Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,311 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

data shiga dakinta tana dubawa abun ya sake burgeta,duk da anwar ba wani mai hali bane amma Allah ya hore masa tsari da iya siyayya,komai daya bata ya burgeta,ta jima tana kallon wani zobe,duk dana azurfane amma an qawatashi qwarai dole ya burgeka,zanen heart ne a jiki amma heart din rabi ne,murmushi ta saki tana sakashi cikin yatsunta,yayi masifar yi mata kyau,saita tattara kayan ta kaiwa ummanta wanda ita kanta ta yaba da qoqarinsa kaman yadda abbanta ya yaba,hakan ya mata dadi qwarai,ya kuma bata tabbacin kenan bata da matsala bata da wani shamaki da zai hanata mallakar anwar,tuna haka cikin jin dadi ya sanyata qanqame filon da take kai tana hango kanta da anwar dinta a matsayin ango da amarya qarqashin inuwa guda. Cikin farinciki da walwala ta gabatar da walimarta,komai ya tafi lpy ya kuna qayatar sai jiran sakamako,a sannan komai na tafiyar mata lpy,rayuwar tana hangen nan gaba kadan zata yi mata kyau,komai zai qarasa dai daita musu,anwar ma an masa qarin albashi wanda hakan dukka su biyun ya musu dadi. *SANADIYYA* Ana tsaka da haka gagarumin tashin hankali da yayi sanadiyyar lalacewa komai,ya zama silar tabuwar rayuwar mutane da dama,yayi sanadin wargajewar wannan iyali,ya kuma silar tarwatsa rayuwar shahidan...ya zama wani sanadi na dasa baqinciki mai tarin daci da zafi a rayuwarta ta faru. Rayuwa tsakanin mahaifinta da mahaifiyarta rayuwa ce ta rashin haquri,dauke kai yafiya da juriya da akasan dukkan ma'aurata da yiwa junansu,fada gaban yaransu wannan ba wani sabon abu bane tun tasowar shahidan,wanda hakan ya sanya bayan girmanta abun ya zame mata wani ciwo da duk sanda ya taso mata yake mata zafi da quna a zuciya,dukkan wani mataki da take ganin ya dace ta dauka a matsayinta na diya mai qarancin iko da abun fada ta dauka harma wanda ya zarta huruminta amma babu abinda ya sauya,duk da alqawari da qoqarin sauyawar da suke. Kwatsam dare guda mahaifinta ya jijjigo maganar qarin aure suna tsaka da rayuwarsu cikin rufin asirin Allah,wanda hakan ya sanya mahaifiyarta tayi tsalle ta dire tace batasan wannan zance ba,dalilin daya janyo tashin tashina da fadan da bata taba gani ya wanzu tsakaninsu ba,hakan ya sanya walwalarta da duk wani kuzari nata ya ragu,anwar ne mutum na farko dayafu kusanci da ita a sannan shiya soma gane tana cikin damuww,amma baisan dalili ba,taqi kuma sanar masa,ta yaya zata gaya masa wannan murdaddeb zance?,tun baya baisan halin da gidan nasu ke ciki ba saboda kare martaba da qimar iyayenta,duk sanda ta fuskanci akwai rashin jituwa tsakanin iyayen nata bata taba yin zance a gidansu,a gidan anty amina take zancanta,toko yanzu ma da lamarin gidan nasu ya lalace can take tafiya ya sameta anan,don ba zataso wataran wani mummunan abun ya faru a gabansa ba duk da yana musu kallon iyayensa amma asirin ciki sai hanji. *MAFARI* Cikin tashin hankalin da bata taba tsintar kanta a ciki ba ta fito daga gidan nasu tana hawaye,yau a gidansu a gaban idanunta ake doki in doka tsakanin ummanta da abbanta?,wanne irin iyaye gareta?,ya ilahi ji take kaman zuciyarta zata fashe,ji takae bugawa zuciyarta zatayi,ita kadai tasan yadda takeji tana jin kaman zuciyarta ta kumbura ne ta cika qirjinta,zataso ace zunnurah na nan saidai ina,gidan anty amina takeson zuwa amma babu ko nutsuwar daukan kudin mota a wajenta,ba tare da tuna nisa da tazarar dake tsakaninsu ba ta hau tafiya cikin fitar hayyaci da tashin hanakali bacin rai da baqinciki. Dawowarta kenan daga inda taje ta sauka a abun hawa,tana yunqurjn shigowa layin nasu ta hangi kaman shahidan,tayi mamaki don shahidan bata taba zuwa gidansu ba,hakanan bata yowa layinsu don asalan ita bamai yawo bace,sauri ta qara donta cimmata,sai taga itace dince kuwa,amma a binda ya bata mamaki hawayen data gani shabe shabe a i fuskarta,hannu tasa ta kamota tana cewa "Shahida,meye haka kuka kike fa akan hanya" sai a sannan ta kula da fiddausin,sake fashewa da kukan tayi,ita koma waye ta gani zata iya fada masa abinda ke damunta ko zataji sassauci a zuciyarta,abun ya mata yawa,wannan damuwar bata shekara daya bace ko biyu,ganin haka sai fiddausin ta janye shahidan zuwa gidansu,ta tura gate din gidan suka shige sannan suka nufi dakinta ta qofar baya,sau tari takan iya shigowa ba tare da an sani ba saboda gidan nada girma babu laifi. Kuka take sosai tana cewa "Na gaji fiddausi....na gaji da wannan bacin ran,ina zanje naji dadi,me zanyi na samu sassauci?" Murmushi fiddausin ta saki,duk da shahidan bata gaya mata damuwarta ba amma tana ganin sara ne yazo kan gaba "Ina da maganin damuwa shahida,maganin da zai dauke duk wata damuwa da kike ciki komai qarfi da girmanta,zaki jiki fresh kaman yau aka haifeki,nauyi da zuciyarki keji ya sauka kaman bai taba faruwa ba" idanunta dake jiqe da hawaye ta daga tana kallon fiddausi "Don girman Allah ki bani kona daina jin suyar da qirjina yakemin" "Kwantar da hankalinki basai kin hadani da girman Allah ba" ta fada tana zuge jakar data shigo da ita,kwalabe ta fito dasu ta hada abubuwan ciki ta gauraya sannan ta miqawa shahida "Daga kanki ki shanye nina daga wajen likita nake shi ya rubutamin shi yace maganin damuwa ne" ba tare da kowanne tunani yazo kanta ba,ba tare da tayi lissafin komai ba,ba tare da ta jinkirta ba ta daga kai ta shanye duka din kamar yadda fiddausin tace mata,cikin wasu qananun mintina ta soma jin dummm,ta soma ji kamar ana sauyata daga tata duniyar zuwa wata daban,ta soma daina gane komai,take a nan ta zube saman gadon fiddausin,lokaci qanqani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita,dariya fiddausin ta saki tana rufe kwalabenta tare da maidasu haka tana cewa "WASA FARIN GIRKI YARINYA". *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videoshttps://youtu.be/T9a10h1Apqs 👆🏽👆🏽👆🏽👆🏽👆🏽👆🏽👆🏽 *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani DON GIRMAN ALLAH karki sharing,idan kina da buqata ki tuntubi wadan nan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 1️⃣2️⃣ A hankali ta farka tana mutstsuka idanunta da taji sun mata nauyi,sam ta mance inda take saida tayi dan tunani sannan ta tuna,da hanzari ta tashi ta zauna ganin gari yayi duhu sabanin sanda suka shigo gidan akwai hasken rana,agogon bango ta kalla sai taga qarfe takwas,hakan yana nuna kenan ta rasa sallar la'asar magariba dama isha'i. Da hanzari tayi nufin tashi saidai gaba daya jikinta a mace yake babu qwari,daidai lokacin da fiddausi ta shigo dakin dauke da plate din abinci,cikin murmushi take duban shahida "Sannu kin tashi?,ya kike jin kanki yanzu fresh ko?" Eh to,lokacin da tayi baccin ta mance komai,saidai yanzu bayan ta farka komai ya sake dawo mata,saidai baccin da tayi din ya rage mata bacin rai kadan,amma duka ba wannan ba,sallolin data rasa lokacin da take bacci su sukafi damunta,saboda haka tace "Banyi sallah uku ba fiddausi,nunan bandaki na daura alwala"ta fada tana jin babu dadi har cikin ranta,wannan wanne irin bacci ne?,bata taba irinsa ba,hakanan koda bata da lafiya bata taba hada salloli ba. Qofa ta nuna mata wadda take cikin dakin gadon nata,nan shahida ta shiga ta daura alwala,ta fito

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});