yayin data zuba masa idanunta,duk wani wani motsinsa yana yinsa ne kan idanunta,batasan wanne kalarso take masa ba arayuwa,saidai koma meye tasan cewa son da take masa wani bangarene mai girma a rayuwarta. Kanshi ya daga daga wayar yana sake kai wani spoon din abincin bakinsa,sai a sannan ya lura da irin kallon da take masa "Hey!" Ya fada yana murza yatsunsa,hannayen ta sauke tana dan qaramin murmushi bayan ta sauke ajiyar zuciya "Kallon fa?" Ya tambayeta a taqaice,muryarta cikin rauni da nuna fargaba wanda ya wanzu har saman fuskarta tace "Ina tsoron kar na rasaka anwar,ina jin kamar watan watarana zan rasaka" ta fada can qasan ranta tana jin kishinta na cin zuciyarta,tana jin kamar zata dawo rayuwarshi ta rabasu,ta san cewa a yanzu sun yiwa rayuwar juna nisa saidai ta kasa samun nutsuwa da kwanciyar hankali duk da haqarta ta cimma ruwa,aje cup din da yayi niyyar kaiwa bakinsa yayi,ya hade hannayenshi waje guda gami da saka yatsunsa cikin na juna "Meye abun jin tsoro a ciki?" Kai ta kada tana gyara zamanta bayan ta goya hannayanta a qirji "Kai din kalar namijin da kowacce mace keso da buri ne,don me bazanji tsoron kar a rabani dakai ba?" Bai bata amsa ba sai kofin daya aje dazun yanzu ya sake dauka,yana mamakin yadda take daukar abubuwan da suka shafe shi da girma haka,saidai har yanzun baya jin wani feeling na daban ko na musamman tattare da ita,yana dorata ne kawai bisa mizanin wasu abubuwa da martabarta ke alaqantuwa dasu "Shine dalilin kenan da kikai qorafi wajen anty hasana?" Ya jefo mata tambayar yana kafeta da ido,gefe guda kuma yana karantarta a fakaice "Aure kikeso?" Kai tsaye ta gyada masa kai a sanyaye tana mai fata da addu'ar cikar burinta,shuru ya ratsa na tsahon minti daya ba tare da wani daga cikinsu yace komai ko yayi wani qwaqwaqwaran motsi ba,ture kujerar da yake kai yayi baya sannan ya miqe tsaye yana kwashe wayarshi da muqullin motarsa "Zamuyi magana later" ya fada yana sauka daga step din da dining din yake kai,da hanzari ta biyoshi a baya tana son tace wani abu,kacibus sukayi da hajiya bilkisu mahaifa ga nafisa,dan dakatawa yayi kadan cikin girmamawa "Au harka kammala kenan?" "Eh zan wuce office ne ana jirana" "To ko saika dawo din?,da akwai maganar da da nakeso muyi" "To ba damuwa" ya fada yana ja da baya,ta wuce yabi bayanta zuwa cikin falon. "Alhaji ne yace na tuntubeka,me zai hana ka dawo cikin gidan nan kaci gaba da zama damu kamar yadda ake a baya?" Nafisa dake lafe kusa da hajiya bilkisu ta daga kai a hankali tana satar kallonshi,addu'a take a ranta Allah yasa ya amince da hakan,da tafi kowa jin dadi a duniya,koda yaushe bata da burin daya wuce ta ganta kusa dashi "Ayima alhj godiya na gode sosai,saidai yanayin aikina bazai bani damar hakan ba,hakan ma alhmdlh babu wata a matsala" dan shuru tayi sannan ta jijijjiga kai "Toh shikenan...babu damuwa Allah ya dafa...." "Don Allah ya an....." Nafisa tayi hanzarin fada don ba hukuncin dataso anwar din ya yanke kenan ba,harara hajiya bilkisu ta jefa mata wanda shine silar yankewar sauran maganar tata,miqewa yayi yayi mata sallama kana ya fice daga falon gaba daya zuwa inda ya aje motarshi. "Ke wace iriyar yarinya ce ne nafisa?,bakiji gargadin da nake miki koda yaushe akan ki dinga kama kanki gaban anwar?,a haka kike tunanin zaki samu qima da daraja wajenshi?" Langabe kai tayi cikin sigar tausayi tace "Afwa mom...." Bata sake ce mata komai ba ta gyara zamantabta dauki wayarta ta shiga danne danne,hakan ya sanya nafisan itama miqewa ta haura sama inda dakinta yake. Kai tsaye gaban mudubi ta isa ta tsaya sosai tana qarewa kanta kallo,har yau cikin zuciyarta bata jin ta mallaki anwar yadda takeso,tanaji a jikinta har yau zuciyar anwar ba tata bace,meta rasa?,meye bata shi?,ta fita komai,ta kere mata a komai,tun daga kyau,kudi zuwa matakin karatu,amma tana jin har yau kamar ta kashe maciji ne bata sare kanshi ba. Da hanzari ta koma da baya ta lalubi wayarta dake aje gefan pillow dinta,sai data fara tura mishi saqo dake qunshe da kalaman soyayya sannan ta lalubi number mema ta kira,bugu hudu ta d'aga "Yayinki ake" mema ta fada cikin daga murya mai cakude da dariya dariya,murmushi nafisa ta saki tana shaf fuskarta zuwa wuyanta,yayin da take sake qarewa kanta kallo a madubi,wannan kalma na mata dadi,amma gaba daya kaman bata aiki akan anwar,duk da cewa bata da wata qwaqwqwarar hujja da zata nuna cewa babu sonta cikin zuciyarshi,saidai ita din bata gamsu da yadda mu'amalarsu ke gudana ba har zuwa yau "Wannan kalma mema taqi amfani akan anwar har yau" "Kai haba?,wane mutum?,shi ya isa?,me ya fiki dashi da zai...." "Dakata mema....kice komai a kaina amma banda akan anwar....mema,ina tunanin mun kashe maciji ne amma bamu sare kanshi ba,zuciyata da ruhina har yau basu gamsu ba,ta yaya zan sake binneta da ranta?,ta yaya zan sake b'atar da ita daga duniyarshi?,inason haskena shi kadai ya wanzu a cikin ruhi da rayuwarshi" "Yanzu me kike tunani?,me kike gani?" "Ke zanwa wannan tambayar" shuru mema tayi na wasu 'yan sakanni sannan tace "Alright ina da wadansu 'yan dabaru da shawarwari,amma yanzu bana qasar,ina benin republic...." "Ubanme kike jeyi can?,ke mema???" Nafisa ta katse meman cikin zabura,tun kafin ta gama bayanin nata,dariya mema ta saki sannan tace "Share kawai" "Ohk....ya zama dole ki dawo to" "Saboda me?" Ta fada a dan tsiwace "Saboda matsalata,kin sani sarai bana son jira?" "Haba hajiyata....kinsan me ya kawoni nan din?,asara kikeson janyomin kenan" "Har ta nawa?" Ta tambayeta kai tsaye "Dubu dari ce ba yawa" "Zan biya....ki tabbatar gobe kin dawo,wajen yammaci mu hadu a indomie joint" "Allah ya barmin hajiyata,karkiji komai,bari na fara hada kayana" ta katse wayar yana fadawa saman katifar dakinta,ba wani benin da taje,ba nisa tayi ba,don a yanzu haka ma tana cikin katsina. Aje wayar nafisa tayi,sannan ta juya ta shige bandaki. Jujjuya wayar yake a hannunshi bayan ya kammala karanta saqon nafisan,sau tari bai fiya maida mata amsa ba,har hakan ya zame mata jiki bata fiya damuwa ba,har zuciyarshi yake hakan bawai da gayya bane,bayajin wani abu dangane da duk wata kalma da zata fito daga bakinta ko ta saqon waya,maida wayar yayi aljihunsa sannan ya fito daga motar tashi ya kashe ya tunkari ginin kamfanin.*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *KO KUMA* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ku danna
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96