Chapter 54
Chapter 54
Mommy. Auwal ma ganin yanata zama shi d’aya yasa ya yiwa Abban sai da safe ya tafi, bayan yaga sauk’owar Sakina. A tare suka fito shi( Auwal ) yayi part d’insu su kuma suka wuce mota Sakina na baya Hudan na gaba a haka har suka isa bakin k’ofar gidan Baba. Ba Hudan ba hatta Sakina zumud’i take yi.. Cikin rawar k’afa suka fita a tare suka shige gidan. Basu tarar da mashin d’in Baba a soro ba, da alamun bai kai ga dawowa ba. Gidan shiruuuu, sai d’an hasken fitulu da suke hangowa ta d’akin Umma da Mama. A hankali Huda tasa hannu ta d’an tura k’ofar kafin su shiga a tare da sallama… Kendir d’in dake kan dressing mirrow ne ya taimaka wajen haskaka d’akin! Tana zaune a k’asa gaban gado kan sallayarta, da charbi a hannunta, da alama bata tashi daga wuridin bayan Isha ba dan ga hijabinta ma a jikinta, a gefe guda kuma ta kunna maganin sauro yana d’an tashi da kad’an da kad’an. D’ago fuskarta tayi ta kallesu, kafin ta maida idonta k’asa kamar bata ga kowa ba!. Gaba d’aya jikinsu sai yayi sanyi, amman suka aro jarumta suka k’arasa inda take! Sakina ce tayi k’arfin halin hugging d’inta kafin tace “Mama Ina wuni ya jiki?” “Alhamdulillah” kawai tace Maman tace mata. Itama Hudan ta gaisheta ta bita da “Alhamdulillah” Sannan ta mik’e ta cire hijabin jikinta ta ninke da sallayar, ta mik’e ta haye gado ta kwanta abunta. Duk kasa cewa komai suka yi, d’akin ya d’auki shiruuuu. Wajen minti goma ta tashi taje ta kashe kendir d’in ta dawo ta tofa addua ta kwanta, harda d’an jan abun rufuwa. Sheshshek’ar kukan Huda ne ya sa Sakina kunna flash d’in wayarta! Itama Mama jin kuka yasa ta mik’e ta zauna daga kan gadon tana kallonsu a inda suke. A hankali Sakina ta cewa Mama “Mama dan Allah ki yi hak’uri mana.” Cikin katseta Maman tace “Hak’urin me?” Dibi dibi Sakina ta hau yi kafin ta samu damar cewa “Naga kamar kina fushi da mu ne” Murmushi Maman tayi kafin tace “ba fushi nake yi ba Sakina, ko kad’an bana fushi daku Kawai kun zab’i abunda kuka ga ya dace ne Nima kuma na zab’i wanda naga ya dace!” Ajiyar zuciya ta (Mama) sauk’e kafin ta juya kan Huda tace “Na san abunda kika yi ranar da kika zo duba ni a asibiti! Dukda Ummu taso b’oyewa amman naji kuma na fahimta! Na gode Hudan, Mahaifin ki ya fini ko? Ba komai.. Amman abunda nake so ki fahimta shine Tunda shi kika zab’a, to ki zauna a iya shi kad’ai kar in sake ganin k’afar ki a inda nake! In ba hakaba wallahi sai ranki ya b’aci! Na bar masa ke! Tunda naga a ganin ki yanzu ban dace ki zauna da ni ba, kin girma ko? Kin mallaki hankalin kanki, so bani da wani amfani a wajen ki, tunda ba abunda zan iya miki ko zan iya baki..” Wani irin kuka Hudan ta rushe da shi, tana shirin yin magana Mama ta katseta ta hanyar cewa “Haka ne mana, kar ki min kuka gaskiya na fad’a! Kinyi girma ai yanzu tunda har kika iya yankewa kanki decision..” Sakina ce tace “Mama dan girman Allah kiyi hak’uri, wallahi kin yi misunderstanding d’in mu ne Please Mama ki tsaya ki fahimcemu” “Hmmmm” Maman tace, kafin tace “Nima kun kasa fahimta ta Sakina ba wai haushi naji ba fa, kawai ina baku space d’in da kuke buk’ata ne, tunda gashi ta nuna min k’iri k’iri abubda ranta yake so ai kinga sai in barta in daina kutsa kaina cikin rayuwarta ko?? Ku tashi kuje dare yayi, na san yau ma yana waje yana jiranki! And maganar zuwa kotu itama na daina yi! Tunda gashi k’iri k’iri kin riga kin zab’i abunda kikeso, so ba amfanin zuwa kotun tunda babu amfanin inje inata yak’i ni kad’ai. Sai kuje ku yi ta rayuwarku mai dad’i cikin daula ke da Mahaifinki.” Tana gama fad’in haka ta koma ta kwanta abunta. Kusan 20 minutes suna bata hak’uri, amman tak’i kulasu Sai da suka kaita bango ta tashi ta balbalesu da fad’a tace “wallahi In basu fita ba zata dake su! Su bar ganin wai sun girma.” Mik’ewa Hudan tayi kamar zata fita, sai kuma ta koma da gudu ta je ta kanainaye Maman tace “Ni ba inda zan je, dan Allah ki daina fushi dani haka, ba zan sake komawa ba, anan zan zauna.” Kasa cewa komai Mama tayi.. Suna a haka wayar Hudan ta fara ringing, har ta tsinke ba wanda yayi yunk’urin d’aukar wayar… Sai da aka sake kira, tukunna Sakina tayi k’arfin halin d’auka ta d’an fita waje, ta fad’awa Abban halin da ake ciki “Sai da safe” kawai yace mata, daga nan ya kashe wayar! A chan d’aki kuwa, da kyar Mama ta d’an kulasu.. Sai da Hudan tayi mata alk’awarin ta bar zuwa gidan Abba har abada sannan ta d’an sauk’o…. Daga Hudan har Sakina, gabansu fad’uwa yake yi dan basu san ta inda zasu fara yi mata bayanin baikon Hudan da sa ranar da aka yi ba! Chaan dare! Kowa ya kasa bacci sai juyi suke yi, Mama ta hango kendir d’in d’akin Umma a kunne, ita tama yi tunanin ko tana d’akin Baba ne tunda ita ke da girki, gudun kar ya k’are ya kama wani abun yasa ta cewa Sakina “taje ta kashe mata kendir d’in, in k’ofar a bud’e take.” Tun daga bakin k’ofar d’akin Sakina fara jiyo gwarti! Tsaki tayi ta d’anyi sallama kusan sau uku, jin shiru yasa ta d’an tura k’ofar ta shiga… Kendir d’in saura kad’an ya k’are, dan ba don ta je ba ma to da babu abunda zai hanashi kama kan mudubin katakon d’akin, dan Umman bata d’aurashi akan komai ba kamar yadda taga Mama tayi ba. Kallonta tayi dariya taso kufce mata, da sauri ta hure kendir d’in ta fito ta maida k’ofar ta rufe ta wuce a ranta tana mamakin rashin hankali jahilci da rashin sanin ciwon kai irin na Umma! Ace y’arki tana nan da ciki a chan wani gidan da baki san ko su waye ba! Amman kalli yanda ta barrarraje tana shek’a uban bacci kamar wata jaka! Da wannan tunanin Sakina ta k’arasa d’aki ta tarar bacci yayi nasarar d’auke Hudan, daman ita bata da wuyar bacci. Itama Sakinan bata wani dad’e ba baccin ya d’auketa cike da tunanin rashin man kai irin na Umma…inda ace su Ummu ne akace d’aya a cikin ita ko Huda bata gida ta tabbatar ko gigin yin bacci ba zasu yi ba!….. Abunda Sakina bata sani ba shine Umma magani mai k’arfin tsiya ta sha, dan yau kusan kwananta uku bata iya bacci tun lokacin da Jalila ta gaya mata Huda cousin d’in Arshaad ce! Ga kuma Mahaifinta yana son ta harma sun bar gidan kakan da shi da yayanshi duk akan Huda! Yau kuwa da Jalila ta kirata take shaida mata irin daular da Hudan take ciki sai da ta kusa hauka! K’arshema dishi dishi ta fara gani! Ga zuciyarta tana ta bugawa da mugun k’arfi ga zazzab’i. Don haka ta lallab’a taje wani Chemist a chan bakin titi babba da aka bud’e
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96