Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 39

Chapter 39

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,302 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

me nayi maka?,me yasa kakeson sanya zuciyata cikin rudani,kasan ya nake ji duk sanda na kiraka baka daga ba,ko na turo maka saqo baka karanta ko ka turamin reply ba?" Idanunshi ya daga ya dubeta sai ya sake kautar dasu yaci gaba da abinda yake,tunu qwalla ta cika mata idanu,ta tsani wannan miskilancin nashi ya motsa,wahala takesha,tana ji a ranta duk sanda ya soma shariya irin hakan kaman dai ya tuna tsinanniyar yarinyar da yanzu tsanarta ta ninku a zuciyarta wato shahida,data sani baya ga rabasun da tayi ta nakastata yadda ko da wasa ma bazai sake kawota cikin zuciyarsa ba,amma data taba masa zancan ya tunata ne ranar taqa zallar bacin rai,ya gaya mata karta sake mishi wannan zancan don ba huruminta bane,sannan kuma karta sake masa maganar wata shahida,abinda ma yasaka ranta ya danyi sanyi kenan,ta cika da fatan Allah yasa tabar ranshi kenan har abada. "Meye laifina dear..." Ta fada cikin son fashewa da kuka,saiya tattara dukkan abinda yake gefe guda ya rufe system din sannan ya daga kai yana dubanta duba na kai tsaye,yana fata Allah ya yaye mata wannan son da take masa,sam ko kadan shi hakan baya masa dadi "Ni na aikeki kona bada daman ki bada sanarwar engage dinmu rana ita yau?" Kai ta girgiza tana dubanshi hawaye na sake cika idanunta "Wannan wacce irin banzar dabi'a ce,mu yahudawa ne nafisa?" Nan ma kai ta gyada saidai cikin ranta tana jin dadi da sauqin radadin da take ji,ta zaci wani babban laifi ne ta aikata,koya ganta ne ranan nan da saddam randa sukaje dinner din abokinsu,wanda basu dawo ba sai sha biyu da rabi na dare,ita a ganinta wannan sam ba laifi ne ba,hasalima saika isa ka qasaita ka amsa sunanka wani sannan za'a ga wani abu daya shafi event dinku a gidan talabijin din "Kayi haquri,kuskure ne,bani na biya bama siyama ce tace lallai a saka" "Siyama....ita tace rana ita yau din kiyi wani bikin engage namu kenan?,ohk tunda haka ne rana ita yau din ita saita tabbatar da abun kota tursasani" ya qarashe fada yana janyo wayarshi dake gefe,da sauri ta riqe hannun nashi don tafison a kawo qarshen komai,bata jurewa fushinsa,jinsa take har zuciyarta,kallonta da yayi ya sanyata saurin janye hannun nata,yasha mata kashedin tabashi ba sau daya ba ba sau biyu ba "Don Allah dear don Allah,wallahi na fasa ba za'a yi ba" yana da tausayin mace hakanan mutum ne shi da tun asali yake tausaya raunin 'ya mace ko wacece "Kome mutum xaiyi ya kamata ya dinga duba da abinda bai sabawa addini da al'adarsa ba,sannan ka dinga dogon nazari da tsinkaye a duk lamarinka kafin aiwatar dashi" "Kayi haquri" "Ya wuce" ya fada a taqaice "Yanzu daga ina kike?" Kame kame ta soma yi,don tun dazun suka fito gantali ita dasu mima,yanzu haka suna cikin mota su suka rakota bashi haquri,ko hajiya bilkisu ma batasan tazo ba,ganin ta rasa qwaqwqwaran abun fada guda daya ya dakatar da ita "Is ok...yanzu ki wuce gida" "To yaushe xakazo?,kwana biyu ma gaba daya ka daina zuwa ko cin abinci,mama nata complain" ta fada cikin shagwaba "Zanzo da zarar na samu dama" "Can i call you anjima?" Ta sake tambaya,idanunsa ya lumshe kana ya bude,don maganar ta soma isarsa "Allah ya kaimu anjima" miqewa tayi ta masa sallama cikin salon nuna qauna sannan ta juya ta fice daga gidan,ajiyar zuciya ya sauke sanda yaji fitarta,saiya hada kayanshi gaba daya don zaman gun har ya fita akanshi kuma. Bacci ya samu yadanyi,qarfe hudu ya tashi,yayi alwala ya fice masallaci,daya dawo ya shiga wanka ya shirya tsaf cikin dogayen kaya wanda bai fiya sakasu ba,ya dauki wayoyinshi da maqullin motarsa ya fice,ya yiwa mai gadin sallama ya wuce. Tafiyar mintuna qalilan ta sadashi da gidan anty usaina,suka gaisa sosai da mai gadin qofar da yake shiga,saidai qofar ana gyaranta ne saboda gate din yana masa tauri bai buduwa da sauri,tilas yayi rivers ba don son ranshi ba ya zagaya ta daya layin. Idanunshi fes yana iya hangen qofar gidan daga qofar gidan anty usainar,a hankali ya dauke kanshi yana fidda zazzafar iska daga bakinsa,horn daya yayi aka bude masa don tuni ya zagayo mai gadin,ya saka motar tashi yayi parking sannan ya kasheta ya fito. Anty usainan ya tadda da yaran ta zaune cikin valcony din dake gefan matattakala hudun da zata sadaka da babban falon gidan,assigment sukeyi,dukansu suka hada baki suna masa sannu da zuwa cikin girmamawa ya amsa,har ta miqe zasu shiga ciki taga yana zare sau cikinsa "Barni daga nan anty na zauna cikinsu nima,sati biyu kenan bamu hadu ba" da d'aya da d'aya ya dinga bibiyar karatunsu,yammata masu kimanin shekara sha hudu sha biyar da sha shida,sai namiji mai shekara sha uku,yaji dadin yadda yadda ya samu karatun nasu na tafiya daidai,wansa daga qarshe ya sallamesu da kyautar dari biyar biyar suka shige cikin gida suna murna,wajen ya rage daga shi sai anty usainar. "ya jikin naka?"anty usainar ta tambayeshi bayan sun gama gaisawa,dubanta yayi "Waye yace bani da lafiya?"gajeran murmushi ta saki "kana tunanin zaka iya boyemin ne,tun zuwan da kayi cikin wancan satin nasan baka jin dadi" "Don dai karkice na musa miki ne...amma da nace lafiyata qalau,kawai stress ne na wajen aiki" kai ta kada kawai,tasan dama bazai taba yarda ba,baisan tsohon abu bane wannan a wajenta,ta karanceshi ciki da bai "Hakane....Allah ya taimaka to" "Amin" ya amsa yana ciro wayarsa da tayi qara alamun shigowar saqo,nafisa ce,ya karanta ya maida mata da thanks sannan ya maida wayar idonsa kan anty usainan "Dama inason muyi wata magana ce da kai" "Toh anty,Allah yasa ta samu" "Eh to.....zancan nafisa,munyi magana da ita ta sanarmin kace rana ita yau kakesan suje su sami alhj abba,amma saga bangarenka banji kace komai ba har yanzu,ya kamata fa anwar ka maida hankalinka jikinka,da da yanzu ba daya bane,kullum shekaru qara yawa suke akan mutum,baya ga haka ma ya kamata mu fita kunyar yarinyar nan da iyayenta" shuru yayi yana saurarenra idanunsa na kallon carfet din da suke kai,har sai data kammala sannan ya dubeta cikin nutsuwa da jeranta kalamai "Anty,har yanzu banji nutsuwa da gamsuwar nafisa ta zama mata agareni ba,har yanzu ina qoqari da tsarawa kaina yadda zan amshetq,bana son ayi abinda daga qarshe zai xama wani batu na daban,ina matuqar ganin qimar mama da abbanta,ina ganin mubi komai a sannu har zuwa sanda komai zai dai daita,zuciyata ta amshi abun dari bisa dari yadda ya dace"fuska anty usaina ta canza,har cikin ranta tana jin anwar din zai aikata ba dai dai bane kawai "Anwar,idan ka sauya ra'ayi ne kawai ka furta,har xuwa yaushe kakeson yarinyar tayita zaman jiranka?,tun tana kara har takai ga tana takowa ta sameni da maganar,waishin ma idan bakayi aure ba yanzu sai yaushe xakayi anwar?" Ta jefa masa tambayar tana tsareshi da idanu "Duka anty ba wannan maganar bace" "To wacce ce gaya min?" "Kamar yadda na gaya miki ne a baya,har yanzu zuciyata ta kasa nutsuwa da yadda da soyayyar kowacce yarinya,da nafisa zata haqura dani da nafi kowa murna,saboda zanso mata ta auri wanda yake sonta ba wanda takeso ba" "Maganata ta tabbata kenan,kawai anwar ka fasa auren nafisa kakeson cewa,ka shirya butulci wa mahaifanta" cikin bacin rai ta qarashe maganar "Banason ranki

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});