Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 84

Chapter 84

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi’ Amman ta kasa nutsuwa kuma zuciyarta ta k’i ta daina tafarfasa…… Sannan zata fita daga estate d’in nan, da Auwal ya maida mata shi kamar kurkuku. Murmushi tayi aranta tace “Zan jefi tsintsu biyu da dutse d’aya!” Driver ne ya jasu su duk biyun a baya, kamar yadda tayi zato kuwa masu gadin da kyar suka bari aka fita da ita.... Sai da Mom ta nuna mata d’akin da zata zauna a sama, daganan ta wuce nata d’akin. Sai da Ummi ta tabbatar kowa ya watse tukun tabi bayan Mammy Sisters d’inta( Mammyn) kuwa ko sallama basu yi mata ba suka wuce suka rabu da ita. A d’aki ta sameta sai faman safa da marwa take yi ta hana zuciyarta sukuni sam!. Ta ganta sarai taga shigowarta amman sai tayi banza da ita taci gaba da kai kawon da yake yi. A hankali Ummi ta nemi waje ta zauna tukunna tace Mammy Da sauri Mammy tace “Zainab tashi ki fita! In dai shawararki kika san zaki sake bani to tashi ki fita tun kafin raina ya b’aci!”. Murmushi Ummin tayi sannan ta fara magana “Dama ai in dai kinga mutun yana farin ciki idan ana bashi shawara in yayi ba daidai ba to ki tabbata ba gaskiya ake fad’a mishi ba! Nazo in baki shawara ne Mammy kuma zan yi matuk’ar farin ciki idan naga kina jin haushin shawarar tawa dan na san gaskiya ce nake fad’a. Bari kiji in fad’a miki abunda na San Baki sani ba.. idanuwanki ne suka kulle ba kya ganin komai ba kya ganin kowa sai k’iyayyar Huda da Aisha wadda kika gani abkan k’afafuwanta!” Da sauri Mammyn ta kalleta kafin tace “Magana zaki fad’amin? Me kike nufi? Use your words! Ta fad’i hakan tana me k’arasowa daff da ita. Mik’ewa Ummin itama tayi sannan tace “Ba zan yi using words d’ina ba Mammy dan na san kin san me nake nufi! So yanzu ba lokacin tashin tashina bane ba, yanzun lokaci ne wanda ya kamata ace kin farka idanuwanki sun bud’e sannan kin kalli rayuwa da idon gaskiya da basira. Bari in baki wani d’an misali , watak’il ki gane abunda kowa yake son fahimtar da ke wanda kika kasa nutsuwa ki fahimta.. For instance ace, ki samu kare ki kulle shi yayi kwanaki baki bashi abinci ba! Rana d’aya ki samu dogon lungu, a k’arshen lungun ki ajiiye nama da k’asusuwa da ruwan sha sannan ki kawo zarto k’usoshi da wuk’a ki ajjiye a daidai ta saman lungun a saman wannan naman sannan ki d’ana mishi tarkon da in dai yabi ta kai ya taka to wannan wuk’a da zarton zasu sauk’o su chakeshi su kasheshi murus har lahira ba tare da ya ci wannan naman ba.” Ajiyar zuciya Ummi ta sauk’e kafin tace “Ki gaya min in akwai mahaluk’in da ya isa ya hana wannan karen cin naman nan? Ko kuwa shin wannan karen zai iya hankalta da wannan tarkon da yake a gaban naman? Amsar anan itace ‘a’a’, sai dai In d’auke shi za ayi ta k’arfin tsiya a sama mishi sabon nama a bashi yaci. Sannan ne za a samu sauk’i. Wannan karen ba kowa bace face, ke. Naman nan kuwa, Hudan ce da Aisha waenda k’iyayyarsu haushi da takaicinsu ya sanya kika kasa ganin komai da kowa hatta tarkon dake gabansu wanda in dai kika taka to tabbas wuka zata fad’o kanki ta kashe ki har lahira ba tare da kin tab’a su ba! Waennan tarkon da wuka’ak’e ba komai bane Mammy face Dad da Arshaad da auren ki da mutuncinki da k’imarki, da kike k’ok’arin lalatawa ki kashe rayuwarki jin dad’in ki kwanciyar hankalinki da farincikinki da aurenki, duk akan rashin hak’uri. Second option kuma da na baki na ‘sai dai a d’auke karen a bashi sabon nama’ Shine wanda ni, y’an uwanki da Aaima muke ta k’ok’arin fahimtar da ke!. Idan kika yi hak’uri kika sawa kanki da zuciyarki salama, zaki samu peace of mind za ki samu farin ciki amman fa sai kin yi tunani irin na mutane bawai irin na karnuka da basa ji basa gani idan suna jin yunwa ba. Ki daure ki kwantar da hankalinki, wata rana sai labari. Kar kije maybe akwai babban rabo a tsakanin Hudan da Arshaad ki kashe kanki ba tare da kin hankalta ba...” “Attakhbir! Allahu akhbar! Mai k’aramar kwakwalwa da zuciya. Naji na gode reformed Zainab! Na lura tunda kika ji azabar cell shikenan zuciyar ta mutu. To bari kiji in gaya miki Wallahi! Kin ji dai na rantse gara rabon dake tsakaninsu ya kashe ni! Akan in zauna a gaban idona a d’aura musu aure inaji ina gani dan na tabbatar bak’in ciki ne zai k’arasa ni muddin Arshaad ya auri wannan Yarinyar!. Kinji dai kankat! Kenan, ko?. Oya jeki na gode duk ranar da fargabar cell ta bar jikinki, kya iya zuwa mu yi magana.” Cewar Mammy. Bak’in ciki ne ya hana Ummi sake ce mata komai, dan haka kawai ta juya ta fita cike da takaici da tsananin mamakin Mammy. Da harara Mammyn ta rakata, sannan tayi tsaki ta koma kan gadonta ta zauna. Ummi na fita suka had’u da Daddy da alama d’akin shi zai yi amman yana ganinta yace “ta zo suje ya kaita kawai ya gama tukun ya huta.” Ba ta san taya zata fuskanci Abba ba, bata san taya zata fara bashi hak’uri ba! Hakan yasa tunda taje ta yiwa su Granpa sallama suka d’au hanya zuciyarta take ta faman tsitstsinkewa..... Ba kowa a parlourn dan su Shuraim tun safe suka tafi gandun albasa. Basu dad’e da gama waya da Dad ba yace mishi yana gida don haka suna zama ya kirashi yace “ya sauk’o gashi ya kawo Ummi” Wallahi Abba har ga Allah har cikin zuciyarshi shi mantawa ma yake yi da wata Ummi. Mike’wa yayi kawai ya je jikin drawer inda yake ajjiye important documents d’inshi ya d’auko takardar da ya dad’e ajjiye da ita, ya fice yayi k’asa. Da kyar ya iya daurewa suka yi cikakkiyar gaisuwa shi da Dad. Ummi na shirin gaidashi da fara sake bashi hak’uri har da d’am zamowarta daga kan kujera taji yace “Ke! Zo ki karb’a nan” Ganin ya mik’a mata farar takarda ya sanya gabanta ya hau dukan uku uku! Ba ita ba hatta Dad sai da ya shiga rud’ani. Bata gama gigicewa ba sai da ya daka mata wata uwar tsawa! A take jikinta ya d’au rawa. Gudun kar ta b’ata mishi rai ya sa ta mik’e da kyar ta k’arasa inda yake tasa hannu biyu ta karb’a…. Dad ne yace “Abba meye wannan ka bata?” Yana mai tsareshi da idanu. Cikin nuna halin ko in kula yace “Ta karanta za ta gani” Da kyar Ummi ta iya bud’e takardar, jikinta na karkarwa tana adduar Allah yasa ba abunda take tunani bane… Zuwa yanzu ran Dad ya soma b’aci da attitude d’in Abba dan haka cikin b’acin rai ya yunk’uro da niyyyar fara zazzzage mishi ta cikinshi dan yaga alamun da renin wayo ya sauk’o k’asan shi kuwa yadda Mammy ta gama chaza mishi kai wallahi ba Abba ba ko waye ya shigo gonarshi yau sai ya ci ubansa! Ya bud’e baki kenan, yaji k’arar fad’uwa! Da sauri

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});