Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 39

Chapter 39

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

addu’ar a shafa mata . Suna fita Abba ma yace mata “ta d’auko hijabinta ya kaita ta duba Mama” Murna a wajen Hudan ba a magana dan da gudu ta haye benayen, bata yi minti uku a saman ba ta sauk’o sanye da hijab har k’asa wanda ta gani a cikin kayan da aka bata. Ya lura da yadda jikinta har karkarwa yake yi, shiyasa bai b’ata mata lokaci ba yace “suje”. Da sassarfa ta shige motar. Shi dai Abba kallonta kawai yake yi, tabbas Hudan da shi take kama komai da komai amma idan tana wani abun sai ya dinga ganinta kamar Maryam!!! Wani d’an murmushi ne ya sub’uce mishi, a hankali cikin sanyin jiki ya murza key ya tada motar ya nufi gate. Masu gadin gidanjensu na chan estate su suka d’auko suka taho dasu.. Suna Isa gate d’ayan ya ajjiye rediyonshi a kan dogon bencin da suke zaune su wajen biyar harda driver da mai wankinsu da gyaran fulawar, yaje ya bud’e musu makeken gate d’in, suka fice. Tunda suka fita Huda ta kasa sukuni, tsabar zumud’i, gani takeyi kamar Abba baya gudu, har d’an tasowa take yi ta d’an lek’a gaban titin ta gaban glass d’in motar.. Dariya ta bashi sosai dan haka yace “Gani kike kamar bana gudu ko?” Ya fad’a yana dariya sannan ya k’arawa motar wuta… Itama murmurshin tayi ta koma ta zauna da kyau a mazaunin ta. Tafiyar minti ashirin ce ta kaisu AKTH emergency, dan ma sun d’an tarar da go slow a hanya. Tana shirin fita taji yace “You promised Hudan, right?” A hankali ta d’aga mishi kai, sannan tace “Na gode sosai Abba” sannan ta fita. Da kyar security suka barta ta shiga bayan tayi ta nacin ce mishi Mamanta ne a kwance, Allah ya taimaketa, wanda yake gadi ne a wajen ranar da suka kawota ita da Aslam, kuma d’azu tabbas yaga Maman nata an fito da ita tana d’an zagaye, shiyasa ma ya barta ta shiga, don ya tunata tun ranar da suka zo ita tana kuka shi kuma yanata mamakin had’uwar Yarinyar, hakanan yaketa ganin hoton fuskarta a zuciyarshi amman ya san ko hauka yake ba zai ma yi tunanin tunkarar ta ba. Dube dube ta hau yi bayan ta shiga, da kyar da sid’in goshi ta hango su… Mama da Ummu a kan gadon a zaune suna magana da alamun mai matuk’ar mahimmanci ce sai Sakina ita kuma a gefe kan kujerar mai jinya da waya a hannunta. BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 41 Basu ga tahowarta ba, kawai suka ga an afka kan Mama da gudu an rungumeta! Kukan da ta fashe dashi ne yasa suka gane itance, da sauri Sakina ta d’ago ta, ai kuwa tana ganinta tayi hugging d’inta tana dariya. Ummu itama murna kamar tayi me, Mama kuwa ba a magana. Ummu ce ta zare Hudan daga jikin Sakina sannan ta d’an muskuta ta ajjiyeta a tsakiyar su ita da Mama. A hankali Mama tasa hannu ta shafa fuskarta tana hawaye, da sauri itama Hudan ta goge mata hawayen tace “ki bar kuka Mama, i missed you so much, kwana biyun nan ji nayi kamar shekara wallahi” Ta fad’a tana sakin wani kukan, sannan ta kwanta jikin Mama. Sakina ce ta d’aka mata duka a cinya kafin tace “dalla Malama d’agata, kin wani zo sai kuka kike yiwa mutane salon ki karya mana zuciya muma mu biye ki! To Mama dai ance a daina sakata a damuwa dan haka sai kiyi k’ok’arin tashi ki ware garau ki bar wannan tab’arar.” Da sauri ta d’ago tana goge hawayen da suka k’i tsayawa, da kyar kuwa ta tsaidasu, ta d’an harari Sakina tana murmushi sannan juya tace “ina wuni Mama, ya jikin ki?” Da murmushi Maman tace “Alhamdulillah” Sannan Huda ta juya ta gaida Ummu, wadda itama ta amsa mata cikin kulawa sannan tace “ya mutanen gidan naku?” A hankali Huda tayi k’asa da kanta tace “Alhamdulillah” Sakina ce tace “a estate d’in kike? Family house d’in nasu kamar estate ne kowa da kowa ko?” Numfashi Hudan ta fesar tukun tace “Eh, nan aka kaini da farko, amman yanzu dani da Abba da Daddy da Ya Auwal mun tashi mun koma wani gida a baya. Saboda Granpa yace ‘Abba sai dai ya zab’a, ko ni ko su!’.” Cikin mutuwar jiki Sakina tace “Shine ya zab’e ki kuka tashi?” Da “eh” ta amsa, kafin tace “Har da d’an uwanshi ‘Daddy’ shima muka tashi, sun yi fad’a sosai jiya da Granpa d’in.” Tana shirin sake yin magana Mama tace “Kuka tashi as in how?? To ai yayi ta banza ne, dan ke kam kin zo kenan!! Ya aka yi kika fito? D’azu su Kaka suke gaya mana kalar rashin kunyar da yayi musu ai! Yanzu haka takardun shiga kotu ake had’awa!…” Cikin rashin jin dad’i Ummu tace “Mama dan Allah ki daina biyewa su Abba Modu kina k’ara tunzurasu! Kina ji fa bawan Allahn nan har gidansu ya bari, saboda ita!. Ko fa anje kotun nan na fad’a miki bamu da nasara saboda kamar yadda Abba Madun yace d’an uwanshi( Daddy) ya fad’a musu d’azu ‘ko a iya case d’in Baba aka tsaya dole a bashi Hudan!!’ Ballantana kuma idan aka duba yanayin standard of living! Shi (Abba) yana da aikin da zai iya kula da ita ke kuma.....” Shiru Ummu tayi ta kasa k’arasawa ganin yanda Maman ta kafeta da idanuwa. Cikin jan numfashi Maman tace “Ki k’arasa mana! Ni kuma bani da aikin yi, bani da komai ko?.” Sai kuma tace “Bari kiji idan su sun yi amfani da Baba to ni kuma zan yi musu amfani da Granpa! Ai har gara Baba shi bai tab’a korar Huda a gidanshiba, Granpa fa?” Cikin katseta Ummu tace “Amman ai yanzu ko me Granpa yake ji dashi bai isa yayi mata ba! Saboda Abban ma ya d’auketa a kusan shi gaba d’aya! Dan haka Kotu ba zata duba wannan bama a matsayin reliable.” Cikin d’an fad’a Mama tace “Wai Ummu kina nufin in barta kenan a wajenshi ko me kike son gaya min?” Cikin kwantar da murya Ummu tace “ba nufi na kenan ba, ki fahimceni Dan Allah… Maganar shiga kotun ne bana so saboda idan anje mune za muji kunya! Kuma In dai Abba yaga anbashi custody d’inta gaba d’aya to fa ba lalle ya dinga barinta tana zuwa mana ba! Mama, Hudan y’a mace ce! Makaranta ma zata shiga yanzu university wanda idan kika kwantar da hankalinki ma wata rana a wajenki za tayi Hutun ta! A hankali a hanakali zakiga zata iya dawowa wajenki gaba d’aya wata rana. Abunda nake so dake shine yanzu ki barshi (Abba) Zafin zuciya ne kawai yake damunshi.. Ni a nawa ganin banga amfanin a shiga kotu anata kace nace ba k’arshe kuma na san mu ne da kunya!. Kuma Hudan aure zata yi nan ba da dad’ewa ba, daga k’arshe fa dole ta bar gabanku gaba d’aya daga ke har shi. Dan Allah Mama ki fahimceni ki tayani fahimtar da su Kaka.” Cikin tsananin b’acin rai Maman tace “Eh!! Ai shiyasa ya turo mata da Arshaad, kuma abunda basu saniba na riga na gama yanke hukunci ‘In shi kad’ai ne Namiji a duniya to

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});