Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 42

Chapter 42

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,299 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bude flask din dake gaban mubina ta gutsiro wainar takai bakinta "Da tunima na gama ai,maqociyarmu ce ta shigo umma tace a zuba mata shine nake tara miki wata yanzu" "Ummmm....amma fa tayi dadi sosai" ta nemi waje kusa da mubinan tana zama ta janyo yaji ta soma gutsira tana dangwala,mubina na bata labarin bikin wata cousin dinsu dake matsowa,shirin da akeyi anko da dai sauransu "Kowa shiri yake yaya sosai,kinsan wanda zata aura din yana da kudi ba laifi" murmushi kawai shahida ta fitar,wato duk wadda akace yau zata auri me danshi murna ake mata "Allah yasa abokin zama ne,ya sanya alkhairi" "Ameen yaya,naga umma ma tasa an kawo mana ankon,amma bandake" harararta tayi "Ce miki akayi ni cima zaune ce da za'a min anko?" Dariya mubina ta qyaqyace da ita "Waya isa yace miki cima zaune,hajiya accountat da kanta"sai data ci ta qoshi sosai sannan ta isa bakin famfo ta wanke hannunta ta daura alwala ta wuce falon umma. Da sallama ta shiga,su biyu ne zaune suna hira,ita da wata baquwar fuska da batasan wace ba,saidai kallo daya ta yiwa matar taji gabanta yayi mummunar faduwa,itama matar idanunta kan shahida,murmushi kan fuskarta tana amsa sallamar tata,dauke idanunta tayi ta samu gefen kujera ta zauna "Sai yanzu kika shigo?" "Haba tun daxu umma,na tsaya naci waina ne" "Ashe takice amma umma ta bamu muka cinyeta" cewar matar cikin fara'a,sai shahida ta juya ta dubeta itama fuskarta ba yabo ba fallasa tace "Ina yini?" "Lafiya qalau,mun yini lpy shahida ko?" Ta amsa gaisuwar gami da jeho mata tambaya daga qarshe,kai ta gyada tana mamakin yadda akayi matar ta san sunanta,bayan umma bata furta sunan a gabanta ba "Tunda nake zuwa ban taba ganinki ba sai yau,Allah dai yayi yau zanga yaya shahida" ta kuma fada tana murmushi,itama murmushin shahidan ta maidata mata,ganin kaman bata saki jiki ba ya sanya umma cewa "Maqociyarmu ce nan gaba kadan gidanta yake,tayi wajen wata shida da tarewa sai yanzu Allah yayi ta leqo mana,gidan nan da faruq yake gaya miki ana sadaka duk juma'a?" Sai a sannan ta fahimci gidan da take nufi,kai ta gyada tana sake fadada fara'arta,don mubina tasha bata labarin kirkin matar,daki ta wuce daga haka tana jiyo hirarsu da umma. Har ta gama zamanta ta soma shirin tafiya matar tana nan,a nan taci abincin dare tare dasu umman,mamaki take sosai shahida,a ina suka santa ne?,wace ita?. A falo tana rataye da jakarta ta dubi mubina "Cikin kayan da antyn katsina ta kawo miki daukomin na zabi style zankai dinki,yi sauri ki daukomin,sa'id yayi anguwa mai nisa yace ya barshi basai ya dawo dakata ba tunda kusa da anguwarsu yake,motar haya zanbi kar dare ya sake yimin" "Wallahi duka na sakasu yaaya suna wajen wanki" goshinta ta dafe tana jan dan tsaki cikin rashin jin dadi "Halinku daya ai indai mubina ce,kowanne kaya da an saka an cire duk kyanshi sai ruwa,saiki haqura ai har sai ta karbo itama da dan banzan sanabe,ki kama kayanki ki wanke amma saikin kai wankau" murmushi matar tayi har fararen haqoranta suka bayyana kan idanun shahida,gabanta ya sake faduwa,matar tana mata kama da wata,kaman ta taba ganin fuskar "Kinga qanwata zo muje ki zabi style wanda kikeso kinji"tayi maganar sanda ta miqe tsaye ta dauki hijabinta dake aje gefe tana sakawa,kallonta shahida tayi,sai taji tana jin nauyinta sosai,banda haka ce mata zatayi a'ah ta barshi,amma saita kasa fada,don ita gaba daya ta jima rabonta da sake amincewa da wani a rayuwarta,duk wata baquwar fuska da zatayi kutsewa rayuwarta kaffa kaffa take da ita. "umma...ina kuka samota newai?,ni gaskiya ba wani gidanta da zan bita" shahida ta fada dai dai saitin kunnen umman cikin nuna rashin yarda "Babu komai matar sananniya ce,hakanan mun dan jima tare,kije kawai" hakanan jiki ba qwari ta fito ta sameta bakin famfo tana daura alwala,ta kammala ta yiwa umma sallama suka fice. Ko a tafiyarma bata yarda sun hada kafada ba,tana gaba ne tana binta a baya,duk da haka takan juyi jefi jefi ta sako ma shahidan hira,nata eh ko a'ah ne har suka qaraso gate din gidan,tsaiwa shahidan tayi tana kallon gidan,kaman taso ta taba ganin anwar tsaye bakin gate din sau daya,saidai bata tabbatar dashi dinne ko bashi bane,kawai dai tun daga ranar ta tsani kallon qofar gidan ma "Muje ciki mana shahida saiki zaba a nutse" murmushin yaqe ta saki "Nan ma ya isa,idan da yara saiki turo su miqo min na wuce,yau nayi dare sosai a waje takwas ta kusa" "Yanzu zaki wuce ai,ki shigo ko kuma nace mubina ta fiki kirki dason mutane" murmushi tayi saita bi bayanta kawai. Sosai falon ya burge shahida,komai a kammale a tsaftace yana fitar da qamshi "Zauna gu waje nan shahida" tana nuna mata kujera da hannu,a darare ta zauna din tana bin falon da kallo mai gwanin sha'awa da burgewa,sanda yake fidda hijabinta wata 'yar budurwa ta sauko daga sama ta matakalar benan dake falon "Sannu da zuwa ummi kin dade yau" ta fada tana duban maman tata "Wallahi sa'ida...yauwa shiga dakina ki bude wardrobe dina,inda na aje dinkunan da aka kawomin din nan shekaran jiya ki cirosu gaba daya" "Toh" ta amsa tana shirin juyawa idanunta ya sauka kan shahida,saita sake juyowa da sauri ta kalleta ta kalli ummin nata,sai kuma ta juya ta sake hayewa saman. "Ina zuwa shahida kinji" ta fadi tana nufar wata qofa dake nuna alamun kitchen ne,wayarta dake jaka ta dauki kuka alamun kira ke shigowa,ta cirota tana dubawa,noradden ne,saita latsa tana karawa a kunnenta "Ranki ya dade,ya akayi sa'idu yabarmin ke a waje da daren nan?,naje gida baki nan,na kirashi yace wajen umma yabarki,kuma kince basai ya dawo ba" "Eh uzuri nayi masa ne" ajiyar zuciya ya aje "Ni gaki kin fiddoni,kema kinsan ba yadda za'ayi na iya kwanciya kina waje,fito gani a qofar gida" "Na fito daga gidan ai" "Ina kika je?" "Ina maqota" sai tayi mishi kwatancen gidan yace gashinan,babu jimawa ta fito dauke da wani dan qaramin faranti da aka dora ruwa da lemo,gefe daya dambun nama da meatpie ta aje gabanta "Ga ruwa kisha" murmushin yaqe ta danyi don har yanzu a darare take,hakanan taji ta kasa sakewa "Na qoshi wlh anty" "Da alama dai da gasken shahida baki da kirki" dariya maganar ta bata,saita kuma sakin murmushi sosai "Ba haka bane anty,kina gani kusan ma tare mukaci abincin" "Eh...amma ko albarka kyasa" bata sake cewa komai ba ta gutsuri meatpie din kadan,dai dai sanda ta qwalawa yarinyar kira "Sa'ida me kike ne?,kiyi sauri sauri fa take gida zata wuce" "Gani nan ummi" tana maganar ne sanda take sakkowa daga saman cikin sassarfa rungume da kayan a qirjinta,a gaban ummin ta zubesu "Riga daya ce ban gani ba ashe ta shiga cikin wasu kayan "ok...gasu ki xaba wadanda zasu miki" a nutse take daga dinkunan,duka sun mata hakanan sunyi bala'in kyau,tana son yace xata dauka duka tanajin nauyinta,saita zabi uku daga ciki "Wadan nan ma sunyi,na gode" tura mata sauran tayi "Jeki dasu gaba daya,mai yiwuwa telan yaga wanda zaifi miki kyau akan wanda ke kika zaba" haka ta tattara duka kayan ta zuba mata a wata 'yar jaka mai kyau,ta mata sallama ta fito. Yana tsaye jikin motarsa wayarsa na hannunshi yana danne danne,ganin fitowarta ya sanyashi

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});