Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 45

Chapter 45

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,306 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

murfin ta rufe ta daga masa hannu "Allah ya kiyaye" shima hannu yadan daga mata,har zai tada motar tayi hanzarin tsaidashi "Sorry...don Allah ka yimin alfarma mana" "Allah yasa batafi qarfina ba" murmushi tayi "Bata fiba,saidai idan ba za'a min ba" dan qaramin murmushi yayi "Fadi muji"sai data danyi shuru na sakanni sannan tace "Kamfani triple R Gem nakeso ka rakani don Allah" shuru yayi yana dubanta "Me zakiyi a can" hannu ta yarfar "Kai ya anwar,da banso gaya maka ba Allah,amma..." "A'ah,riqe cikinki" yayi maganar sanda ya tada motar,da sauri ta zaburo "Bafa wani abu bane,wasu sarqoqi nakeson saya a can" kallonta kawai yake,burin nafisa yayi girma da yawa,duk sarqoqin garin nan amma sai taje har triple R ta saya?,iya saninshi wajene dake da babu abun qaramin kudi a can,dutse ne masu daraja da tsada suke sarrfasu,wanda ba kowa ke iya siyan abun kwalliya ba acan,bayason ya fiya gwasaleta har taji kaman ya tozartata,sai ya gyada kai "Alright..amma gaskiya bani da lokaci cikin satin nan gaba daya,saidai ko zuwa next week" "Well,yayi indai zaka rakani din" da haka sukayi sallama ya fice daga gidan yabarta tsaye awajen sonshi na shawagi da ita,sai kuma ta tuna yau akwai partyn da zata saboda haka da sauri ta juya zuwa cikin gida. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Qarfe biyar ta fito daga kamfanin kaman yadda qa'idar lokacin tashinsu yake,saidai gaba daya hankalinta ba'a kwance yake ba saboda baqin hadarin daya hado yake kwance a sama yana shirin zub da ruwa. Kusan mutum uku ne sukayi mata tayin sauketa a gida amma ta doje don kare mutunci da qimarta,ciki harda alhajin dake nacinta wanda ta lallaba ta fito abinta ta baroshi a office din rayyan mai kamfanin gaba daya suna lissafin wasu sarqoqi da sukayi masa,haka ta fito cikin ranta tana addu'a Allah yasa ta isa gida lafiya qalau. Titin babu wadatar motoci sai jifa jifa,ko dama can titin bashi da wadatar wucewar ababen hawa musamman ma na haya,yawanci saina gida,hakan ya sanya ta ku sa kashe minti goma tsaye ba tare da taga gilmawar wani abun hawa na haya ba,cikin abinda bai gaza minti biyar ba hadarin ya taso sosai,iska ta shiga kadawa ko ina sama ta sake duhu,fargabarta ta dadu,ta runtse ido tana jin saukar ruwan saman bisa fuskarta,Allah dai yayi saiya daketa. A hankali yake tuqin saboda yanayin ruwan dake sauka din,uwa uba yanajin kaman yayita shawagi saman titi ba tare daya koma gida ba,yakan kasance cikin kewa da kadaici duk sanda ruwan sama irin haka ke zuba yana cikin gidan shi daya,yakan tuna masa wata hira da suka tabayi da uta,duk da yadda yakeson bunne komai nata amma duk lokacin da ake ruwan sama kaman haka sai hirar ta fado masa "Nafison damina akan kowanne yanayi,tana saka nishadi cikin zuciya,komai yana wankewa yayi fes,tsirrai zaka ga sunyi kyau ya anwar sunyi kore shar,kosu kasan suna farinciki da zuwanta,qamshin qasa iska mai dadin da babu kamarta" tayi maganar ne idanunta na alumshe,saita budesu tar cikin nashi a lokacin da ya zuba mata ido yana tayata murmushin da takeyi na tuna yanayin da tayi "Kasan me yaya anwar?" Ta tambayeshi wanda bata kai ga fadin abinda takeson fada din ba kiran nafisa a sannan ya katsesu,dai dai sanda shima nashi tunanin ya katse yana hango tsaiwar wata matashiya cikin ruwan saman da har hazo hazo yake,tsurawa wajen ido yayi yana ci gaba da tuqin a mugun slow kai kace motar na dab da mutuwa ne,baikai ga qarasawa ba wata farar mota ta yanko daga layin da yake kusa da ita,dab da ita ta tsaya na cikin motar ya fito riqe da lema ya iso gabanta ya matsar da lemar zuwa kanta da alamu magana yake mata,idanu ya runtse yana tsaida motar duk da a tsakiyar titi yake,idanunsa qur akansu,alokaci shahida ta sake ja baya "Ka wuce kawai,bani da damuwa nasan ko ban samu mota yanzu ba ruwan daya tsagaita zan samu" "Haba yallabiya,ke kuwa yau dai kawai,uzuri ne fa,kiga yadda ruwa ke dukanki ke daya atsaye anan,uwa uba tsaiwarki a titi irin wannan lokacin hatsarine ga rayuwarki"kai ta girgixa "ba komai Allah zai kareni" "Duk da haka amma kiyi...." Ta gaji dajin kalaman bakinsa,saboda haka kaman adan hasale tace "Don qaunarka da mahaliccinka kayi tafiyarka" ya fuskanci kaman tanason hasala ne don haka yace "Allah ya baki haquri,naji zan tafi,amma kema don qaunarki da mahaliccinki ki karbi wannan lemar" batason dogon zance saboda haka tasa hannu ta amsa,ya koma ya shiga motar ya tasheta ya wuce,ajiyar zuciya ya saki ganin tafiyarsa,duk da haka saiya kasa tafiya yaci gaba da tsaiwa kaman me gadinta. Ganin ruwan yadan fara sauqi saita soma takawa don canza wani titin ko zata dace,shima saiya tashi motar yaci gaba da binta sannu sannu,yana kallon yadda take digar ruwa har cikin zuciyarsa,saidai bazai iya daukarta amotarsa ba,yanajin wani abu cikin zuciyarsa,kallonta na tuna masa da ganinta da yayi,fitowarta daga motar wani,wanda ba qaramin suya yake masa a qirjinsa ba. *ga mai buqatar littafina da zan fara bayan gama alqawarin Allah,zaije youtube yayi searching SAUTIN HIKIMA,daga qasa zaiga an rubuta SUBSCRIBE da jan rubutu,ya danna sau daya zai koma black,yayi screen shoot ya tiro zuwa wannan number,za'ayi adding dinsa agroup din in sha Allah* 07038670166 *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani don girman Allah karki sharing,idan kina da buqata ki tuntubi wadan nan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 2️⃣3️⃣ Gab da zata tsallaka daya titin mai adaidaita ya taho,ta tsaidashi da sauri,babu kowa a ciki ta gaya masa inda zata ya dauketa suka wuce,sai da yaga tashinsu sannan ya saki ajiyar zuciya "Wai anwar meye damuwarka ne haka?" Wani sashe na zuciyarsa ya jeho masa tambaya,sai a sannan ya dinga tuno abinda ke faruwa,sam duka baisan yana abinda yayin ba,kamar wani umarni yaji ana bashi,kai ya girgiza yana jin haushin kansa,yana ganin ya tsaya ne kawai ya bata lokacinsa,motar ya bawa wuta sosai cikin gudu ya figeta ya harba titi. Su duka suna zaune a falon suna kallo,da sallama ta shiga,dukkansu sannu da zuwa suke mata,anty zubaida na cewa "Wai wai,sannu rahamatullah" murmushi tayi tana zuge lemar hannunta,huda ta tashi da hanzari zata tarbeta ta dakatar da ita "Tsaya huda karki jiqe,don ni da kika ganni yau jalaf nake a kaina ruwan yau ya qare" tayi maganar sanda take aje jakarta "Ahto...haka kawai za'a baki mota kika qi,da kinga yanzu ba ruwanki da ruwa ko rana" "Wallahi anty to ya za'ayi....faruqu don Allah zazzagemin jakarnan ka duban wayata ka shanyan abinda kaga ya jiqe" da sauri huda ta amshe cikin shagwaba "Anty gani sai kice ya faruq kuma?"hararta faruq yayi "To kishiyata" Dariya shahida tayi "Auto auta yi haquri,gyaramin bari naje na sauya kayan jikina sanyi sanyi nakeji" "Idan kin saukoma ga dinkunanki nan an kawo" waiwayowa tayi "Yauwa,yaushe ya kawo?,jiya fa mukayi waya dashi yace bai gama ba" "Dazu ya kawo" "Ya kyauta,don kayan matar data bani aron style nakeson maida mata,kar taga rashin hankalina...bari naje na dawo saina gani" "Uhmmm" anty zubaida ta fada. Sai data soma kunna qwan dakin data kashe dazun da zata fita aiki,haske ya gauraye ko ina,ko.ina tsaf yana fitar da qamshi kaman yadda ta saba masa,ta kalli agogo,shida harda rabi na yamma,an kusa kiran magariba kenan,kayan jikinta ta fitar ta shiga bandaki

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});