Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kika yi ta aika mishi da threats kala kala ba?” Shigowar Doc ce ta katsewa Arshaad maganar da yake shirin yiwa Aslam akan attitude d’inshi towards Mama!! He’s is not like this kwata kwata, he wonders why yake yiwa Maman haka. Ba tare da Likitan yace “k’ala ba ya juya ya fita, ko minti d’aya bai yi ba ya dawo da takardar sallama ya bawa Aslam sannan yace “Kuje gida kuyi solving issue d’inku, dan har ga Allah kun hana marasa lafiya sukuni!! Ba sai kun rufe file ba, zaku iya tafiya kawai…” Yana gama fad’an haka ya kama hannun Mama ya cire mata cannular yana cewa “kuna gama cases d’inku ki tafi asibiti, dan ina jin tsoron jikin nan naki a haka!.” Yana fita Mama wadda daman abunda takeso kenan, ta yafa mayafinta, sannan ta cewa Huda “wuce mu tafi!” ………. Kasa sauk’e kafarta data d’aga da niyyar tafiya tayi jin Abba yana cewa “Babu inda Huda zata bii ki!!” Da mamaki ta juyo tana kallon Abba kafin tace “Ban gane ba!” “Babu inda zata je, tare da ke!!” Abban ya fad’a yana mai k’arasowa inda take sannan ya zuba mata idanuwanshi da ta kasa jurewa kalla tayi saurin yin k’asa da kanta. Cikin tattaro dukkan ragowar k’arfin jiki kuzari da jarumtar ta, ta zagayeshi taje inda Hudan take ta fara k’ok’arin kama hannunta amman kafin tayi hakan tuni Aslam ya juyo da sauri ya rigata, sannan ya tura Hudan bayansa, shi ya zamana yana a gaban Maman!! Da kyar ya iya bud’e idanuwanshi da ya runtse!! Tun lokacin da ya rik’e hannun Hudan ya zubasu a kan Mama! Cikin wata iriyar kasala data dirar masa lokaci guda yace “You have to pass through me first!” Arshaad kam zuwa yanzu ya zo wuya!!! Dan haka cikin fushi ya kalli Aslam d’in yace mishi “Let her go!!” “No” Yace ba tare da ya kalleshi ba! Sannan ya dakawa Hudan wadda take ta k’ok’arin kwace hannunta tana kuka tsawa “Ki nutsu!!”. Wani irin irin kuka Mama ta fashe da shi a take ta durk’ushe a wajen abin tausayi. Abba ne ya umarci Aslam da “Ya kai Hudan mota dan in dai yaci gaba da ganin Maryam a haka tou za a samu matsala!” Da sauri Arshaad yace “babu fa inda zata je ba tare da Mahaifiyarta ba!!! Haba Abba! Ka san kuwa shak’uwar dake a tsakanin y’a da uwa?? Ka san abubuwan da suka yi going through tare, lokaci d’aya kawai kazo kace zaka d’auketa haka nan? Why are you trying to be selfish???” Kallonshi Abban yayi da idanunsa da suka fara rinewa…. He‘s tired so tired of everything!! A yanzu yadda yake jin zuciyar shi tabbas idan ya tsaya kula Arshaad to zai iya yi mishi illa!! So yake yi kawai ya isa gida tare da Huda ya fuskanci kowa da komai! Masu laifi kuma ya hukuntasu dan bashi da tantamar cewa akwai waenda suka san da zaman Huda a dunyia a cikin estate d’in su… Apart from that ma inda ace ya san yanada y’a tun farko to da ko kwana d’aya ba zai barta tayi a gidan Usman ba which definitely ya san anan take da zama… Tabbas ya san bai kyautawa Maryam ba, but she’s not ready to listen!! Baya jin kuma zata yarda ta bashi Huda a cikin sauk’i! Shi kuma a halin yanzu ya kai peak!! Edge!!Limit!! Na tolerance… So yake kawai ya isa gida. Shiyasa cikin k’ok’arin danne zuciyar shi da yake ji tazo masa iya wuya!!! Ya cewa Aslam “Kai ta mota!! Idan tayi tirjiya ka d’auketa!” Yayi maganar ba tare da ya d’auke idanunsa da suka koma tamkar garwashin wuta daga kan Arshaad ba! Yace masa “Do your best ka lallashi Maryam sannan ka maidata gida.” Yana gama fad’an haka ya juya ya bi bayan su Aslam da Huda wadda ta bisa salin alin dan , gani tayi ana cewa ‘ya d’auketa’ ya durk’usa ya fara k’ok’arin ciccib’arta…. Amman fa kukan da take yi still tana k’ok’arin zame hannunta ana Aslam ya sanya gaba d’aya hankalin duk mutanen da suka wuce ta gabansu ya dawo kansu, da yawa tunanin su rasuwa aka yi mata, shiyasa ba wanda yayi k’ok’arin tsaidasu! Sai dai ‘Allah ya ji k’an rai’ kawai da wasu mutanen suka dinga cewa Wasu kuma kallon tausayi suka bisu dashi. Aslam yana isa bakin motar yaiyi mata key ya bud’e ya dannata a ciki ya rufe sannan ya zagaya mazaunin driver ya shiga ya bata wuta, ba tare da ya jira Abba ko Arshaad ba ya d’auki hanyar MT estate da ita........ Arshaad gaba d’aya ya tsorata da ganin yanayin Abba Dan tabbas bai tab’a ganinshi a irin wannan yanayin ba! Duk inda bacin rai ya kai b’acin rai to yau ya hango shi a kwayar idanun Abba! Shiyasa ya kasa tsaidashi. A hankali bayan fitar shi yaje inda Mama ke durk’ushe tanata faman kuka shima ya durk’usa gaba d’aya ranshi ba dad’i! A hankali yace “Mama dan Allah k.....” Kallon da ta d’ago tana yi mishi ne ya sa ya had’iye ragowar maganar sa! A hankali ta mik’e ta gyara mayafin jikinta sannan tace “Arshaad mai yasa kayi mana haka?” Da mamaki yake kallon ta kafin yace “Mama ni kuma mai nayi?” So da Buri Free Book 39 Da sauri Sakina tace “Mamaa” sai kuma ta k’arasa wajen da sauri ta hau tattab’a ta, ganin bata motsi yasa ta sa hannu ta juyo da ita! “Innalillahi wa innailaihirrajiun” Shine abinda Sakina Ummu da matar dake gefen Mama suka fad’a a tare, dan a yadda Sakina ta juyo da ita haka ta biyo hannun Sakinan ta taho yuuu ta zube wanwar kwanciyar rigingine. Ummu mutuwar tsaye tayi a wajen, so take ta k’arasa inda suke amman ta gagara sakamokon ganin y’ar uwartata da tayi kwance tamkar gawa! Ta kasa tab’uka komai banda hawaye ba abunda take yi. Sakina wadda ta rikice tanata tattab’a Maman ne ta juyo tace “Ummu ki zo ki kamata mu mik’ata emergency.. Mama ce amman bata numfashi.” Jin hakan ba k’aramin sake rikita Ummu yayi ba, ita dai kawai ta ganta a gabansu a tsaye amman bata san ya aka yi ta isa wajen ba. Matar nan ce ta matso itama ta hau jijjiga Mama tana cewa “kumafa yanzun nan muka gama magana da ita, tun jiya muke nan tare da ita. In banda kuka ba abunda take yi, nayi tambayar duniyar nan tak’i kulani… Sai dai kawai taje tayo alwala tazo tayi ta sallah. Sai d’azu ne da naga kamar batta lafiya nace ‘tazo muje in rakata taga Likita’, shine na samu ta d’an kulani ta inda take ce min ‘bara ta d’an yi bacci, idan ta farka sai muje’.” Ita dai Sakina cicib’arta ta fara k’ok’arin yi hakan yasa suma suka sa hannu suka taimaka mata suka yi waje da ita..... Su Madu suna tsaye a k’ofar shiga emergency.. Kana ganinsu ka san hankalinsu ba a jikinshi yake ba! Ga tsananin gajiyar da suke tare da ita Dan ma Allah ya taimaka Abokin Junaidu ne ya biya musu kud’in jirgi su kuma suka biyawa Baba Saboda yaga yanayin tsufansu gashi da ya kira Baban ma a hanya ya jisu suna dawowa daga wata tafiyar…. Ba

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});