Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 80

Chapter 80

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,311 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba,abinda ya debe mata kewa kenan har wata washegarin,saidai randa ta cika kwana na hudu dif kakeji,duk sai taji gidan babu dadi,haka ta wuni ita kadai,daga kwanciya sai kallo sai latse latsen waya,har zuwa dare data kammala abinda take tayi shigewarta daki. Tunda ta gama yin baqi bai kuma sakata a idanunsa ba,kafin magariba ta gama komai tayi shigewarta daki,bata fitowa sai washegari shima idan ya fita a gidan,zatayi abincin safe haka na dare ta aje masa,saidai shima bai bata taba abincin ba,yadda ta jera haka zata kwashe abinta,kusan hakan na faruwa ne saboda ya koma aikinsa gadan gadan,bai samun damar dawowa gidan dawuri,hakanan da wuri yake fita. Sati biyu cur aka suka kwashe a haka,idan ya dawo bai ganinta,hakanan idan zai fita ma haka. Zaman taji ya isheta,kadaicin ya mata yawa,tayi kallo har ta gaji,tayi chart ya isheta,saita yanke shawarar ta sameshi tayi masa magana kan komawarta office don tana da buqatar hakan. Sai data idar da sallar magariba yau sannan ta shiga tayi wanka,ta shirya cikin wani cotton material baqi da aka yiwa adon purple wanda yadan ciza,ta gyara gyara gashinta sannan ta feshe jikinta da turaruka yadda ta saba,duk da ko batasaka turaren ba qamshi kayan suke bayarwa na turaren wutar da take turare kayan nata dashi,nan bakin window din dakinta dake fuskantar harabar gidan ta tsaya,ta yaye labulen tana kallon harabar gidan kawai,duk da babu kowa sai mai gadi dake zaune can bakin qofar gidan,amma ko ina gauraye yake da haske tarwai kaman rana,haka gidan yake da wuta 24hrs. Ta jima tsaye tana saqo tana warwara,har ta soma gajiya da tsaiwar ta saki labulen da niyyar komawa ta zauna taji horn,saita tsaya tana ci gaba da kallon qofa sanda baaba ya tura gate din anwar ya sako motarsa cikin gidan,tabi motar da kallo har zuwa harabar da yake ajesu,tana kallo baban ya qarasa bakin motar bayan ya maida qofar ya rufe,ya tsaya daga bakin window din da alama magana suke sannan ya juya ya tafi. Tayi zaton bazai fito daga motar ba jin shuru na wasu mintuna,kana daga bisani taga ya bude murfin motar ya fito,sanye da mens blazzer ruwan blueblack da baqin takalmi sau ciki,yanayin takunsa kawai zai gaya maka a gajiye yake,idanunta akanshi har ya bacewa ganinta sannan ta saki labulen tana sauke ajiyar zuciya,hannunta saman kanta tana son tuna wani abu tana tursasa zuciyarta kan kada ta tuna mata. A qalla sai data bada minti talatin kyawawa sannan ta yafa mayafinta ta fito,sam bata ko sha'awar hawa samansa amma dole ce xata kaita,taso ace yana zama a falo ta cimmasa a can. Yauma da zata gota table din sai data kalla,komai yana nan akai kamar yadda ta dora,saita tabe baki tayi gaba cikin zuciyarta tana cewa "Kai ka jiyo,nidai na sauke haqqina ko". Yana zaune saman kujera one sitter,sanye da boxer da short sleeve shirt farare qal,fitowarsa kenan daga wanka,yayi relaxing bayansa a makarin kujerar,idanunsa na lumshe ya hada yatsun hannanunshi cikin na juna,haka kawai yakejin gidan ya masa shuru tamkar shi kadaine a cikin gidan,yunwa da gajiya suna damunsa,yana buqatar abubuwa da yawa amma ya rasa wanne zai fara tunawa cikin zuciyarsa,cikin haka yaji kaman an buda qofar falonsa,da mamaki ya ware idanunshi da suka dan kada saboda yadda ya jima da rufesu yana kallon qofar,qwarai yayi mamakin ganinta,amma ya shanye mamakin yana ci gaba da dubanta sanda take takowa ciki,bazaiyi qarya ba ta masa kyai cikin yadin jikinta,saiyaji wani bangare daya cunkushe a zuciyarsa yana budewa,tunanin da yakeson yi ya soma dawowa,kwanaki yau kusan goma sha uku kenan bai sanyata a idanunsa ba,ko motsinta bazai iya fadin yaushe rabon daya ji ba,tana sake matsowa qamshin jikinta na shiga ta qofofin hancinsa,qamshin daya sanyashi lumshe idanunsa ya sake budesu a kanta sanda ta samu hannun daya daga cikin kujerun dake can nesa dashi ta dosana ta zauna kan wuta,shuru ya ratsa dakin bayan sallamar data yi na wasu daqiqu sannan tace "Inason magana dakai" idanunshi ya daga ya kalleta na wasu sakanni kafin ya janye duban nashi daga kanta ya maida idanun nasa ya rufe kaman yadda suke dazu,don shine mafita kawai a wajensa "Uhmmm" yace da ita a taqaice "Inason na koma aiki idan Allah ya kaimu ranar monday" da sauri ya bude idanun nasa ya zubesu fes a kanta,saitaji ya mata kwarjini saboda haka ta janye idanunta daga kanshi "Labari kike bani ko umarni?" Ya tambayeta kai tsaye,yanayin tambayar daya mata yasa dole ta kuma kallonshi,tadan sake tsuke fuska "Shaida maka nake"sai ya maida idanun nashi ya rufe sannan yace "Tunda ba umarni bane ba zaki koma ba,kin gama aiki a triple r gem,bama nan ba kawai,kin gama kowanne aiki ako ina idan ba cikin gidan nan ba" haushi takaici da baqinciki suka cikata,me yake nufi kenan?,yana nufin ya rabata da aikinta,cikin hasala tace "Me kakeso kace?,bayan duka qarfa qarfan daka yimin bai isheka ba har saika qara da wannan?,toni ban yarda ba in gaya maka gaskiya,ai bamuyi haka dakai ba" miqewa tayi tsaye ta soma tafiya "Dama na gaya maka ne donkar kazo ka tarar bana nan kace ban shaida maka ba". Tana dab da fita ta tsinceshi a gabanta,suna hada ido ta kauda kai saboda yadda qwayar idanunshi ta sauya launi "Bazan taba lamunta ki fita wani waje mahada jama'a maza da mata ba da sunan aiki,ki gogayya da maza kiyi magana dasu,ki fita da safe ki dawo da yammaci,idan na barki kika koma lallai na tabbata wawa,kuma abinda nayi baiyi riba ba,kina nufin komawa office din danaga wani ya kama yatsarki zai saka miki zobe?,Karki soma gigin aikata kuskure irin wannan,idan ba haka ba zaki gane baki da wayau,idan kuma baki yarda ba bismillah" daga haka ya kauce daga hanya ya bata waje yana komawa mazauninsa,da gudu gudu ta fice daga falon ta soma sauka qasa,tayi nasarar riqe kukanta batayi agabansa ba sai data danga da dakin gadonta,wani irin tuquqi takeji cikin qirjinta da zuciyarta,sam bazata yarda ba,ba zata lamunci ya sake cin galaba a kanta ba bayan wadda yaci,idan yayi haka aiya tauyeta da yawa,tayita zama kenan cikin wannan gidan da zaman cikinsa harya soma gundirarta,zaman da bai mata ma'ana ba sam?,gobe kam saidai ayi duk wadda za'ayi,idan yaso yace ta wuce gidansu. Iska yake furzarwa daga bakinsa mai dumi bayan fitarta yana murza tafin hannunshi kan hannun kujerar da yake kai,yanajin bacin rai nason taso masa yana danneshi,ta yaya zai barta ta koma aiki?,aikin da tun ranar daya ganta cikinsa bai sake samun nutsuwa ba sai daya tabbatar ta daina zuwa ta sanadin aurenshi,randa yaga nuradden din cikin office dinta da qyar ya samu ya saisaita kansa,ji ya dinga yi kaman hawan jininsa zai tashi,sannu sannu ya dinga ambaton sunan Allah har ya samu zafin da yakeji ya sauka,yunwar da yakeji ta dawo masa sabuwa fil,bashi da mafita illa slipper dinshi daya zira ya sauka zuwa qasan. Karon farko da zauna kan dining din,ya jawo warmers din ya soma budewa daya bayan daya,take qamshi ya cika wajen wanda ya qara qaimin yunwar tasa,tun kafin ya soma ci a ido abincin yayi masa,sanda ya soma ci kuwa saiya samu kansa da lumshe idanunsa,dadin girkinta ya ninka fiye da wanda ya sani a baya,a nutse yaci abincin,ya kuma yi qoshin daya manta rabonshi da yayi irinsa,baibat abincinba

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});