Chapter 20
Chapter 20
ba. Shi dinma gaba daya saiya daina ganin 'yammatan dake kai kawo a wajen,ita kadai take gani cikin dinkin ankon da ya amshi fatarta fiye da zato,kowa idonsa cikin na dan uwanshi a haka ta qaraso,baice mata komai na sai gaban motar daya bude mata ta shige,shima ya bude sit din driver ya zauna bayan kubra 'yar anty umma ta shiga gidan baya ya tada motar. Saitake jinsu yau kaman rana ta musamman ce a wajensu,wani farinciki taji yana ratsata,ta samu kanta da addu'ar Allah ya shiga lamarinsu ya buda ma anwar din,motar tayi masa kyau qwarai da gaske kaman tashi "Wani abokina ne ya dage lallai lallai yau sai na amsheta na dana,tun tana sabuwa yamin tayi ban taba danawa ba,kinga kuma bai kamata naqi ba karya dauka wani abun ne na daban kuma" kai ta gyada yayin daya dinga satar kallonta lokaci zuwa lokaci,har bintu ta fahimta ta d'an masa tsiya,kunya ta sanya shahida daukan wani plate data gani ta saka jikin redion motar,tadan qaro volume sanda taji batajin me yake fita daga cd din,waqa ce ta hamisu breaker waqar jarumar mata,sautin waqar ya ratsa motar,kidanta ya fita sosai ta speakers din motar ya karade ko ina,har ta saka hannu zata kashe anwar ya daga mata hannu alamar ta barshi,shuru ya ratsa motar saidai gaba dayansu waqar na ratsasu ne,ji suke kaman su suke rerawa junansu,shurun yaci gaba da yi musu jagora har zuwa inda za'a gabatar da bikin. Sai daya rakata har ciki yayi mata mazauni,ya kuma gaya mata bai yadda da shiga rawa ba sannan ya fito ya dawo cikin motar ya zauna,wanda ya faka ne a bakin titi,sai yabar murfin motar a bude iska na shigowa qafarsa daya a waje. Awa guda da fara gabatar da bikin yana zaune yasa sauraren redio "Yauwa ga wani can....salamu alaikum" yaji an ambata,kanshi ya dago yana dubanta sannan ya amsa,matashiyar budurwa ce wadda a qalla ta doshi shekara ashirin da d'aya,sanye cikin doguwar riga da siririn mayafi,fuskarta saye da tafkeken glass,gabanta ne yayi mummunar faduwa saboda cika mata idanu da kwarjini da yayi mata,uwa uba kyau data jima bata ganshi tattare da wani d'a namiji ba,da qyar ta tattaro miyan bakinta tace "Don Allah bawan Allah ko zaka taimaka ka duba mana motarmu?" Tayi maganar tana qare masa kallo ta cikin glass dinta,sai daya kashe redion sannan yace "Me ya sameta?"yarfar da hannu tayi cikin yauqi "toh wlh ban sani ba,ina cikin driving ta soma slow sai kuma ta tsaya gaba daya" dan jim yayi kafin ya jinjina kai ya fito daga motar ya rufeta sannan yayi gaba zuwa inda motar tata take. Tsahon wani lokaci yana qoqarin ganin ya gyara saita tashi saita sake mutuwa,saboda haka ya dago yana goge hannunsa da tsumma "Gaskiya dole sai bakanike yazo"ya fadiwa nafisa dake gefe tsaye suna qare masa kallo ita da qawarta mima "Ya salam...bari na kirashi Allah yasa yana kusa" ta ciro tsadaddar wayarta ta soma nemanshi,cikin sa'a yace yana kusa ta bashi adress din inda motar take "Idan ba damuwa ko zamu dan zauna cikin motarka kafin ya iso saboda zama a wajen ba dadi" nafisa ta fada sanda anwar ke komawa zuwa cikin tashi motar,tsayawa yayi ya waiwayo,kaman yace a'ah sai yaga mata ne bai kamata ya barsu tsaye ba,tunda motar tasu ba zasu iya zama cikinta ba,shi kuwa diya mace ako ina take yana da kishi da qoqarin kare mutunci da martabarta bakin gwargwado koda bai santa ba "Ba damuwa" ya fada yana sake yin gaba,idanu suka hada da mima ta kashe mata ido gami da sakin murmushi suka bi bayansa. Ya tsammaci duka baya zasu shiga,sai yaga mima ce kawai ta shiga bayan,nafisa ta shiga kujera mai zaman banza,sai data zauna sosai sannan ta waiwayo ta dubeshi tana murmushi "Suna na nafisa....kaifa?" "Muhammad anwar" ya bata amsa a taqaice,idanu ta lumshe "Nice name...sunan ya dace da maishi" saiya waiwayo ya dubeta kafin ya dauke kai,murmushi ta sake saki "Dan wanne anguwa ne kai?,Allah yasa ban matsanta maka ba da tambaya" kai ya jinjina sannan ya gaya mata unguwar da yake "Kai ai bamu da nisa sosai" itama tasu unguwar ta fada masa,kusan duk unguwannin nasu maqotan juna ne,shuru ne ya sake ratsa tsakani yayin data lula duniyar tunanin yadda zata sha kan anwar,don ba zata cuci kanta ba kallon farko taji anwar yayi mata,infact ma zata iya cewa ta kamu da sonshi ne kai tsaye. Isowar mechanic din shi ya katse duk wani tunaninta,hanya daya ta rage mata saboda haka ta miqa mishi wayarta "Idan ba zaka damu ba ka sakamin numberka mana,saboda nayi maka godiya" kai ya girgiza "Basai kinmin godiyar komai ba" kai ta langabe "Ya zama dole na gode maka,saboda alkhairi kayi min" baison jan zancan saboda ya gaji da surutunta,saboda haka ya amshi wayar daidai sanda shahida ke takowa zuwa inda motar take,tana iya hango komai saboda akwai haske cikin motar,mummunar faduwar gaba ta samu,saidai ta kasa hana kanta qarasawa wajen,saitaci gaba da takawa harta isa bakin motar,daidai sanda ya gama saka mata number din ta amsa tana murmushi tace "Na gode,sai gani na gaba" ja baya shahida tayi a hankali sanda nafisa ke fitowa daga gaban motar,idanunsu suka hadu dana juna,kallon kallon suka yiwa juna kafin nafisan tayi gaba mima ta rufa mata baya,binsu shahida tayi da kallo har suka bacewa ganinta cikin duhuwar wajen sannan ta dawo da dubanta ga anwar wanda sai sannan ya lura da tsaiwarta a wajen.*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos *Alqawarin Allah* 1️⃣1️⃣ "Wacece?,me takeyi a nan wajen?" Ta tambaya tana daga tsaye ba tare data shigo cikin motar ba "Motarsu ce ta lalace nayi qoqarin gyara musu,bata ma gyarun ba sai data kira bakinikensu" "Shine tazo kusa da kai ta zauna?,har kana amsar wayarta tana jifanka da murmushi?" "Shigo tukunna sai muyi maganar" ya fadi yana bude mata murfin motar sosai,kaita girgixa sai kawai ta juya tabar wajen idanunta cike fal da qwalla,cikin hanzari ya fito don ya cimmata saidai ina tuni ta kutsa cikin mutane ta bace masa bat,haka ya qaraci nemanta bai ganta ba,dole ya dawo gaban motar ya dinga jera mata kira amma bata daga ba. A hankali wajen ya soma yoyewa,ya sake shiga ya dubata amma kome kama da ita bai gani ba bare ita "Ya salam shahida....ya salam" ya dinga furtawa a jejjere sanda yake tuqa motar zuwa hanyar gidansu amaryan,ba qaramin tashi hankalinsa yayi ba,bai samu 'yar nutsuwa ba sai daya isa gidan yasa aka shiga aka binciko masa aka tabbatar masa ta dawo gidan nan sannan ya saki ajiyar zuciya,nan kuma ya shiga jera aiken kiranta,saidai mirsis taqi zuwa,ganin dare ya soma yi ya sanyashi haqura kan tilas yaja motar yabar unguwar,bai je gida ba sai daya soma kaiwa abokinsa matar,yace daya barta ma sai sun gama bikin don tafiya ma zaiyi ta sati guda,murmushi ya saki wanda kusan na yaqe ne,donshi kusan sam baiji dadin hawa motar ba,yana ganin kaman itace silar faruwar komai,inda ace a motar haya suka tafi shikenan nafisa ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96