Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 47

Chapter 47

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tace “gaskiya wajen nan ya burgeni Huda, over!! Ina tunanin had’uwar parlourn ashe bedroom d’in har ya fishi? “ Murmushi Hudan tayi tace “Ni kuma duk toilet d’in yafi burgeni” da sauri Sakina tace “muje In gani” ta fad’a tana cire hijab d’in jikinta dake nan har k’asa. Suna shiga nan itama tace “gaskiya kam toilet d’in duk yafi had’uwa” Haka nan suka taru suka dinga hauka, daga su kunna wannan sai su kashe wannan, wani abun ma ba iyawa suka yi ba da karambani suka koya. Babu abunda yafi burge Sakina irin closet dan haka ta fito wajen tana kuma setawa Hudan zaman kayanta kafin ta fito a wanka. Bata wani dad’e ba ta fito a wankan tana fitowa tace “itama ta shiga tayi wanka sai ta chanja kayan jikinta, lace d’in zai yi mata nauyi dan garin ana zafi sosai” Murmushi Sakina tayi kafin tace “Ni fa daga ni sai hand bag d’ina nazo, Ummu daa hanani zuwa tayi fa, sai da Baba ya bud’e mata wuta!Amman tace wai gobe da safe in dawo, har na d’auko kaya set uku tace wai In na tafi da kaya ba zan dawo da wuri ba! Shi kuma Baba yace tunda Abba ne da kansa ya rok’esa to sai lokacin da kika saba da nan d’in tukunna zan koma!. Wallahi tun d’azu jikina a sanyaye yake, Mama ma bata san na taho ba, dan Ummu tace bata san da wanne ido zata kalle ta ta fad’a mata ba! Shinema dalilinta na hanani zuwa tun farko daman.” Ajiyar zuciya Hudan ta sauk’e kafin tace “Ranar dana tafi ya aka yi? Ina ta kiran Ummu bata d’auka.” “Hmm.. Mama ce ta rikita kowa wai Abba ya aiko an sace ki! Amman har yanzu a haka su Ummu suka barta basu gaya mata ke kika tafi da kannki ba saboda kar taji haushinmu, kawai dai ance mata kina nan d’in so ta kwantar da hankalinta tunda kina wajen Mahaifinki ne ba wani mugun hannu ba.” Hawaye Hudan ta goge kafin tace “Sakina wallahi ni ban san ya zan yi ba” ta fad’a tana fashewa da kuka, rungumeta Sakina tayi kafin tace “wallahi Huda ni kaina abun nan yana daure min kai, sai ka rasa ina zaka tsaya, gaba d’aya ni kaina i’m confused, ballantana kuma ke. Muyi ta addua kawai ki kwantar da hankalinki, kinji?Please”. Hawayenta ta goge jikinta duk yayi sanyi, sannan ta d’an d’aga kanta a hankali kafin ta cewa Sakinan “kije kiyi wanka sai ki sa kayana Inner wears kuma ina da sababbi suma, muyi sauri dan na san yanzu Abba zai fara kira, lokacin dinner yayi.” Hijab d’inta wanda ta ajjiye a bedroom Hudan ta fita ta d’auko ta wuce ta sa a washing machine ta fito ta bata towel, Ita ta tayata wankin dan sai da ta tayata ma shanya kayan data cire suka wanke d’in tukun ta fito ta barta dan tayi wankan. Sallah ta tarar Hudan tanayi lokacin da ta fito dan haka itama ta nemi hijab ta tayar da sallar. Sauranta izu d’aya a izu goman daya kamata tayi, dan haka ta hau karatu bayan ta idar…. Tana idarwa tayi addua ta tofa ta had’e ruwan d’azu data shigo dashi dana d’akin waje d’aya!. Da mamaki Sakina ta kalle ta kafin ta tambayeta Bayani ta hau yi mata a kan ‘na maman Aslam ne wanda ta basu labarinta….’ “Allah sarki Allah ya bata lafiya, abun tausayi wallahi” Sakinan tace. Kayan bacci dukkansu suka sanya, sai suka d’aura hijabai a sama, sannan suka sauk’a dan Abba har ya kirata kamar yanda tayi tsammani. Sai da ta lek’a d’akin su Sudais, ganin basa nan yasa suka nufi k’asan. Har Aslam suka tarar a dining d’in da Arshaad amman yanzu ya chanja kaya wanda hakan ke nuni da wanka yaje yayo. Yaji tahowa amman bai d’ago ba, dan babu abunda yake sosa mishi zuciya irin yadda ko kallon inda yake bata yi. Sai da suka k’araso tukun Abba yace “a’a inyee! Yau ga annuri a fuskar princess, duk a dalilin Sakina, irin wannan murmushi haka?!” Ya fad’a yana murmushi kafin yace “bismillah ku zauna mana” A hankali suka fara k’ok’arin jan kujera… Yana shirin d’agowa ya ga da gaske Sakinan ce jin abunda Abba yace, yaji tace “Ya Arshaad Ina wuni.” Da sauri ya d’ago, ya d’an zaro ido alamun mamaki, sai kuma ya fara murmushi yace “Lafiya, Alhamdulillah. Ashe kece da kanki! Welcome, ya gida?” “Alhamdulillah” tace kafin ta d’an turo baki tace “Ai gani nayi da farko ka wani had’e rai ko kallon inda muke ma bakayi ba” Dariya yayi kafin yace “Hankalina baya wajen ne, sorry” Itama murmushi tayi ta sake gaida Abba da Aslam wanda ya amsa ko kallonta bai yi ba! Tunda suka sauk’o ma ta lura bai ko kallesu ba… Tana ganinshi tashi d’aya ta fahimci shine Aslam. Lokacin da Hudan take zuzuta mata kyawun Aslam d’in bata yarda ba, dan har ta fara tunanin wani abun a tare da Hudan na daban, but yanzu kam tagani itama! “Tubarakallah!” Ta fad’a a k’asan ranta. Cikin nutsuwa taji Hudan suna gaisawa da Abba wanda yake zaune a opposite d’insu shi da Aslam. Da kulawa yake tambayanta hope taji dad’in ganin Sakina? Is she happy now? Taji dad’in zuwa munjibir park d’in? Ba wata damuwa ko?…… Murmushi Hudan tayi duk tana ta binshi da “Alhamdulillah komai Alhamdulillah..” Abun yayi matuk’ar burge Sakina a ranta tace “yau ina Baba da Umma suzo suga gatan da akewa Huda, suga yanda Abbanta yake janta a jiki yana lallab’a ta” Wani farin ciki ne taji ya lullub’eta, tabbas tana yiwa Hudan murna da baiyyanar Mahaifinta! Itafa sometimes ji take a ranta kamar ma tafi Hudan farin ciki. A hankali taji sun gaisa da Aslam, taga ita Hudan ta d’an samu darajar kallo a wajenshi tukunna yace “lafiya” da d’an mitsitsin bakinshi. Har an fara serving ta mintsili Huda da k’arfi ta k’asa k’asa inda ba za a gani ba. “Ouch” tace, a hankali sannan ta juyo tana kallon ta, harara Sakina ta zabga mata k’asa k’asa tace “shi ba zaki gaidashi ba???” Itama Hudan hararar ta maida mata ta cigaba da zuba abincinta! Mintsilinta Sakina ta sake yi, kafin tace “Wallahi ko ki gaisheshi ko kiyi ta karb’ar ruwan mintsili kala kala!” Dai dai nan wayar Abba tayi k’ara … Excusing kanshi yayi ya mik’e ya d’an koma gefe yana amsa wayar dan it’s a very important call ba zai yiu yayi ignoring ba. Kamar jira Sakina take, nan ta sake sakar mata wani sabon mintsinin da sai da tayi k’ara mai sauti sosai this time around har su Aslam sai da sukaji suka juyo suna kallonsu… Sudais kuma ya fara kyalkyala dariya dan shine a kusa da Sakina yana kallonta tun d’azu! Ganin da Huda tayi Sakina ba zata hak’ura ba yasa ta juya, kujera biyu ne tsakaninta da Arshaad d’in dan haka ta d’an kalleshi tace “ina wuni” Sai da ya sake tamke fuska tukun yace “Lafiya” Yanajin haushi a ranshi, wato gaisuwar ma sai ta ga dama zata yi, kuma shine na k’arshe! Har su Sudais sai da ta gama kulawa tukunna shine last! Tashi Sakina tayi daga kan kujerarta ta dawo ta gefen Hudan side

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});