Chapter 61
Chapter 61
har k’asa ya gaida su Mama, shima (Arshaad) d’in d’an rissinawa yayi ya gaidasu, daga nan suka d’an zauna. Kafin daga baya suka mik’e suka ajjiye musu jibga jibgan ledojin da suka shigo musu da su, suka yi musu sai da safe… Ummu ce ta cewa su Sakina “su tashi kar ayi ta jiran su” da kyar suka fita tare da su Arshaad da alk’awarin gobe da sassafe za su dawo!. Sai da suka fita tukun suka ga ashe har da Abba aka zo. Ita da Sakina ne suka shiga motar Abba, Arshaad kuma suka wuce shi da Auwal. Suna yin parking Sakina ta bud’e ta fara fita bayan ta yiwa Abban sai anjima, Hudan na shirin fita Abban yace mata “Ya jikin Maman naki?” A hankali tace “da sauk’i”. Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “Arshaad yace har da karaya ko?” “Eh” Ta bashi amsa. Cikin d’acin zuciya yace “na yiwa Mamanki laifi! Na saka polisawan wajen da akai kai Mijinta sun yi mishi duka bana wasa ba! Wanda shima hakan da nayi na san maybe idan taji labari zata iya jin haushina! But maza irin Usman irin haka ya kamata a dinga yi musu. Inaso in cire hannuna akan case d’in amman sam na kasa Hudan ban san mai yasa ba. Wallahi da ace ina da hali ko inda Maryam tabi Usman bai isa ya taka ba! Amman k’addara ta riga fata, kuma ance ba a shiga tsakanin Miji da mata, sam.” Shiruuu, Hudan ta d’anyi, tana son gaya mishi amman kuma sai taji ta kasa. Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace mata “Good night, kije ki huta kun sha jigilar asibiti.” A hankali tace “good night Abba” ta fice. Sun dan tab’a hira kad’an a parlour da Arshaad sannan ta sallameshi ta bashi sak’on Mommy, ta nufi d’aki a ranta tana mamakin yajin da Aslam yayi musu, lokaci d’aya kawai ya d’auke k’afa!. Har ta haye bata ga shigowar Abba ba kuma ta san ba fita yayi ba. Ya dad’e a mota, kafin da kyar ya samu ya fito ya shiga ciki yana ganin dishi dishi tsabar tashin hankalin da b’acin ran da yake a ciki, ya rasa me zai yiwa Usman ya huce takaici da bak’in cikin da yake ji….. Sai da su Hudan suka zo kwanciya tukun take gaya mata yanda suka yi da Abba d’azun sannan a hankali ta d’aura da cewa “bana son had’awa Mama case biyu shiyasa na k’i ce masa komai” Murmushi Sakina tayi kafin ta kamo hannuwanta duka biyu tace “Ki yi tunani, duk abinda kika ga ya dace, kiyi musu.” Da sassafe ta tashi ta shirya, tana shirin zuwa side d’in Abba taga call d’in Arshaad, sai da ta d’anyi jimm!! Tukunna ta amsa ta gaidashi. Cikin kulawa da so ya amsata kafin yace “ta sameshi a k’asa” Tare suka sauk’a ita da su Shuraim waenda za su school. A parlourn ta tsaya tayi musu a dawo lafiya, sannan ta k’arasa inda Arshaad d’in yake zaune. “Za ki fita ne? Naga kin shirya da sassafe” Yace yana kallon ta. A hankali tace “eh, amman sai wajen 9 yanzun ina son yin magana da Abba ne” Cikin bata dukkannin attention d’inshi yace “Exactly abunda ya kawo ni kenan. Did you tell him? I’m sorry na san bai kamata in yi miki wannan maganan ba but naga kamar Abban is disturbed, na dad’e ban ganshi a wannan yanayin ba. Me kikayi deciding? Za ki fad’a masa ne?” Ya jero mata tambayoyin yana mai tsareta da ido. Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin tace “jiya dai ban gaya mishi ba, but yau na yi deciding in fad’a mishi d’in, duk da ban san ya zai yi handling abunba, and I’m not even sure they still want each other back.” Murmushi Arshaad yayi kafin yace “Believe me they do! Amma kin tabbatar this is the right time? After all that has happened especially ma a ita Maman” A hankali Hudan ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace “I’m sure. Na riga na gama deciding” Murmushi Arshaad d’in yayi sannan yace “Ok dear. Allah ya taimaka, ya sa a dace.” “Ameen” tace. Yana d’an murmushi ya mik’e yace “Anjima idan na koma gida na d’an shirya zan zo asibitin in shaa Allah.” “Allah ya kai mu” tace. Kafin daga nan suyi sallama ya wuce office ita kuma ta nufi side d’in Abba..... A bakin k’ofar parlournshi ta tsaya ta d’anyi knocking jin shiru yasa ta tura ta shiga. Ba kowa, dan haka ta nufi bedroom. Ta jima tana knocking tukun chaan, taji ance “come in” A hankali ta tura ta shiga, da alamun tun d’azun a balcony yake dan yanzun taga yake shigowa cikin d’akin. Yayi mamakin ganinta da sassafe, dan haka suka fito parlourn suka zauna kafin ya kalle ta yace “Ya aka yi dota?” Kame kame ta fara yi, dan bama ta san ta Ina zata fara ba sai yanzu ta d’anji nauyin shi da nauyin maganar da ke tafe da ita! Chaan! Dai ta dake ta d’an sunkuyar da kanta k’asa tace “Daman, Baban ma na ji Ummu tace ya yiwa Mama saki d’aya shekaran jiya, jiya kuma tayi miscarriage” Tana gama fad’an haka tayi saurin sake sunkuyar da kanta k’asa tana ci gaba da wasa da y’an yatsun ta. Ta kusan minti biyar a haka, jin shirun yayi yawa yasa ta d’ago kanta ta d’an kalleshi, yana a yanda ta barshi idanunsa a kanta amman daga gani hankalinshi baya kanta. Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “Hudan, are you sure?”. A hankali ta d’aga kanta kafin tace “Very sure”. Ajiyar zuciya ya sake sauk’ewa kafin yace “Thankyou! Za ki iya tafiya” A hankali ta mik’e tayi mishi sai anjima ta fita. Su kad’ai suka yi breakfast d’insu, daman a shirye suke, dan har handbags d’in su sun sauk’o dashi, Hudan ta zaro waya zata kira drivern kenan Abba ya shigo shi da Daddy…. Wani dark ash d’in yard ke jikinshi anyi masa d’inkin kaftan! Kyalli da taushin yadin kad’ai ya isa ya sanya ka gane kud’insa ba na wasa bane sannan daga ganin d’inkin ka san ba a k’asar nan ma aka yishi ba. Ya murza bak’ar hula da bak’in takalmi…. Yayinda Daddy yake sanye cikin suite maybe office yake shirin wucewa. Gaisawa suka yi. Cikin kallon agogon dake d’aure a tsintaiyar hannunshi Daddy yace “dota ku yi sauri mu wuce ko?” Mikewa suka yi Sakina tace “mun ma gama” suka gyara zaman mayafansu. Su Abba ne suka fara fita sai su. A motar Abba suka tafi Daddyn yana binsu a baya. Bayan sun shiga asibitin an yi parking, Hudan tana shirin tamabayar Abba ‘k’arfe nawa za azo a d’auke su’ taga shima ya bud’e motar yana ce mata “ta zagayo tayi leading way d’in” Bayan ta fita sun zagayo, Sakina tayi k’asa da murya tace mata “Ashe yau Abba zance zai zo shiyasa naga ya ci kwalliya” Da sauri Hudan ta mintsineta tana d’an juyawa dan taga ko attention d’in Abban yana a kansu..Magana taga suna yi shi da Daddy wanda ya fito daga mota dan haka ta d’an sauk’e ajiyar zuciya kafin ta jaa hannun Sakina suka yi gaba.. Abba na da ji sosai shiyasa sarai ya ji
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96