Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 12

Chapter 12

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,330 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yanayin ba,duk yanayin rayuwa da yake ciki hakan bai hanashi bacci ba,sai gashi a karon farko saboda ita ya kasa bacci daren ranar gaba daya,duk juyin da zaiyi itace cikin ranshi. Yana biye da ita bata sani ba,baiyi mata magana ba saida suka gota wajen suka shiga wani layi "Yanzu yau kuma haramiyar ladan rakiyar za'a yimin?,wanne irin laifi nayi haka?" Cak ta tsaya,farinciki da kuma faduwar gaba na cakuduwa cikin ranta,idanunta a waje har ya iso gabanta yasa hannu ya amshi botikin,ya jera kafada da ita "Muje" ya fada cikin sassanyar muryarta da kullum take mamakin dad'in muryar da Allah ya bashi,idan yana magana dole sound dinshi yaja hankalin duk mai sauraro,yau saitakejin nauyin tafiya dashi,ta kasa yin gaba,ya sake dubanta "Waiko amsar tambayata itace a'ah akemin irin hakane" wani wal tayi da ido,saiya dafe qirjinsa da hannunsa daya "Kiyi haquri karki qarasa tarwatsamin zuciya,wannan zuciyar mai rauni ce akanki" Fuskarta ta qunshe cikin hijabinta tana dariya qasa qasa,wawiyar ajiyar zuciya ya saki "Wai Allah na,alhmdlh,ko iya haka aka tsaya na tabbatar da cewa ina da nasara...amma dai a gayamin ana sona?" Kai ta kada cike da tsananin kunyarsa,wani dan tsalle ya saka sannan yace "Alhmdlh,alhmdlh" yana rungume da hannayensa. A hankali suka ci gaba da takawa shida ita,saidai ita gaba daya nauyinsa takeji,yayin da shi kuma yake janta da hira jefi jefi,yau duk masu binsu da kallo mutanen cikin unguwarsu basu dameta ba,har sai taji ma batason su isa gida yace zai wuce. "Kina son wanda bakisan sunanshi ba hakanan bakisan waye shi ba" ya fada bayan ya miqa mata botikinta,ita sam bata damu da wayeshi ba,sonsa takeji irin wanda bata taba zata ko tsammatar akwai irinsa ba a duniya,tanajin koma wayeshi yayi mata hakan "Ni sunana muhammad anwar aminu,haifaffen kano ne kuma dan kusa da unguwarku ne ni,maraya ne ni bani da uwa bani da uba,sai 'yar uwata d'aya data ragemin anty usaina,ina karatu ne a fce kano...kefa?,shahida ko?" Murmushi ta saki tana dubanshi cikin tausayi jin cewa maraya ne,kai ta kada sannan tace "Khadija amma shahida,nice ta farko wajen umma da abbana,ina da qanne hudu,nan ne gidanmu a nan aka haifeni,ina SS 2 yanzu" kai ya kada sannan yace "Idan nazo anjima za'a barni na ganki" kai ta gyada da sauri,don tasan yadda zatawa ummanta bayani yadda zata fahimta "Shikenan zanzo anjima in sha Allahu,inason mu soma mu'amala cikin fahimtar juna gaskiya da amana...ki shiga gida lokacin islamiyya ya kusa ko?" "Na gode" ta furta cikin siririyar muryarta data dauki hankalinsa,kai kawai ya iya gyadawa ya bita da kallo harta shige. "Waye a waje kuke tsaye dashi?" Tambayar da ummanta ta soma jefo mata kenan sanda ta aje botikin tana shirin zama,kunya ta d'anji ta kamata,saita kasa amsa mata da wuri har sai data maimaita "Ba kowa umm,yadai taba rakoni gida sanda su ahmadi suka fasamin botiki,shine...shine...." Saita kasa qarasawa,murmushi kadan ummantata tayi,saboda burinta bai wuce su aurar da shahida ba da zarar ta kammala secondry schl,ita kanta tasan basa kyauta mata yadda koda yaushe suke cikin fada da juna suna sakata kuka qunci da baqinciki "Shine me?" Ta sake tambayarta tana tura mata kwanon da tayi kwadon zogale ta rage mata saboda tasan tana sonshi,sai data sadda kai sannan tace "Shine yace wai anjima zaizo idan za'a barni na fita" "Allah ya kaimu" ta fada tana miqewa don ta wanko hannunta,cikin farinciki taja kwanon ta soma cin zogalenta,wanda tana gamawa ta shige bandaki ta sake watsa ruwa saboda ranar da ake,fitowarta kenan daga bandaki dauke kwandon wanka zunnurah ta iso,tana shiryawa tace "Zunnu...akwai labari fa yau"bakin zunnnura a washe tace " ta samu kenan?"kidai muje na baki kisha,ta fada tana zura plate shoes dinta,ta dauki jakarta suka leqa suka yiwa umma sallama suka wuce. A hanya ta labartawa zunnurah komai,dariya ta dinga "Kai amma wannan gayen yayi addu'a tuquru kafin yazo,shahida da babu wanda ya isheta kallo?,da kinga wata da saurayi ma zakice wannan ai iskamci ne dududu shekarunmu nawa?,ashe harkin girma" dundu ta dumawa zunnurah "Banason iskanci qawa,wallahi nayi mamaki nima sosai,dama haka abun yake?,kinji kuwa yadda nakejinsa a raina?,har banason mu rabu,idan yana kallona wlh zunnurah ni kadai nasan me nake ji a zuciyata,ban taba tsammanin akwai wani da zanji haka a kansa ba" dariya zunnurah taketa tiqawa "Na shiga uku ni zunnu,sati daya kacal amma shine kika zare haka?,Allah yasa to nan gaba kar ya haukatamin qawa ya cuceni" "Ba komai idan ya haukataninma zunnu" ta fada tana tayata dariyar,gab da zasu shiga makarantar sukayi kacibus da fiddausi,da fara'arta take musu magana amma shahida ce kawai ta amsa suka rankaya suka shige makarantar tare. Tunda ta dawo daga islamiyya ta kasa zaune ta kasa tsaye,qiyasta da qimanta yadda haduwarsu zata kasance take,wannan ne karon farko data soma son wani a rayuwarta,kuma karon farko da zata fara tsayawa zance da wani. Tuni ummanta ta yiwa babanta bayani,bai kuma ce komai ba,illa ya kirata ya masa tambayoyi game da shi,ta bashi amsa gwargwadon abinda ta sani game dashi,yace ta kula kuma idan sun fahimci juna zaiyi magana da yaron. Ba wani kwalliya tayi ba,tadai saka kayanta masu kyau atamfa riga da skert,ta kuma yafa wadataccen mayafinta,sanda ya aiko kiranta tare da mubina suka fita,yana zaune saman yalwataccen dakalin qofar gidansu,daga soron ta tsaya tana qare masa kallo,yayi kyau sosai fiye da dazun cikin qananun kaya,iya kwanakin kadai da tayi tana ganinsa ya tabbatar da cewa shi din dan gayune kuma mutum mai son tsafta,bata taba ganin kayanshi babu guga ba,hakanan bata taba ganinsa da datti ko wani abu makamancin haka ba "Daure ki fito princess...saiki kallenin da kyau" habawa,wata iriyar kunya ta taso ta lullubeta,bata taba tsammanin yana kallonta ba,saita sake lafewa ta kasa fitowa,tashi yayi yana murmushi ya tsaya a qofar soron nasu yana kallon mubina dake gaidashi,ya amsa yana shafa kanta gami da yi mata wasu tambayoyi tana amsa masa,rabi duk a kan shahidan ne,kunya duk ta sake kamata ganin yadda mubina ba abinda ya shalleta,komai ya tambayeta gaya mishi take,saida suka gama hirarsu sannan yace "ALLAH YA TAIMAKEKI...kona koma ne yau ba za'a samu ganina ba?" Dole ta fito ta saka musu tabarma daga soron nasu,da yake yana da yalwa sosai masu wucewa ba zasu takurasu ba. Gaisheshi ta sakeyi ya amsa yana tambayarta gida kaman ba dazu suka rabu ba,cikin wani shauqi da yake fusgarsu gaba dayansu.https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *KO KUMA* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARINGπŸ™πŸ½* πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½ https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos ALQAWARIN ALLAH 08 Anwar dinne ya soma cewa"Kamar yadda kika sani na gaya miki daxun cikakken suna na sannan kuma ni maraya ne,na rasa mahaifina da mahaifiyata da qannena guda biyu duka rana guda" zaro idanu shahida tayi cike da mamaki da tausayi tana duban anwar "Eh rana daya,sanadiyyar hatsarin mota da sukayi a hanyarsu ta dawowa daga qauyenmu" "Wayyo....Allahu akhbar" ta fada fuskarta na nuna tsantsar tausayi,qwalla na cika idanunta,tausayin anwar ya kamata,rayuwa ba uwa ba uba ya zata kasance kenan? "Mu biyu muka rage a gidanmu,ni da yayata kaman yadda na gaya miki,yayata nada aure tun kafin rasuwar iyayenmu,yanzu haka tana gidan aurenta ni

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});