Chapter 38
Chapter 38
dama bayan cin abincin dare yana zama ne cikin yaran nashi su taba hira kafin ya tattara ya wuce dakinshi. "Rahama,meye ya faru ranar hutun noor international?" Tambayar da abbun ya jefo mata kenan bayan ta gama dubawa su farouq haddarsu da wajibul manzil da aka basu kan tajwidi,a hankali ta dago idanunta ta dubi abbun,daita sunkui da kanta qasa,tana tuna duk wani cin fuska da anwar yayi mata,tanq tuna kalamanshi akanta daya bayan daya,wani daci na tasowa daga qirjinta zuwa harshenta,saidai ta dake zuciyarta,batason ko daya ta sake zubda qwalla a rayuwarta saboda anwar "Uhmmm..." Abbu ya sake bata dama ganin tayi shuru "Abbu sun koreni ne" "Kora kaman yaya?,me kika musu?,wannan wanne irin cin fuska ne?" Anty zubaida ta fada a hasale,yayin da abbu yayi shuru har sai da anty xubaida takai aya "Dazu gamayyar malaman makarantarku sun sameni har wajen aikina,sun bani haquri kan abinda ya faru,na gaya musu banda masaniyar abinda yafarun,sun bayyanamin cewa mai makarantar ne gaba daya ya sallameki,dukkansu basu da masaniyar ainihn dalilin daya sanya ya koreki ba,duk da kina daya daga cikin haziqan malaman da suke alfahari dasu,idan don kamarace bake daya kika makara a ranar ba,amma suna so na baki haquri in sha Allahu zasu magana dashi master din,kuma sunsan yana da sauqi zai fahimta,to,duka dai sun gama bayanansu,na kuma ari bakinki naci musu albasa cewa kema ba zaki koma ba,idan baki manta ba dama kan yarjejeniya na barki koyarwa a makarantar,yanzu kuma abinda muka gina yarjejeniyar akai ya afku,saboda haka yanxu kinga nayi winning,dole ki karbi duk aikin dana samo miki kenan" ya qarshe yana murmushi,don bashi da ra'ayin tursasa dan adam ne,amma dama tun asali ta yaya shahida me matakin karatun irin wannan zata tsaya koyarwa a primary?,wanne irin maida kai baya ne "In sha Allahu abbu,nima bani da sha'awar komawar har abada" "Shikenam faduwa tazo daidai da zama,Allah yasa hakan shine yafi alkhairi" "Amin abbu na gode" ta furta idanunta har yanzu na kallon qasa,nan ta yimusu saida safe da zummar zata sha magani ta kwanta. Sai data raba dare tana gayawa kanta ya kamata ta motsa gaba,ta watsar da komai,ta ciyar da rayuwarta gaba,ya kamata ta shafe komai kaman yadda take gayawa kanta a 'yan kwanakin nan,idan bata manta ba,idan kuma zata iya tunawa,anwar din data gani dazu da anwar din data gani satin daya gabata ba shine anwar din data sani shekaru goma baya ba,lallai ba shakka bashi bane,ya kamata aga wata shahidan ta daban ba wannan ba "Yes!" Ta fada tana baiwa kanta qwarin gwiwa da tabbacin zata sauya komai. Washe gari da qwarin gwiwarta ta fito,hakanan tayi yaqin maida murmushi da fara'arta gaba daya,koda bata samu duka ba taji a jikinta ta maida kaso hamsin cikin dari,wanka ta soma yi sa'annan ta fito ta shirya cikin kwalliya madaidaiciya a riga da skert na atamfa don kusan tafi son atamfa saboda tana son kaya cottoon kasancewarta mutum da batason zafi,feshe jikinta tayi da turarenta na din din din,ta tsaya gaban mudubi tana kalli kanta,ita kanta tasan tayi kyau,kwalliyar data jima bata bari ta rabi koda fuskarta ba,murmushi ta sakarwa kanta da kanta tana sake baiwa kanta qwarin gwiwa,sai taji gaba daya hankalinta ya karkata ga aikin da abbun yace zai sama mata,batason ci gaba da zama haka "I need to make my self busy,so i can forget dat am deeply hurt and broke" ta qarshe maganar tana juyawa cikin hanzari ta dauki wayarta ta fice daga dakin. A tunanin anty zubaida zata ganta sukuku ko cikin damuwa saboda maganar jiya amma sai taga sabanin hakan,itama hakan yayi mata dadi sosai,ranar alhamis ce babu islamiyya,haka ta sake sosai cikinsu huda sukayita buga games bayan sun gama karatu,ta kira mutanen data jima bata kirasu ba,ta kira zunnurarta sun jima suna hira,har ita kanta ta dinga tambayarta yau da alama ranar ta musamman ce. Koda noradden yazo shima yazo yau a sa'a,ta tanqwara zuciyarta ta fita ta saurareshi ba tare da wani dogon turanci ba,ba laifi kuma ta dan jima wajensa,don ta dauki mintuna aqalla ashirin abinda bai taba faruwa ba a tarihin zamantakewarsu,ita kanta yau taji zuciyarta sakayau kaman ta rage mata nauyi daga cikin nauye nauyen dake takure da ita. *zafafa biyar na kudine,idan kika gani don GIRMAN ALLAH karkiyi sharing,idan kina buqatar siya ki tuntubi wannan number* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *ga mai buqatar littafina da zanyi bayan kammala alqawarin Allah,yaje youtube yayi searching SAUTIN HIKIMA,zaiga SUBSCRIBE da jan rubutu ya dannan zai koma black,yayi screenshoot ya turo zuwa ga number da zatazo a qasa,zan sakashi group din da yardar Allah SUBSCRIBW KYAUTA NE BA'A DAUKAN KO SISI* 07038670166 *Alqawarin Allah* 2️⃣0️⃣ Zaune yake shi daya cikin dan qaramkn garden din dake bangare raban na gidan nashi,wanda yasa aka masa shi sannan aka qawata masa,yakan yawaita zama lokaci zuwa lokaci musamman a sanda yake buqatar kebewa ko yin wani gagarumin aiki da bai buqatar surutu ko takura,snye yake da t.shirt mai gajeran hannu gami da trouser light and dark brown,tray ne dan qarami aje a ganshi da butar shayi hadi da qananun kofuna guda biyu akai,daya kofin yana hannunsa,idanunsa zube kan laptop din dake kunne gabanshi tana aiki yana kallon wani aiki daya soma tsarawa,inda yake fidda duk wajajen dake da kura kurai,yayi. Da wani sashen kuma ranshi ke a bace saboda sanarwar da nafisa ta fitar a fashion tv,baisan ya akayi ba sai saqonnin taya murna ya tashi dashi fal email dinshi,watsapp dinshi da twitter,angage din ma da ba'akai ga tabbatar dashi ba. Qarar bude gate din gidan da mai gadi yayi ya shiga kunnuwansa,sai yayi tsai yana sauraro,iyakar saninsa yasan dai ya gaya masa kar yabar kowa ya shigo masa gida idan ba muhsin ba,saboda yana son ya hada hankulanshi waje daya,zuciya da qwaqwalwarsa ta samu cikakken hutu. Ba'a wuce minti biyar cikakke da budewar ba ya juyo taku,kamn ya juya saiya basar yaci gaba da abinda yake,don qamshin turarenta daya rigashi isowa ya gaya mishi ko wacece. Ta dauki minti biyar tana tsaye a bayanshi,hannayenta harde a qirji tana qare masa kalla,ba shakka ta jarabtu da son anwar irin soyayyar da bata tsammaceta ba,har kwanan gobe kuma bata ji a jikinta zahiri da badini ta samu irin soyayyar da take kwadayi daga gareshi,haka ta gaji ta saki hannayenta tana fidda ajiyar zuciya ta taka har inda yake,gabanshi ta zagayo ta tsaya tana dubanshi,fuskarta a narke haka ta karyar da wuyanta,sai daya mula don kanshi sannan ya dago ya mata kallo daya,haka kawai yakeji wasu abubuwa marasa dadi akanta,har yanzu baisan a wanne aji zai sanya nafisan ba,ta kuma qi ta gane taqi ta fuskanceshi "Baki iya sallama ba?" Sai tadan sassauta kwabw fuskar da tayi,tana son ta koyi sallama duk sanda ta iskoshi kaman yadda ta fahimci tsarinsa ne amma takan yawaita mantawa,kuma mima ta gaya mata dole ta siffantu da duk wani yanayi da tasan yana so yana kuma cikin tsarinsa "To salamu alaikum" amsa mata yayi duk da har yanzu bai daga kai ya sake dubanta ba "Ba zakace na xauna ba?" Ta fada cikin shagwaba,ture kofin dake gabansa yayi "Sai nace ma?,ai ga kujera nan kina gani ko?" Kai ta gyada a hankali taja kujarar dake fuskantarsa ta zauna. Hannayenta ta hade waje guda,ta sake sassauta murya "Dear...don Allah
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96