Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 62

Chapter 62

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,307 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

basu da muhimmanci,zuwankin da ganinki ya fisu muhimmanci" wani farinciki data jima bataji kamarsa ba ya tsirga mata,ta lumshe ido tana sakin murmushi,ta jima bata ji kalmar data mata dadi matuqa daga anwar din ba irin wannan,sannan ta budesu idanun nata a kanshi "Ya gida yasu momy" "Kowa lafiya suna ma gaidaka" ta fada tana zuba masa lemo sannan ta tura masa,bai musa ba yaja yadan kurba tana binsa da kallo,batasan wane irin qauna takewa anwar din ba,jifa jifa take sako hura yana tayata kana ta sako masa zancan bikinsu,lissafin events da zatayi da sauran abubuwa,yana kurba yana saurarenta sai daya shanye sannan yace mata "Next week za'a kawo lefen idan Allah ya kaimu....saidai kuma kafin sannan inason nayi wata muhimmiyar magana dake,duk da na riga na shaidawa su momy amma naga kece yafi cancanta ki sani,kuma ni yafi dacewa na sanar miki da kaina" dukka hankalinta ta bashi ganin yadda ya tara shima nutsuwarshi waje guda gamida soke yatsunsa cikin na juna yana dubanta sosai "Uhmm,ina jinka" "Komai da kika gani a duniya muqaddarine daga Allah,hakanan ba wanda ya isa sauya tsarin Allah,yadda ya tsarawa bawa haka zai karba,naka kawai ka gode masa,zaka iya tsarawa rayuwarka abu amma idan baiyi dai dai da tsarin Allah ba zai sauya maka ne da wanda yake ganin shine daidai da rayuwarka kuma shine mafi alkhairi,to...ina tunanin ku biyu za'a daura mana aure dasu lokaci guda,na nemi aure watanni biyu baya da suka wuce Allah ya qaddara kuma an bani,yanzu haka cikin satin da za'a kawo naki kefen suma za'a kai,lokacin daurin aurenma kusan daya ne,rana ce kawai aka bambanta,kinga ya kamata ace kin sani saboda kina da haqqin ki sani din,nasan mai yiwuwa hakan zai bata miki rai saboda halin kishi irin na mata,saboda haka ina mai baki haquri tare da shaida miki haka Allah ya qaddara dama tun fil'azal shi yasa ya hukunta faruwar hakan,ina fata hakan bazai dameki ba don kowacce cikinku matsayinta daban" wani irin abu taji yana mata yawo tsakiyar kaa kamar ana yamutsa qwaqwalwarta,wannan wacce iriyar mummunar rana ce?,wanne irin mummunan labari kunnuwanta suke dauko mata?,saita cije lebanta da kyau ga zatonta mafarki take ko zata farka,saita fuskanci da gaske ne,wani abu ke niyyar toshe mata numfashi,ta fahimci idan bata bari tayi kuka ba wani mummunan abu na iya faruwa da ita,saboda haka kawai ta saki hawayen da take qoqarin tarewa suka soma zuba "Wanne irin abu kake gayamin haka anwar?,kana gayaminne fa kishiya zaka yimin tun ban shiga gidanka ba,anwar kana gayamin zaka hada soyayyata data wata ne fa,kana gayamin zamu hada miji da wata,zaka raba soyayyarmu,wai shinma yaushe ka ganta harkaji kana sonta kaji zaka iya aurenta?" "Karki damu,ba wata sabuwa bace cikin rayuwata,mun jima tare,rabuwarmu da ita qaddarar haduwarki dani ce" "Shahida?!" Ta fada cikin razana da kuma salo na tambaya,saiya zuba mata idanu yana kallonta tare da mamakin kama sunanta farat daya da tayi kafin daga bisani yace "Eh,ya akayi kika santa?" Sam batabi takan tambayarshi ba saboda ji take kamar alqiyamarta ta tsaya,a ina ya tono shahida?,a ina ya ganta?,ya akayi suka daidaitawa?,ya akayi ta aminta zata aureshi?,ya akayi yaci gaba da kulata?,dama soyayyarta bata mutu cikin ransa ba?,inaa,har abada ba zata taba yarda ta hada anwar da shahida ba qarqashin inuwa daya,kuma ta kasance a tsakiyarsu?,ashe data cika shashasha "Kacemin kawai ka koma wajen tsohuwar masoyiyarka donka samu damar wulaqantani idan ka aureni,har abada anwar bazan hadaka da wata ba,bazanyi zaman kishi da kowa ba,bazan zauna da kishiya ba" ta fada tana miqewa tsaye,cikin hargagi,hannunshi ya daga mata a nutse "Ki nutsu nafisa ki samu waje ki zauna" "Bazan nutsu ba,bazan zauna ba,ka daina kiramin nutsuwa a wannan yanayin,saidai ka zaba koni ko ita" furucin ya fito hade da kuka mai cike da tashin hankali "Ba wanda zan zaba hakanan ba wanda zanqi zaba" ya amsa mata kai tsaye tana dubanta cikin yanayin dake nuna jarunta da mazantaka na jajirtaccen namiji,kai take jinjinawa hawaye na zuba daga fuskarta sosai yana hadewa da majina,ji take kaman ta cire ranta,ji take kama ta dauki numfashin shahida da bata tashi dawowa rayuwarta ba sai sanda ta sakankace take saka ran ta mallaki anwar,tana ganin da tayi faduwar baqar tasa,data shiga ta zama 'yar kallo gwara ta haqura dashi har abada "Anwar!...kaje ka auri shahida bazan aureka ba,bazan aureka ba har abada" tana kaiwa nan ta juya da gudu gudu sauri sauri tayi cikin gida,yayi niyyar dakatar da ita amma sam bata tsaya ta saurareshi bama bare taji me zai sake fada,saiya furzar da numfashi,kana ya ture kujerar baya ya miqe yana daukar muqullin motarsa gamida da handkherchief dinsa dake aje saman teburin ya saka cikin aljihunsa ya nufi qofar fita,sai daya shiga parking space sannan ya dauki motarsa yayiwa mai gida horn ya bude masa gate ya fice daga gidan cikin nutsatstsen tuqi. Yana tuqin yana furzar sa iska mai dumi daga bakinsa,wai me yasa mata dukka harkarsu matsala ce?,don kawai yace mata ba ita daya za'a daurawa aure dashi ba shine xata masa wannan jinnun?,to xaya zuba ido yaga iya nata gudun ruwan. Wayarshi dake aje gefe ta dauki rura,yadan juya ya kalleta,ganin number anty usaina ce ya sanyashi dagawa,ya saka handsfree ya aje gefansa "Kana wajen ta ina ne?" "Ina hanya anty" "To shikenan saika iso"bai amsa ba ya katse kiran ya aje wayar ya maida hankalinsa ga tuqinsa,duka hannayensa na zube saman sitiyarin,yayin da rabin tunaninsa ya tafi ga abinda nafisan tayi yanzu,me take tunani?,zaita binta ne yana lallashinta?,ko yace ta taimaka ta aureshi?. Yana fitowa daga motar su sa'ida suka shigo gidan,dawowarsu kenan daga makarantar dare dake can daya bangaren na unguwarsu,ba yadda anwar din baiyi ta qyalesu ba amma tace sam batason zaman banza,zaman kallon bayan sallar magariba daga waccar tashar a koma waccar,dukansu suka iso suna masa sannu da zuwa ya amsa ya shiga cikinsu suka shige cikin gidan. Qaramin falon anty usaina suka shiga suka bar yaran a babban falo,idanunsa nakan tauraruwa tv anty usaina ta shigo ta aje masa abinci,kallon abincin yayi " banajin yunwa anty"tana shirin zama tace "Kaci a gidan abinci kenan?,gwanda dai kayi auren nan suma sa huta da ganinka" murmushi ya saki yana shafa kanshi,zama tayi suka gaisa "Ya za'ayi da kayan lefen?,na ina za'a fara kaiwa?" Tsaki yaja can qasa sannan yace "Ni kaina ban sani ba,ina tunanin iya nasu za'a kai,don nafisa tace ta fasa" idanu anty usaina ta fiddo "Ta fasa kamar yaya?"hannayenshi ya watsa sannan yace "Oho,na shaida mata kawai su biyu ne dalilin da yasa tace ta fasa kenan" saita sauke ajiyar zuciya tana dubanshi "Don tace ta fasa bawai yana nufin ta fasa dinne ba,kishi ne kawai da bacin rai,lokaci qanqani zata sauko,saboda haka ba za'a fasa shirin komai ba,zuwa gobe ka kirata ka bata baki duk yadda kukayi saika sanarmin" kai kawai ya gyada yana mita qasan zuciyarshi,yadan jima anan suna tattaunawa sannan daga bisani yayi mata sallama ya wuce. A guje nafisa ta shiga falon gidan nasu ta wuce momy dake zaune tana kallo ta haye sama dakinta,da kallo momyn ta bita harta shige,saita dauke kai tana sauke ajiyar zuciya,dama ta sani za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya,yadda nafisan ta dora burinta da rayuwarta duka kan anwar din tasan za'a sha gwagwarmaya duk

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});