Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 89

Chapter 89

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

family d’in MT haka suke lefe duk matan gidan da aka tashi aurar su ko wacce sai da aka yi mata kit d’in gold! Yanzu kuma wannan kinga shine jika na farko da yayi aure. Kaii ammanfa wannan Yarinyar ta tako, gaskiya tayi goshi Allah yasa y’ay’anmu a danshinta. Zata sha gata ba kad’an ba! Naji ma kamar ance wai k’asar zai bari ma da ita gaba d’aya!”. Tabbas zuwa wannan lokacin Umma ta daina ganin komai in banda duhu! Maganar ma sama sama ta dawo ji daga nan kuma jinta da ganinta suka d’auke d’iff!! Mutanen wajen kowa hankalinshi yana kan kallon lefe mai abun mamaki da alaajabi Saboda kaff cikin su babu wadda zata ce ta tab’a ganin lefe kwatan kwacin wannan.... Dimmm!!! K’arar fad’uwar Umma ta sa jamar dake kurkusa da ita zabura suka jujjuyo….. “Subahanallah! Mai ya sameta!! D’in da aketa maimaitawa ne ya janyo hankalin mutanen gurin kaff kowa akayi kanta akai mata rumfa...... A zaune Auwal ya tadda shi, a d’akinsa. Ya jinginar da kanshi a jikin gadon ya lumshe idanuwanshi fuskar shi tayi jajawur! Kana ganinshi ka san yana cikin tashin hankali. Auwal bai damu da yanayinshi ba dan shi ganinsa ma da yayi a zaune ko shirin tafiya bayayi shi yafi komai b’ata masa rai! Cikin muryar b’acin rai yace “Haba Arshaad! Ka sa mutane sun tara jama’a kai kawai ake jira kazo ka wani zauna anan, me kake jira? Gaka nan dai a shirye tsaf! Mai kuma ya hana ka tafiya tun d’azun? Nace maka ina zan taho karka jira ni. Ka san yanda hankalinsu ya tashi kuwa? Dagajin muryar Sakina ka san ba lafiya ba! Taso mu tafi da sauri dallah” Wata nannauyar ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin a hankali ya samu ya d’an bud’e lumsassun dogayen idanuwanshi, sai da Auwal ya d’an zabura sakamokon had’a ido da suka yi da Arshaad d’in! Da kyar ake iya hango maroon eye balls d’inshi da suka b’uya cikin jajawur d’in idanun nasa. Sai a lokacin Auwal ya lura da yanda jijiyoyin kanshi suka fito sukai rud’u rud’u! Da sauri ya k’arasa ya zxauna a gefen shi kafin yace “Lafiya kake?? Me ya sameka haka?” Ya jera mishi tambayoyin duk ya rikice. Banda ajiyar zuciya ba abunda Arshaad yake ta faman sauk’ewa yama kasa yi mishi magana Da kyar ya samu yace “Mammy ce ta….” Sai kuma yayi shiru. Cikin firgici da tsoro Auwal yace “Ta hana ka zuwa?? Lumshe ido Arshaad yayi kafin a hankali yace “Har ma auren! Tace idan aka d’aura sai ta tsine min!” A zabure Auwal ya mik’e kafin yace “Innalillahi wa innailaihirrajiun! Shine kuma ka zauna za ka kashe kanka haka? Zama ai bai ganmu ba! Bara in je in samu su Dad in yi musu bayani, idan ta kama har Granpa sai a sa a case d’in. Mai yasa Mammy zata yi mana haka?” Ya k’arashe maganar kamar mai shirin fashewa da kuka. A hankali Arshaad d’in yace “Ba wanda bai sani ba. Kowa ya san da case d’innan. Har mamanta da sisters d’inta duk an bata hak’uri amman tak’i hak’ura.” Wata kakkausar ajiyar zuciya Auwal d’in ya sauk’e kafin yace “Ya aka yi Mammyn ta sani? Last time da naje na dubasu naga kamar duk basu san da zancen ba.. Na san dama suna iya causing problems shiyasa nima ban yi gigin fad’a musu komai ba! Ko maybe Ummi da aka kawo ce ta kirasu ta gaya musu?” Da d’an mamaki Arshaad d’in yake kallon shi kafin ya sauk’e ajiyar zuciya yace “Baka had’u da Mom ba hala? Sun dawo jiya. All of them” Da mamamki shima Auwal d’in yake kallonshi ya ma kasa cewa komai. A hankali Arshaad ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace “Auwal do me a favour.. Ka kira Sakina, inaso kayi mata bayanin komai amman kace kar ta fad’awa kowa kawai a san yanda zaai a gudanar da event d’in ba tare da an jira ni ba! Yanzu na san Mammy idonta a kaina yake dan tun d’azu nake lura tanata turo Aaima tana mata patrol so ba zan iya fita ba. Sakina is smart she’ll know what to do yanzun In shaa Allah ni kuma anjima da daddare za mu je Ina son ganin Hudan na san abunda zan yi. For now amman kawai ka lallab’a mun Sakina tayi handling komai, kafin nan da anjima.” Cike da gamsuwa Auwal d’in ya d’aga kai alamar to sannan ya zaro waya ya fara kiran Sakina. Tun lokacin da aka fara rangad’a gud’a taji dan haka ta mik’e ta lek’a ta windown d’akin Shuwa.. Ji tayi kamar ta zuba ruwa a k’asa ta sha sakamokon hango su su biyu a zaune da ta yi! Bata ganin fuskar su especially Huda da har yanzu tata fuskar a lullub’e take sannan windown a rufe ne kuma sun yi mata nesa.. Bata san lokacin da hawayen farin ciki suka zubo mata ba! Tana gani yanda mata suke zuwa suna d’an d’aga mayafin kad’an suna shafa mata da hannuwanta shi kuma a tafukan hannunshi da goshinsa ake shafawa sannan su ajjiye musu gift a cikin d’an kwanon da aka ajjiye wasu kuma kud’i. Ba k’aramin burgeta suka yi ba, banda kalmar ‘Alhamdulillah’ ba abunda taketa nanata a ranta tana mamakin dalilin da ya sanya Aaima karkacewa ta gilla mata wannan uwar k’aryar haka Wata zuciyar kuma tace maybe an gyara abunne Mammyn ta sauk’o cikin kawar da tunanin a ranta tace “Chan ta matse musu” Sannan ta hau raya yanda zata yiwa Arshaad in sun had’u na k’in d’aukar wayarta da yayi. K’arar wayarta dake kan gado ce ta katse mata tunani dan haka ta isa ta d’auki wayar.. Kamar ba zata d’auka ba ganin sunan Auwal ne sai kuma ta d’anyi murmushi a ranta tace ‘Kar In zama kaza mana’ dan haka ta d’auka ta kara a kunnenta kafin yace komai tace “Gashi chan Ya Arshaad d’in yazo suna zaune ana saka su a lalle. Thanks for your time” Tana gama fad’in haka ta katse kiran. Da mamaki suka kalli juna shi da Arshaad dan a hands free wayar take Shiruu, d’akin ya d’auka chan kuma Auwal yace “Bara inje wajen maybe ko fushi suka yi shiyasa tayi min gatse” Cikin katseshi Arshaad yace “Kaje wajen Mom mana. Kace bama ka san ta dawo ba bayan a gida d’aya kuka kwana. Kaje wajenta daga nan ka d’an lallab’ata may be in tasa baki Mammy ta hak’ura.” Har ya d’anyi gaba sai kuma ya juyo yace “Su kuma fa?” “Kar ka damu na gama tsara komai, zuwa anjima da daddare za muje in shaa Allah. Zan sameka a gida.” Cewar Arshaad yana mai maida kanshi da lumshe ido dan kanshi ba k’aramin ciwo yake yi ba amma kuma har ga Allah y’ar maganar da ya samu suka yi da Auwal ya d’an ji sassauci a ranshi. “Allah ya kaimu” Shine kawai abunda Auwal yace yana me fita daga d’akin da waya kare a kunnen shi still yana sake kiran Sakina sai dai har ya tsinke bata d’auka ba. A tsakiyar main parlourn suka kusa yin karo da Aaima, kasancewar hankalinshi naga wayarshi yana turawa Sakina message. D’agowa yayi yana kallonta itam ma shi take kallo kafin

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});