Chapter 56
Chapter 56
anty,ko waye aka yi masa haka anty ba'a kyauta masa ba,ta yaya za'a badani kamar an gaji dani,yanzu an siya min mutunci kenan?,kina gani fa shi wanda akace an bawa din bansan ko waye ba,uwa uba yau kwanaki nawa shi dinma bai nemeni ba,qafa da qafa kiran waya ko text,me kike tunanin sun jawomin kenan anty?" Ta qarashe maganar da sigar tambaya idanunta kan anty wanda gab suke da ziraro da qwallar dake cikinsu,kai anty zubaida ke kadawa,ita kanta abun bai mata ba amma uncle hisham ya dakatar da ita kan babu ruwanta,duk wata hanya da zata bi tasha cikin uncle din ya gaya mata na ko waye donta gayawa shahidan ta samu dan relief ya tosheta "Haka zaki haquri shahida,qaddara ta riga fata,amma sai nake ganin idan da laifinsu kema da naki laifin,kinyi wasa da damarki qwarai,shekara nawa nuradden na bibiyarshi ki bashi dama kikaqi,idan da ace kin bashi dama da tuni yanzu wani zancan ake ba wannan ba,nidai bani da wani abunyi bani kuma data cewa saidai ince kiyi haquri kiyita addu'a kawai,nima kuna zan tayaki" kai kawai ta kada,ta bude baki zata ce wani abu wayarta ta sake kadawa karo na barkatai,tare idanunsu yakai kan wayar,nuradden ne,sai anty zubaida ta kalli shahidan "Babu hujja ko alfanun boye masa komai,kawai ya kamata ace ya sani ni a ganina" tana kaiwa nan ta miqe don ficewa ta bawa shahidan damar amsa wayar. ******* ****** ********* A hankali ya miqe daga gaban qaramin akwatin mai lambobin sirri yana sauke nannuyar ajiyar zuciya,duk sanda ya budeshi koda wani abu zai ciro daga ciki saiya tayar masa da wawakeken mikin dake danqare a zuciyarsa,cikin nutsuwa wadda ta cakudu da kasala ya isa gaban akwatinshi ya jefa abinda ya dauko daga ciki ya rufe zip din akwatin sannan ya saukeshi daga saman gadon ya soma janshi har zuwa falonshi. Saman dining ya isa ya zauna a nutse ya soma duba abinda aka dafa din,rabin hankalinsa nakan wayarshi da haka ya zuba abincin ya soma ci,knocikin din da akayi shi yaja hankalinsa,saiya dan daga kanshi yana duban qofar,kafin yace komai aka turo aka shigo,nafisa ce,sanye cikin doguwar riga ta atamfa da madaidaicin mayafi,idanunta bisa kanshi yayin daya dauke nashi idanun ya maida kan abincinsa,hakan yasa tayi hanzarin tunawa da batayi sallama ba,saita dan koma da baya tayi sallamar sannan taci gaba da takowa cikin falon a hankali tana nazarin falon,falon ya jima yana burgeta,duk da wannan shine ganinta dashi na uku,saboda haidar din bai lamunci ta dinga zuwa masa gida ba bayan shi kadaine cikin gidan. Bata tsaya ba har sai data isa dining din,fuskarwa a washe take kallonshi,ta dora jakarta saman teburin tana kallon abincin da yake ci,saita zari spoon ta saka cikin farantin nashi tana cewa "Goodmorning boss" idanunshi ya daga yana janyewa daga cin abincin yana cewa "Morning...me kika fito yi yanzu?" Zama tayi saman kujerar dake daura da ita,ta langabe wuya tana kallonshi bayan ta aje cokalin hannunta "Rakiya mana dear....uhmm....ji nake kaman na bika wlh,kaika janyo mana kaga da tuni tare zamuyi tafiyarmu babu me tuhumarmu" saiya yagi tissue yana goge bakinsa,ya cilla dan qaramin dust bin dake gefanshi yana miqewa daga saman kujerar "Amma dai kinsan akwai wadanda zamu fita tare,kuma duka maza ne,bai kuma kamata ki shiga cikinsu ba ko?" Itama tashi tayi tana daukar jakarta,cikin hanzari harta cimmasa tasha gabanshi "Amma dear,tafiyar wata biyu fa banan kusa bane,ni a wajena ba laifi bane don nayi maka rakiya" *ga mai buqatar sabon littafina da zan fara bayan alqawarin Allah,sai yaje youtube yayi searching SAUTIN HIKIMA,da zarar sunan ya fito akwai rubutun SUBSCRIBE da jan rubutu,ki danna shi sau daya zai koma black,saikiyi screenshot ki turo zuwa number dake qasa,za'a saki a group din in sha Allah* 07038670166 *Ziyarci tasharmu ta youtube don samun qawatattun litattafan hausa,masu qunshe da zallar soyayya darasin rayuwa da kuma nishadi* 👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 https://youtu.be/H7M7h6l6wNM *Alqawarin Allah* 2️⃣8️⃣ Bata tsaya ba har sai data isa dining din,fuskarwa a washe take kallonshi,ta dora jakarta saman teburin tana kallon abincin da yake ci,saita zari spoon ta saka cikin farantin nashi tana cewa "Goodmorning boss" idanunshi ya daga yana janyewa daga cin abincin yana cewa "Morning...me kika fito yi yanzu?" Zama tayi saman kujerar dake daura da ita,ta langabe wuya tana kallonshi bayan ta aje cokalin hannunta "Rakiya mana dear....uhmm....ji nake kaman na bika wlh,kaika janyo mana kaga da tuni tare zamuyi tafiyarmu babu me tuhumarmu" saiya yagi tissue yana goge bakinsa,ya cilla dan qaramin dust bin dake gefanshi yana miqewa daga saman kujerar "Amma dai kinsan akwai wadanda zamu fita tare,kuma duka maza ne,bai kuma kamata ki shiga cikinsu ba ko?" Itama tashi tayi tana daukar jakarta,cikin hanzari harta cimmasa tasha gabanshi "Amma dear,tafiyar wata biyu fa banan kusa bane,ni a wajena ba laifi bane don nayi maka rakiya". Bai amsata ba saida ya ciro wayarshi ya amsa kiran dake shigowa sannan ya maidata ya daga kai ya zuba mata idanunsa da kullum kwanan duniya ke sanya nafisar sake dilmiya cikin so da qaunarshi,kallonsa kawai yakansa taji wani sanyi da sassauci cikin ruhinta,taji tamkar an mata rahama "Waye ya kawoki?"wuya ta noqe tana jefa masa wani kallo da take fata ko yaya yayi tasiri a zuciyarsa "da kaina na taho"hannu ya miqa mata,ta kalleshi tana son qarin bayani "Bani muqullin motar"ba musu ta zuge jakar tata ta dauko muqullin ta miqa masa,saiya sakashi a aljihunsa sannan yace mata muje. Tana gaba yana bayanta,a hankali yakai idanunshi kanta,saiya lumshe idanu yana tuna wani lokaci can baya,lokacin da yake mata rakiya zuwa gida,lokacin da take sadakar shinkafa da wake,ya tuna randa ta zura da gudu tabar mishi botikinta saboda ya furta mata kalaman soyayya,murmushi ya sube masa cikin qiftawa da bismillah kuma murmushin ya bace bat,bacin rai ya maye gurbinsa,ya hadiyi wani abu mai tauri yana girgiza kai,hotunanta ita da saurayin suna yawo a idanunshi,fuskar saurayin daya ajeta a mota har yau taqi barin idanunshi,ya dunqule hannunsa daya yana jin wani abu mai dumi na zagaya jikinsa,har kwanan gobe takaicin dukan da baiwa saurayin yake ba,amma yaci alwashi...yaci alwashin dashi kadai ya barwa kansa sani...... Inda yaje aje motocinsa ya nufa,ta bishi a baya,ya bude daya daga cikin motocin ya mata alama da hannu kan ta shiga,wani dadi ya kamata,yau din taga kamar wani dama dama yake da ita,ta rabeshi ta shiga ta zauna,maimakon shima ya shiga sai taga ya maida murfin motar ya rufe,ya duqa bakin window din idanunshi cikin nata,wanda hakan ya sake narkar da ita ya kashe mata jiki,qamshinsa ya cika mata hanci,kamanninsa suka fito sosai,cikin daddan muryarshi yace "ga driver nan zai kaiki gida,karki sake irin wannan fitar da sassafe haka,zamuyi waya kafin na tashi,motarki kuma zansa a kawo miki ita,sai Allah yayimin dawowa?" Kai kawai ta gyada,ta kasa cewa komai saboda gaba daya jikinta a mace yake dakyau da kwarjinsa,baya yaja ya miqawa drivern muqullin,yana tsaye har suka fice daga gidan,ya saki ajiyar zuciya yana duba agogon hannunsa,da yana da yadda zaiyi ya ragewa nafisa sonshi ko yadda ta damu dashi da yayi,sam baiso ta zura kanta da yawa kamar yadda yayi,shi a ganinsa wannan shine babban kuskure ko gangancin da mutum zaiyi a soyayya. ***** ****** ******** A hankali take takowa zuwa qofar gidan nasu,sanye da dogon hijabi har qasa mai hannu,kallo daya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96