Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 85

Chapter 85

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,315 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba saime?,akwai dubbai da suka damu da ita,don na taimakeki ma na rabi rayuwar taki shine kike wani zaqalqalewa kina zaton ke watace a wajena?" Ido da baki duka ta saka tana son tantance me yake cewa,daidai lokacin da qararrwar dake nuna akwai baqi can falon qasa ta soma kadawa,saiya miqe kawai yana tabe mata baki ya fice ya sauka qasa. Daada ce ita da mubina da khadija,su sukayi waya dazu kan zasu rakota,tun bikin daada bata koma ba umma tace saitayi sati uku,sai yanzu ta soma shirin komawa,zuwanshi gidan wajen daada hira babu adadi,ta fuskanci abubuwa da dama game da zamansu ba tare daya gaya mata ba,da batayi niyyar zuwa gidan ba sam,amma taga ya kamata ta danyi gyara ko yaya ne kafin ta wuce karta tafi tabar baya da qura,don tasan umman shahidan koda wasa ba zata taba taka gidan shahida a yanzu ba,donko hira ake bata sanya baki,yaji qishin qishin din zata zo din yau dalili kenan dayasa ya tsare shahidan a sama don kar daada ta ramfo komai,don hausawa sunce babba babba ne,abinda zai gano ko kahau bishiyar rimi ba zaka hangoshi ba. Shi ya tarbesu daada tahau baza ido "Ina ita waccar ja'irar,kaine kake tarar baqin ita kuma tana me?" Murmushi ya saki "A'ah a'ah,kawai yaune na karbata,tana sama batajin dadi ne,ta samu targade a qafarta" "To ce mata ta sauko,don tayi targade saboda tsabar son jiki shine zata hau sama ta nade?,oh ni habiba,yaran yanzu saidai abarsu,kamar wadda ta karye" "Yi haquri daada karki rudamin mata,kin manta ke mai laifi ce dama?" Ya fada cikin tsokana,da ido ta bishi baki sake "Iyeeee....au wato harka soma bin bayan matarka?" Murmushi ya saki sosai sannan yace "Yi haquri daadarmu,so so ne amma aisonkai yafi ko?" Kasa amsashi tayi,cikin zuciyarta tanajin sanyi da dadi na yadda ta fuskanci.yana kulawa da jikarta,ta cika da fata da addu'ar Allah yasa itama haka take masa kada ta basu kunya,kada kuma ta watsa musu qasa a ido,mubina yasa ta shiga kitchen ta hada musu abin motsa baki,sai dayaga ta shirya musu komai sannan ya zqri muqulli don zuwa ya sama musu abinci "Ku hau saman daada ku sameta kafin na dawo" "Kaga nifa ba zama zanyi ba,mai motar daya kawomu ma yana qofar gida yana jira in fito ya maidani,don yau ni kam kwanan garinmu zanyi" qememe taqi barinshi ya fita,tace saidai yahau sama ya sauko mata da shahida "Kiyi haquri daada ki hau,ba zata iya saukowa ba" "Ita sabon qashima taqi saukowa bare ni tsohon qashi za'ace nayi tattaki nahau,tunda goya mata baya kake tayita narkewa kaga tafiyarmu" daqyar ya lallaba daadan tahau saman,inda mubina da khadija sukayi xamansu nan falon suna kallo. Har yanzu tana zaune saman abun sallah a haka daada ta shigo,sai taji dadin zuwan daadan,tana ganin tazo a daidai,ita ta qulla komai saboda haka dole ta yiwa anwar magana ya barta ta koma bakin aikinta,ba yabi ba fallasa ta gaidata,ta amsa tana qare mata kallo,bawani sauyi data gani tattare da shahidan na mace me aure,saita tabe baki,zata fara magana shahidan ta rigata cikin sautin wanda keson fashewa da kuka "Daada ki masa magana ya barni na koma aikina,kinga tun asali da aikina ya ganni,sannan kuma baice min bazanyi ba sai jiya da nake gaya masa zan koma yace waina gama aiki,daxun nan kan ku shigo ya dauki wayata ya ballamin layina waina daina amfani dashi" rashin sani yafi dare duhu,wani kallo daadan ke mata akaikaice,sai data gama tsaf sannan tace "Yo ai ni banga wani abun azo a gani dakika tabuka ba daxai nuna kinsan ma kina da aure,daga ke harshi banga wani sauyi tattare daku ba" "Kai anwaru" ta kira sunanshi tana zare ido,ya amsa mata ta masa nuni da kusa da shahida "Xauna nan" ba musu ya zauna yana qunshe dariya,daada sarkin rigimammu,da alama akwai magana a bakinta "Tunda kuka tare ta taba maka kwanan turaka?" Ta jeho masa tambayar kanta tsaye,take qwaqwalwarsa ta gaya masa abinda take nufi,kunya ta rugo ta rarumeshi,bai taba tunanin tambayar da zata masa kenan ba,cikin hanzari yace "Daada ai...." "Aime?,idan baka da amsa to bari na amsa maka,bata taba ba,kalli qafafunta da wuyanta,idan tace ma eh to qarya take,oh la'ilaha illallahu muhammadarasulillahi sallallahu alaihi wasallam" ta debo salati tana tafa hannuwa _afwa masu karatu,kunsan yadda sabgogi ke kutso kai cikin rayuwa_🙏🏽 *Alqawarin Allah* 40 "Ni habiba naga abinda ya isheni.....rahama?!" Tayi kiranta da sunanta na ainihi,daga ita har anwar din sai sukayi tsuru tsuru suna kallon daada yadda ta dauki abun,kunya da daurewar kai duk suka cikasu "Kinason ki gama lafiya kuwa?,kinsan tsinuwar mala'iku kuwa akanki?,so kike ki shiga wuta da qafafunki?,to wallahi kishiga taitayinki karki jawowa kanki masifa ki jawo mana,rahama!" Ta sake kiran nata cikin kambama abun,yadda daadan ke magana da yadda shahida ta soma turo baki fuska a hade cikin bacin rai saiya so baiwa anwar dariya,shi tuni a nasa shekarun ya fahimci tayine tana sane donta tsorata shahidan,ta kuma sake kawo gyara a zamansun gaba daya "Yanzu daada fisabilillahi waya gaya miki wannan maganar?,shi yace miki haka?ko kuwa ni?" Daquwa ta watsa mata "Kinci gidanku,don gyatumarki a tsufana ni akwai abinda za'a boyemin?,to wallahi wallahi tun muna shaida juna ni dake ki gyara duk abinda na gane da wanda ma ban gane ba,duka kin fini sani ai basai nayi filla filla ba,kin ganni nan bana daukar sakarci,ba abu bane me wahala na miki dukan tsiya cikin gidan nan kibar ganin kina da igiya a kanki,girma kuwa ban ganshi ba bare ya hanani dakarki,aiki kuma ba zakiyishi ba haihata haihata...." "A'ah daada....ba'ace haihata haihata ba" anwar ya dakatar da daada yana boye dariyarsa wadda shahidan ta fuskanci hakan,ta sake qulewa sosai,wato ita tako ina bata da nasara,bata da rinjaye kenan? "Zatayi aiki idan tanaso....amma ba bisa qarqashin kowa ba sai qarqashina,zatayi aiki a nawa companyn kuma a office dina" ya qarashe zancan yana duban daada ba tare daya dubi shahida ba,don yasan kai tsaye cewa zatayi ba zatayi ba,amma ga mamakinsa sai yaji ta amsa da "Na amince zanyi" ta amsa masa idanunta qyar a kansa,tasan yayine don ya qureta yayi da manufa,ita kuwa tacu damarar takura masa itama tunda har ya bullo ta wannan hanyar,sai daya gama karantarta ta qwayar idanunta sannan ya girgixa kai "Well,hakan yayi,daga yau daga yanzu ma na daukeki aiki,za'a dinga kuma baki salary kamar na kowanne ma'aikaci dai dai da matsayinka,salary dinki shine salary na farko dayafi na kowanne ma'aikaci yawa duba da matakin aikin dana baki" kaita juyar tana hadiyar bacin ranta,cikin ranta ba haka taso ba "Shikenan ma,shine daidai,kaga kuna tare ko yaushe,tuwona maina,yamafi tsari" daada ta fada tana ware hannaye,daga haka daadan ta miqe bayan ta sake kwakkwafar shahidan,ba yadda anwar baiyi ta zauna ba tace sam,daqyar shahida ta iyayi mata a sauka lafiya,ya fita rakata. Cikin kwanakin hakanan shahidan naji na gani ta zauna saman nashi,saidai kwana uku rak tayi wanda ta jita kaman akan wuta take,a falo duka tayi xamanta,sai shima ya shareta kawai ya shiga sabgarsa,randa taji dama dama a qafarta ranar ta sake tarkatawa ta koma dakinta. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 A hankali take takowa zuwa bakin dining din donta samu tadan dumama cikinta,bayan ta gama shirinta tsaf kamar yadda ta saba duk lokacin da zata je office,madaidaiciyar kwalliya tayi wadda ta qawatar da ita

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});