Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 50

Chapter 50

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,282 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mamaki take kallonshi "Katsina kuma anwar?" Kai ya gyada yana murmushi "Mamaki kikayi anty irin wannan kallo haka?" "Ai dole nayi mamaki,idan zaka katsina ba haka muka saba yi dakai ba,hasalima saina tursasaka kafin kaje,wani lokaci ma saika zabi lokaci da kanka,baka taba cemin zaka katsina haka katsaham ba sai yau,kodai wani abu ya faru acan ne kake boyemin?" Sai ta bashi dariya ganin yadda duka ta damu,har yanzu bata daina damuwa dashi da lamuransa ba "Anty na,babu wani daya faru,shikenan Allah baya shiryar da bayinsa duk sanda yaga dama,da da nake qin zuwa yanzu Allah ya shiryeni shikenan?" Kai ta kada "Allah yasa" "Yasa ma" ya amsa yana murmushi "Atamfofi ne kawai zan baka ka kaiwa innan kayan sallarsu dana saba basu,sai kuma sannu da jiki da zakace ina yiwa basira" "Gsky banjin zan samu zuwa gidansu basiran,saboda ayau nakeso na dawo" "Shikenan,mayi waya" ta fadi tana miqewa don shiga ciki ta debo masa saqon. Zuwa qarfe sha biyu na rana ya gama duk wata siyayya da yakanyi musu a sanda zaije katsinan waje kakanninsa wadda ta haifi mahaifinsa,kasancewarsu masu qaramin qarfi sosai,daya na raina ya dauki hanya,ya saki ajiyar zuciya yana qissima yadda abubuwan zasu kaya idan ya isa can.*zafafa biyar na kudine,idan kika gani don GIRMAN ALLAH karki sharing,ga mai buqatar siya zaki tuntubi wadan nan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 2️⃣5️⃣ Tafiyar awa biyu cif ta shigar dashi garin katsina,tuqi yayi lafiyayye cike da nutsuwa da kuma tunani kala kala,kai tsaye unguwar kakanninsa ya nufa. Yana qoqarin parking motarsa kawunshi modu ya fito da alama masallaci zashi saboda yadda yake dan hanzari,bai ganshi ba hakan ya sanya anwar kirayenshi,saiya waiwayo yana dubanshi cikin murmushi "Ikon Allah,yau kaine a garin da kanka?" Yana murmushi gami da kashe motar yace "Wallahi kawu,mun sameku lafiya?" "Lafiya qalau...mu shiga daga ciki" "A'ah kawu,gwara na soma yin alwalar tukunna" "To...to,shiga daga mana saika daura" "Ah ah kawi,kar naje su tsaidani mu rasa jam'i,idan mun idar ma shuga tare" daya daga cikin yaran da sukazo wucewa kawu modu ya qwalawa kira ya sashi ya shuga ciki ya debo musu ruwa a buta "Dan kuwa yau inna ta samu nayi,kazo yau zuwan ba zata sanda ba'a tsammaci ganinka ba" murmushu anwar yayi "Wallahi kawu,Allah ne ya kawo tafiyar haka"mintuna kadan yaron yafito dauke da 'yar matsakaiciyar buta,anwar ya karba suna dan taba hira da kawu madun harya gama alwalar suka rankaya zuwa masallacin. "kaine yau kuma?" Inna ta fada sanda yake qoqarin zama kan daya daga cikin kujerun dake falon,murmushi ya saki yana dubanta,sun riga da sun camfashi baisan dalili ba "Nine inna,kaman wanda bai zuwa?,kodai rikicin tsufa ya soma samunki ne kike zaton na jima sosai banzo ba?" Baki ta tabe tana rufe kwanon shan data gama shan ruwa a ciki "Idan ina rikicin tsufa na kasa lissafi ai kawunka ahmadu baiyi tsufan da zai kasa lissafi ba ko?" Dariya ta bashi sosai har sai daya danyi sannan yace "To shikenan yanzu Allah ya shiryeni,saime kuma?" Harararshi ta danyi "Allah yasa" "Amin inna" gaisheta yayi cikin mutuntawa ta amsa tana tambayarshi su anty usaina "Lafiya lau take,tana gaisheku dakyau" "Muna amsawa" daidai lokacin rashida 'yar kawu ahmadu ta shigo da kwanon abinci guda biyu,cikin girmamawa ta isa gaban anwar ta aje tana gaidashi "Duba cikin dakina ki dauko kwanon sha ki debo masa ruwan a randa idan zai iya sha" dariya ta sake bashi,ya fuskanci rikici yau take ji da gaske,saboda wancan zuwan da yayi tace ya zabi daya cikin yammatan 'yan uwa dake katsina ya hada da wdda zai aura a kano duka ya aura,yasan yau zai kashe bakin tsanya ne gaba daya shi yasa bai tada maganar ba ya barta take rikicinta "Sha kuwa harda shaye shaye...amma ba yanzu zanci abincin bane,zanje wata unguwa ne na dawo,saqonku na tsaya saukewa don na ragewa motar nauyi" duban rashida yayi dake zaune gefe tana kallonshi,ji take daman a gidansu yake "Inasu abdurrashid?" "Suna qofar gidan malam" "Maza jeki kiraminsu" da hanzari ta miqe ta fice kawu ahmadu ya sako kai hannunsa dauke da ruwan roba da lemon roba ya aje gaban anwar yana cewa "Garin yau ana zuga rana da zafi,ko rashin saukar ruwan sama ne kwana biyu ya saka haka oho?" "Ba mamaki kawu,kasan ko yaya hadari ua hadu ba ruwa sai gari ya bada zafi" daga haka kawun ya samu waje ya zauna suka shiga taba hira kan harkar noma da abinda ya shafi damina har yaran suka shigo. Cikin girmamawa suka gaidashi kowa na murnar ganinsa,ya amsa musu cikin kulawa ya dubi kawu da inna "Kawu xanje wata unguwa na dawo,Allah yasa zan sameka idan na dawo din,akwai maganar da nakeso mu tattauna" "Eh nima inason dan fita in duba shago na yau aike akemin,dalilin ma daya sanya ka ganni gida ban fita kasuwa ba kenan,amma ba jimawa zanyi ba,zan sallami yaranne na dawo" "To ma sha Allah,kafin sannan na dawo,inna zanje na dawo" "Allah ya tsare hanya" ta fada tana aje carbin hannunta sannan suka fita da yaran ya bude motarsa ya fito da duka kayan da yake nasu ne,yace sukai cikin gidan,sai daya tabbatar sun shige sannan ya tada motar ya fice daga layin. Sassanyar ajiyad zuciya ya fitar sanda yake gab da isa unguwar,qwaqwalwarsa na masa bitar abinda xaije ya aiwatar din,jiki da zuciyarsa tana gaya masa abinda zaiyi din shine dai dai,a nutse ya kutsa motar cikin layin,bai tsaya ba sai daya rage daura gida daya ya isa qofar gidan sannan ya kashe motar,zamansa yayi ciki yana tunanin ta yadda zai soma shiga gidan,daada zata ganeshi kuwa?,zata karbi zancansa?,zata yarda da qudurinsa?. Idonsa ya bude sosai sanda yaga saurayin daya saba aike zuwa gidan lokaci xuwa lokaci ya leqo ya koma da sauru,addu'a yake Allah yasa ya sake fitowa. Da hanzari sulaiman ya koma zuwa cikin gida da sauri yana kiran "Daada,daada" dattijuwar da ake kira da daadan wadda ke zaune cikin rumfarta tana daura busashshiyar kubewa ta daga kai kawai tana kallonshi har ya iso rumfar tata "Haba sule,wannan wacce iriyar dabi'ar banza ce haka?" "Daada wallahi saurayin nan da yake bani saqo lokaci lokaci nake kawo miki wanda kikace bakisan waye ba kema shi na gani a tsaye a qofar gida,kince duk randa ya sake zuwa na tsaidamiki shi shi yasa nake sauri na gaya miki kar yana bada saqon ya tafi" "Miqo min mayafina....duk abinda ya baka kada ka amsa kace masa lallai lallai ya shigo inason ganinsa" "To" sulaiman ya fada yana bata mayafin sannan ya sake fitowa da hanzari. A nutse yake nufo motar anwar,wanda shima ganinsa yasanshi sauke glass dinsa har sanda sulaiman din ya qaraso bakin window bakinsa a washe,anwar ya miqa masa hannu kaman yadda suka saba,yana Murmushi sulaiman ya miqa masa hannu sukayi musabaha,yana bala'in son musabaha da anwar din,koba komai zai gogi qamshinsa dake burgeshi yaji laushin fata sannan kuma hannunsa ya shaqi sanyin acn dake cikin motar kamar yadda sulaiman din ke cewa "Kwana biyu yallabai?" Sulaiman ya fada yana sosa kai,murmushi anwar din yayi sannan yace "Ko zaka yimin iso gurin mutanen gidan?" "Me zai hana?,dama daadan nason ganinka,ta roqeni ma kan don girman Allah yaudai ka shigo taga me mata aiken nan" murmushi ya kuma saki yana cire belt

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});