Chapter 61
Chapter 61
"Wallahi daada bana sonshi,shima daada ba sona yake ba bazai gaya muku gaskiya bane kawai" baki ta tabe tana mata duban sakarya "Au Allah ko?,ashe tun farkon saninmu dashi mu muka jajibo miki shi ko?,ashe qiyayya ce ta hadaku a baya ba soyayya ba?" "Daada baya sona yanzu bana sonshi!" Ta sake fada cikin kuka "Eh naga alama,shi yasa bai bar kakarki ba yaci gaba dayi mata aike a boye bai bari nasan wayeshi ba,kuma qiyayyar ce tasa ya tasl qafa da qafa ya nemi aurenki hannun iyayenki" "Wallahi daada kinji na ra ntse miki da manufa a lamarinsa" "Dama akwai auren da babu manufa?,shirme kenan" ganin duka taqi fahimtarta saita sauko gwiwoyinta qasa tana kallonta "Daada,don girman Allah ku maida masa kudinsa,ko bazaku bani nuradden ba na amince ko zabamin ko waye a lokacin da kuka saka na bikin nawa ayi dashi" nazarinta daadan tayi na wani dan lokaci sannan ta kamata ta miqar da ita tsaye "Naji,zauna muyi magana" sanyi taji yana ratsa zuciyarta,ta soma jin qamshin nasara,saita miqe din kamar yadda daada ta buqata suka koma saman kujera suka zauna. Saidata bata 'yan mintuna ta nutsu tukunna sannan tace "Komai da kika gani a rayuwa yana da dalili,inason ki gayamin dalilinki na duka wadan nan maganganun da tsallen badaken qin auren mutumin da kowa ya shaida kuma yana da labarin soyayyarku" shuru tayi kawai tana qiyasta ta yadda zata gayawa daadan komai bayan basusan komai ba akan rayuwar data fada a baya,sannan uwa uba shi kansa anwar din ta fahimci ba wanda ya taba gayawa ko bashi labarin komai,idan ta aikata hakan kamar ta dabawa cikinta wuqa,kamar ta yaye mayafin asirin da Allah ya rufa mata kenan?,ganin tayi shuru sai daada tayi tsammanin ko batason magana ne a gaban hasina,saboda haka ta korata waje "Ki gayamin dalilinki,indai matuqar na gamsu,toba shakka a yau basai gobe ba zamu maida masa komai nashi" tofa ga qoshi ga kwanan yunwa,ta ina zata fara ya zatayi?,batason tona komai,batason kowa yaji komai,tana ganin kamar ba muhallin kowa bane ba hurumin kowa bane Kai ta kada "Daada baya sona ne,nima yanzu na daina sonshi,kinga babu amfanin aurenmu" murmushi ta saki tana kada kai "Banda abinki shahida ta yaya masoya haka siddan zasu daina son junansu?,ai ruwa baya tsami banza" cikin nuna dagiya da qarfin hali tace "Hakanan nidai daada muka daina son junanmu,don Allah karku qulla auren qiyayya" hawaye ta siraro daga idanunta muryarta ta soma rawa,saita sake murmushi tana kallonta "Shahida,anyi auren hadin da baki taba ganinsa ba bai taba ganinki ba sai hadi kuma an zauna lafiya harma yafi na soyayyar qarko,kin ganni nan gani da ran Allah?,to sanda na auri kakanku sai randa ya shiga dakina nasan shi na aura,saboda haka indai rashin soyayya ne hujjar fasa aurenki da anwar indai kikaga an fasa to la shakka mutuwa nayi bana raye,ko bana raye zanbar wasiyyar a tabbatar an daura,don anwar din ya cika dukkan siffa da kamalar da annabi yace a baiwa mutum aure" daga haka sai daadan ta miqe ta qyaleta,tashin hankalin data ji a sannan yasa taji zuciyarta ta bushe gaba daya,hawayen idanunta sun bushe tas,saita miqe itama ta shige daki tayi rub da ciki tana sakin ajiyar zuciya ko zataji sanyin tuquqin da ranta yake. Ta shafe a qalla minti talatin a haka kafin daga bisani ta janyo wayarta,ta lalubo number nuradden ta kira,bugu daya tak ya daga,ajiyar zuciya ya soma saukewa da alamu hankalinsa shima ba'a kwance yake ba,duk sai taji bacin rai ya sake shigarta,shi ya janyo komai,shine silar komai "Ka dawo ka sake neman aurena karo na biyu nuradden,bazan iya aurensa ba" ta fada kai tsaye ba tare da tayi sallama ba ko tace komai,kafin taji yace wani abu taji an karbe wayar,da sauri ta daga kai don ganin waye,daada ce,bata ce komai ba ta kara wayar a kunnenta "Nura kana jina?" Ta fadi sanda take ficewa daga dakin,saita miqe ta zauna sosai saman katifar tana bin qofar da kallo. *muna muku fatan alkhairi tare da fatan zaku gudanar da bukukuwan sallarku lafiya cikin amincin ubangiji,Allah ya karba mana ibadunmu,ya gafarta mana zunubanmu,yaji qanmu ya jiqan mamatanmu,yasa mu cikin 'yantattun bayinsa amin umma amin,ZAFAFA BIYAR na muku fatan alkhairi* *_karku manta,ku kasance da tashar SAUTIN HIKIMA TV don sauraren littattafan da zasu debe muku kewa yayin ayyukan sallah a gida* *kundin qaddarata* *daurin boye* *mutuncin mace* Duka wadanda na rubuta *fatan alkhairi a gareku* #zafafa biyar #sautin hikima tv #team anwar #team shahida #team nafisa 🏃🏾♀️ _ma'assalam_🤝🏽🤝🏽🤝🏽 _ziyarci tasharmu ta youtube don sauraren tsaffin litattafanmu dama sababbi da zamu fara dorawa nan gaba kadan in sha Allah_ https://youtu.be/H7M7h6l6wNM *Alqawarin Allah* 3️⃣1️⃣ Minti goma kyawawa daadan ta dawo,ta miqa mata wayartata tana dubanta,sannan ta miqa mata kudin da anwar ya bata tana cewa "Tunda kin zabi zubar mana da qima rahama mu zuba nida ke" daga haka ta juya ta fice,a sannan ji shahidan take kamar ta dora hannu aka tayita zunduma ihu ko xata ji sanyi cikin zuciyarta,me yasa ba zasu fahimceta su bata uzuri ba?,me yasa ba zasu haqura ba?,wai da anwar da itama wa sukafiso ne?,waye nasu a ciki?,kira ne ya sake shigowa wayarta,ta daga ta duba da sauri sai taga nuradden ne,muryarsa kadai ta gaya mata cewa ya karaya bashi da wani sauran fata "Shahida,na rasaki shahida,ta ina zan iya jurewa rashinki?,zan iya tsira daga hukunci da horon rasaki da zuciyata zata yimin?,ki tayani addu'a bansan ya zata kayamin ba" daga haka ya yanke kiran,me daada ta gayawa nuradden?,shikenan ta rabata dashi?,dole ta zauna da mutumin da sam bata ra'ayinsa ne wai?,irin wannan masoyin zata rabata dashi?,kalamansa kawai sun tabbatar da tsantsar qauna da soyayyar da yake mata,saita kifa kawai rubda ciki tana lalube da binciken meye abunyi a qwaqwalwarta,mecece mafita?duk wata dabararta ta qare,wayonta duka ya qure,daada ta yanke komai. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Qarfe bakwai da rabi ne na daren ranar,yana zaune a harabar gidan saman daya daga cikin fararen kujerun roba dake wajen,shi ya zabi zama a wajen saboda yadda iskar damina mai sanyi ke busawa gabas da yamma,hakanan qwayayen lantarkin dake harabar gidan sun haske ko ina harda korayen tsirran dake harabar wajen,sai yake jin zuciyarsa wasai,hakanan babu nauyi qunci ko wani abu da yakejin ya dameshi a yanzu,shaqar iskar yake sosai yana fesarwa har cikin huhunshi qamshin iskar da sanyinta na sake sa zuciyarsa cikin wani shauqi da walwala,fuskarsa fes take a washe. A hankali take takowa cikin gayunta,tayi kyau don ba qaramar kwalliya ta dauka ba,don yau din na daya daga cikin ranakunta na musamman,saboda bako da yaushe take samun dama irin wannan ba,ace yau anwar din yazo zance takanas saboda ita,zata iya irga sau nawa hakan ya taba faruwa a tarayyarsu,shi yasa duk ransa zaizo din ba qaramin tanadi takewa ranar ba. Gabansa ta tsaya sannan tayi sallama tana kallon yadda yayi masifar kyau cikin qananun kaya sai kace wanda ya dawo daga europe,ya daga kai yana dubanta sannan ya amsa,cikin shagwaba shigarsa da yadda yayi kyau yana dada burgeta tace "Ya bakaci komai ba dear?" Ta qarashe fada tana jan kujerar dake kallonsa ta zauna,duban tulin kayan ciye ciyen dake gabanshi yayi sannan ya kalleta,shi sam a ra'ayinsa ba mutum bane mai yawan son ciye ciye,kusan ma babu cimarshi ciki sai kadan,kafada ya daga "Karki damu,duka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96