Chapter 54
Chapter 54
waye daya sanka yadda kaqi jinin zuwa katsina dole yayi mamakin tafiyar taka" "Neman aure naje,na nema kuma sun bani" saita dakata da abinda take tana kallonshi sosai,saidai bata ga alamun wasa tattare dashi ba,hakan ya sanya ta gyara zamanta "Auren wa kuma anwar" "Shahida" ya fada kai tsaye kuma a taqaice,wani abu taji ya tsarga mata gaba daya ilahirin jikinta,saita aje rezar gefanta ta zauna sosai tana kallon anwar,tana jin wani farinciki na ratsata,da gaske ko mafarki take,shahidan da take tayi masa farautarta?,sun shirya kansu ne koko yaya abun ya faru?abinda ya shiga tsakaninsun dama baiyi girman da zasu kasa daidaita tsakaninsu ba amma har ya zama silar rabuwarsu na tsahon shekaru?,ya zama silar lalacewar soyayyar da kowa yake sha'awa,duka cikin lokaci kadan ya karanci tarin tambayoyin dake yawo a idanunta,qaramin murmushi yayi yana jin wani ciwo cikin ranshi,inama ace yadda kowa ya kalli lamarin hakan yake "Karki damu anty,na rage miki aikin da kiketa yunqurin yine" ya qarasa fada yana son ganin yanayin fuskarta,ajiyar zuciya ta sauke ta zauna sosai zaman dake nuna ta soma samun nutsuwa "Zuciyata ta kasa karbar rabuwarka da ita ne anwar,inaji a jikina bai cancanci ku rabu ba" "Shikenan ai....yanzu dai anty abinda nakeso kici gaba da zama a yadda ta sanki har zuwa lokacin da komai zai daidaita" sai yanayin fuskarta ya sauya "Komai zai daidaita kamar yaya?,kana nufin baku daidaita ba ka nemi aurenta a haka?" Kai ya gyada mata "Eh kusan hakanne" "Me hakan ke nufi anwar?" "Babu komai,kema hakan kikeso mu kasance tare fa?" Eh...amma zanso ace hakan ta faru ne a lokacin da duk wani sabani dakw tsakaninku ya zama babu shi" "Karki damu anty" shuru tayi tana nazari,yayin da zuciyarta taji ta mata sanyi sosao,ta dinga jin farinciki na shigarta,tana ji babu shakka abune mawuyaci anwar ya samu soyayya irinta shahidan,abune mai wahalar gaske yaso wata kwatankwacin nata son koda shi yana qaryata hakan tasan wani dalili ne nashi na daban daya rufe masa idanu har yake qaryata hakan "Nafisa fa?" Ta sako mishi zancan da take ganin kamar ya manta ne "Ba abinda ya sauya tsakanina da ita" "Tasan da wannan maganar?" "Zata sani anty,zata sani idan lokacin daya dace ta sani yayi" "Shikenan,Allah ya shige gaba ya kauda dukkan abunqi"mai makon ya amsa saiya soko wani zancan "cikin satin nan ne tafiyata,ina ganin ki lissafa duk abinda kuke da buqata don bazan dawo ba saina gama wata biyun gaba daya,aiki ne mai muhimmanci a gabana" "Babu wata matsala,don bana tunanin zamu buqaci komai harka dawo din" 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Ranar juma'a qarfe biyu na rana suma gama shirin tafiya katsina,ga mamakinta sai uncle hisham ya hadasu ita da haidar da faruqu,ganin haka huda itama ta turje saita je,hakan yasa ta hada kayanta duka suka bar gidan sai anty zubaida kawai. Tafiyar tayi mata dadi sosai saboda su faruq,har Allah Allah ta dinga yi su isa,basu jima sosai saman hanya ba suka isa katsina. Sosai daada tayi farincikin ganinsu su duka,ta rasa inda zata sanyasu,kowannensu haba haba takeyi dashi,saida suka ci suka sha suka nutsu qarfe uku na yammaci,a lokacin su faruqu sun fita kewaya 'yan uwa dake nesa,shahida tace ta gaji ba zata iya fita ba sai gobe,jin haka yasanya huda itama cewa bazata bisu,nan tayi kwanciyarta saman cinyar daada suna hira abinsu. Duban shahida daadan tayi bayan ta maida nutsuwarta sosai "Rahama" ta kirayi ainihin sunanta,saita daga kai daga danna wayar da take ta dubi daada "Yau kuma sunan nawa kike sha'awar kira" maimakon ta maida mata yadda suka saba sai tace "Maida hankalinki jikinki ki aje wannan wayar" jin hakan yasa ta sauke wayar saman cinyarta tana kallon daadan "Abinda yasa nace a turomin ke,inason gaya miki cewa mun bada ke kuma mun karbi kudin aurenki" *KIYI SUBSCRIBING,KI TURA WANNAN NUMBER DON SAMUN DAMAR SHIGA GROUP DIN SABON LITTAFINA DA ZAN SOMA RUBUTAWA BAYAN ALQAWARIN ALLAH IN SHA ALLAH* 07038670166 SAUTIN HIKIMA https://youtu.be/H7M7h6l6wNM *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani don GIRMAN ALLAH karki sharing,ga mai buqata zata tuntubi wadan nan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 2️⃣7️⃣ Murmushi shahida tayi tana kada kai "Haba tsohuwa,wai gajiyar da kukayi dani yasa har kin soma min irin wannan wasan?,toki kwantar da hankalinki idan ma bugun cikina kike,ana gama azumi aka sallace zan kawomiki dandasheshen angona" "Ni banga miji ba kamar anwar" daada ta fada cikin ranta,amma a sarari saita sake hade fuskarta sosai,ta yadda shahidan zata fuskanci bada wasa take mata ba "Ki dakatar dashi,don hatta sadakinki yana hannu,kuma watanni uku ya rage daurin aurenki" cak ta tsaya ta nutsu sosai tana son karantar maganar daadan,ta fidda gaskiyar dake cikin maganar "Sadakina fa daada kike cewa kun karba?" "Idan baki yarda ba tunda ni sa'ar wasanki ce,saiki jirayi wadanda kike yadda da nasu zancan anjima suzo su shaida miki" tana kaiwa nan ta yunqura ta miqe ta nufi qofar fita,hakan yasa shahida ta miqe zumbur cikin tashin hankali harta manta da wayarta dake seaman cinya ta cimma dadan ta ruqo hannunta,muryarta na rawa tace "Daada....wa kuka baiwa ni?,nidai nasan ba wanda na bawa dama,da nura mukayi magana shi kuma sai bayan sallah mukayi dashi zaizo" juyowa tayi ta kalleta "Mai rabo muka bawa,zama zamuyi mu zuba miki ido sai sanda kika ga damar aure sannan kiyi?,to sakalcina baikai nan ba...idan zaki nutsu ki fahimceni ki nutsu idan ba zaki nutsu ba kuma kici gaba da shiriritar saina qyaleki cikin duhu" dakiya da dukkan juriya ta gayyato,ta soma kokawar maida qwalla da abinda ya tare mata maqoshi tana cewa "Na nutsu,ki gayamin don Allah" komawa tayi ta zauna inda ta tashi,itama shahidan ta koma ta zauna idanunta qyarr kan daadan,kamar ta fiddo zuciyar daadan ta karanta komai haka takeji "Yazo yana neman aurenki,dan mutunci ne yaro da mai mutunci kirki da karamci,bashi da wani aibu ko abun qi,hakan ha sanya ya turo magabatansa,kawunki ummaru ya sanshi kawun nashi gaba da baya,hakanan muma din akwai wata 'yar alaqa tsakaninmu duk da bamai qarfi bace,babu wata matsala hakan yasa aka amshi harda sadakinsa,karki damu karki daga hankalinki zaki sanshi zaizo ya sameki kuga juna,ke kanki kinsan shekarunki a yanzu sun isa ace kina gidanki harda albarkar zuri'a ma,idan baki aure ba shahida yanzu sai yaushe?" Kuka ta fashe sosai dashi,don tana ganin itace hanya guda daya da zata iya samun mafita da ita "Don shekaruna sun soma tafiya wanda har yau basu rufa ashirin da biyar ba kawai daada saiku amshi kudin aure harda sadakin wanda ban sanshi ba?,bansan daga inda yake ba?,bani na turoshi ba?,ba soyayya ko sabo tsakaninmu?,wallahi wannan zubarmin da mutunci kawai da ajina kukayi" ta qarashe cikin kuka wanda yasa huda ta tsaya sak tana kallon shahidan,daquwa daada ta watsa mata "Kinci qaniyarki,makaranta muka zubar miki ba aji ba,wanne aji kike nema bayan na gidan aure?,ba gata muka yi miki ba?" Haushi ya ciyota,saita sake saka kuka "Wanne irin gata daada haka ake gata tsakani da Allah?,kaman na rasa mashinshini?,kawai sai mutum yazo muku sama taka ku karbeshi?" "To yanzu aisai ki hadamu ki zanemu uwarmu,mun miki laifi ko?" Ta fadi tana fiddo idanu tana kallon shahida,wani tashin hankali takeji da bacin rai qwarai,idan taci gaba da magana batasan me zai fito daga bakinta ba,daboda haka ta gwammace ta barwa daada falon kawai,haka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96