Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 36

Chapter 36

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

alak’a da shi ba? Eh? Kika barni a duhu?” Cikin rashin fahimta tace “Wallahi ni ban gane komai ba! Dan Allah ka fahimci ni”. Shiruuu, Auwal yayi yana d’an nazartarta yana kallonta.. Chaaan! Kuma yayi tsaki kafin yace “kije ki tattaro kayan ki, ki wuce wajen Gwaggo Asabe, i’ll get back to you, idan kuma zaki zauna anan d’in ne to zan iya barinki but ki tuna abunda na fad’a miki d’azu!”. Da sauri ta nufi d’akin ta na sama, kafin minti goma ta tattaro komai… Auwal ji yake kamar ya shak’e ta yayi ta dukanta! Kawai dai ya barta ne ya samu ta rabu dashi for now dan bayaso Daddy yazo kiranshi da kansa! Amman tabbas sai ya koya mata hankali, dukda ya fahimci kamar jahilcinta da dak’ik’ancinta ne ya janyo komai.................. A gate d’in estate ta had’u da su duk sun fito har Gramma wadda ta kawo su Shuraim don tun jiya da suka k’i bacci da safe kuma suka dinga yiwa Abba kuka akan suna son Ummi ta dawo, ya kaisu wajenta. Da kyar ta lallab’asu bayan tace musu “Ummin tayi y’ar tafiya ne amman soon za su dawo, suyi hak’uri.” Hudan tana k’arasowa Gramma ta kamo ta, tace “Ki kwantar da hankalinki Ki bisu kinji, na san kina kewar Maman ki, amman na san Abba da kansa zai kaiki idan komai ya gama daidaituwa, kinji y’ar albarka?”. Anhankali ta d’aga mata kai tanajin k’aunar matar da girman ta suna ratsa zuciyarta. Dad shima abunda ya fad’a mata kenan sannan yace “duk abinda take buk’ata idan sunje ta rubuta ta bawa Arshaad ya kawo mishi,,already anyi mata d’an siyayyan abubuwan da zata buk’ata for now suna cikin mota.” Da “to” da kuma godiya shima ta amsa mishi. Auwal yana fitowa daga mik’a Jalila wajen Gwaggo Asabe suka fara shirin tafiya… Abba ne ya bud’e mata gaban wata mota yace ta shiga, tana shirin shiga dai dai nan Gwaggo Asabe wadda ta fito yanzu ta k’araso taja Hudan tayi hugging d’inta, ji suke kamar kar su rabu dan har sun saba a cikin y’an wuni biyun da suka yi tare. Auwal yana gefe in banda tab’e baki babu abunda yake yi, ji yake kamar yaje ya shak’e ta! Shi fa ya tsani yaga ana fifita wani, kuma ya lura kamar hakan a jinin y’an gidan yake! k’iri k’iri sun iya nuna banbanci…..gashi yanzu ma akan y’ar k’ank’anuwar Yarinya an kwashe Surukan gida kaf! An kai cell, an bar mahaukaciya!…. Ya ja tsaki yafi a k’irga k’arshema mota ya shige yana ta mita a ranshi yana cewa “Kamar duk ba a tsatso d’aya muka fito ba!” Mu an maida mu kamar wani bole especially ma ni….kowa idan ya tashi k’orafi sai kaji yace ‘Auwal’.” Shi kad’ai haka yayi ta mita yana ta faman kumbure kumbure.. Su kam bama su san yana yi ba. Sallama suka yiwa juna kafin Gramma ta ruk’o hannunta (Hudan) da kanta ta saka ta a mota ta juyo. Daurewa kawai take yi, amman Abba yana zuwa da yayi hugging d’inta sai ta kasa ci gaba da daurewa ta fara hawaye. Da kyar suka lallasheta sannan suka maidata gida, suka fito, suka kama hanya ba dan ransu yanaso ba, suka fice a estate d’in suna masu jin dumbin kewar gida cike a zuk’atansu. Suna fita suka had’u da motar Kaka da Madu, horn suka d’anyi musu don haka suka dakata! Dan shi Abba bai ma gane su ba. A D’an gaba kad’an suka yi parkin, dan haka suma su Kaka suka juyo da akalar motar tasu suka isa inda suke suka yi parking…. Suna fitowa Abba ya ganesu dan haka ya k’arasa ya cewa su Aslam su zauna a motar, shi da Dad kuma suka fita suka samesu. Suna wucewa itama Hudan ta fara k’ok’arin bud’e k’ofar amman sai ta jita a rufe! Cikin d’an tsare gida tace “zan je wajen Kakannina!” A k’ufule yace “Baza ki ba!” Wani takaicine ya rufe ta taji kamar ta rufeshi da duka, taya ga su Kaka tana kallo suna kallonta, amman ace ba zata je wajensu ba? Inaaa, ba zai yiu ba! Dan haka ta fara k’ok’arin bud’e k’ofar ta k’arfi! Tun k’arfinta. Ta gefen ido yake kallonta, tanata dambe da handle d’in motar, tun k’arfin ta. Ta fi minti biyar tana fama ganin ta kasa yasa ta juyo da d’an ladabi tace “Ya Aslam dan Allah ka bud’e inje wajen su mana.” Ta bashi dariya sosai amman ya danne, still amsar d’azu ya sake maimaita mata babu alamun wasa a fuskarshi “Baza ki ba!” Wani k’ululun takaici ne ya tokare mak’ogwaronta, dama ga haushin Arshaad da take ji tun d’azu! (Don Abba har yana shirin shiga motar da take amman ya janyeshi yace “yazo zai tuk’a shi”) Yanzu gashi ya had’ata da wannan boss d’in! Shi bai bari ta tafi da Abba ba kuma shi ma ya kasa shigowa su tafi tare ko dayake ta san saboda yana jin kunyar had’a ido da ita ne shiyasa! Kuma ya san koda ya shigo d’in ma fita zata yi ta bar mishi motar dan haka d’in ta gama shiryawa a ranta. Amman kuma at least ai da ya gwada Insted yana kallonta amman ya shige motar Abba yaja suka tafi da shi da su Shuraim.. .....Abunda Huda bata sani ba shi kuwa Arshaad fushi ya d’auka da ita bana wasa ba ata dalilin zargin da tayi mishi!. Bata iya rashin kunya ba amman bata san lokacin data tak’ark’are ta zabgawa Aslam wata uwar harara sannan ta murguda mishi baki ba! A tunanin ta su Abba yake kallo dan direction d’insu taga yana kalla amma abunda bata sani ba shine duk abunda take yi yana kallonta ta gefen idonshi. Tunda yake a rayuwarshi bai tab’a ganin harara da murgud’a bakin da yayi matuk’ar burgeshi da bashi dariya irin wannan ba, hakan ya sanya wani sassanyan murmushin da ya dad’e bai yi ba wanzuwa akan kyakkyawar fuskarshi, wanda har sai da Hudan taji sautin murmushin tayi saurin juyowa tana kallonshi amman ga mamakinta sai taga still su Abba yaketa kallo waenda suka tsaye a setin su.. Gani tayi kamar Madu yana magana da fad’a fad’a! Cikin takaici ta juyo tana kallon Aslam a ranta tana aiyyana “wato dan yaga ana fad’a shine yake murmushi, lallema wannan mutumin!.” A chan wajen su Madu kuwa abu bai yi dad’i ba! Dan tun farko da Madu ya tambayi Abba “dalilin da yasa ya d’auko Hudan lokaci guda haka?” Abba ya k’ule! A ganinsa dan mai yasa Madu zai yi mishi tambayar ‘dalilin d’aukar y’ar sa da yayi’ bayan shekaru da dama da yayi ba tare da ita ba!. Daga k’arshe dai, Abba tafiya yayi ya bar wajen dan bayason yayi musu rashin kunya. Daddy ne ya tabbatar musu da “sunje har unguwar da Hudan ta taso kuma sunji irin zaman da Huda tayi a gidan Baba, wajen mutane bakwai suka tambaya amman duk maganarsu d’aya ce! Ba abunda basu saniba a halin yanzu na irin zaman da Hudan tayi na azaba a hannun mutumin nan, har k’usar da Ja’afar ya buga mata a ciki suna da labari!” Yace musu “Tun jiya suke ta faman lallab’a Abba, da kyar suka samu ya hak’ura amma daa cewa

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});