Chapter 88
Chapter 88
Anty Zainab da Umma suka samu suka iya zama…Umma so take yi ta sake mik’ewa tsaye tace “To Ina y’an unwan Ango!?” ta sake creating scene amman sam ta kaasa dan in banda dishi dishi babu abunda take gani! A ranta ta shiga aiyyana …..Tabbas sai taci uwar malan ado! Wallahi sai ta saka an yi mishi yasin mai walk’iya! Ba Malami ba ko uban waye shi. Kuma sai ya bata kud’inta. Jiya jiyan nan fa ta sake komawa wajenshi dan ta sake nanata mishi, shi kuma ya tabbatar mata da “babu aure tsakanin Hudan da Arshaad ya riga ya gama aiki kuma ya buga k’asa ya tabbatar ba Mijin ta bane ba sannan ya ingiza zuciyar iyayen shi (Arshaad) ya rura wutar k’iyayyar Hudan a cikinta ta yanda ba zasu tab’a bari ayi auren ba musamman ma Mahaifiyarshi (Arshaad)…” Amman kalli yadda Maman nasa taketa jan Hudan a jiki, anyi musu hoto yafi kala nawa tare sai faman fara’a take yi tana washe baki kana ganinta ka san tana cikin tsantsar farin ciki….Inaaaaa!!!!! Taya ma zata tsaya ta yarda Hudan ta auri wannan No1 kyakkyawan da ita tunda take a rayuwarta ko a telebijin bata tab’a ganin mai kyawunsa ba! Ga uban kud’i ga kyau kamar aljani Allah sarki Jalilan ta dole ta mutu akan soyayyar Arshaad, ai kuwa idan zata yi yawo tsirara wallahi sai ta raba auren Huda da Arshaad ko sama da k’asa zasu had’e Wallahi sai dai in rabo ya kasheta akan dai ta zauna ta nad’i wannan abun takaicin da ta san k’arshe in dai bata d’auki mataki ba to shine ajalinta! Kuma ko yana so ko baya so sai ya auri Jalila! Wannan alkawari ne ta d’aukarwa Jalila da ita kanta! D’an halal ka fasa…….. Anty Zainab ce ta tab’o ta wanda hakan ne ya katse mata tunani. Da kyar ta iya motsa wuyanta dan ji take kamar ba jini da rai a dukkannin ilahirin jikinta Suna had’a ido taga itama Anty Zainab d’in idanuwanta sun kad’a sun yi jazir! Kafin Umman tace wani abu taji tace “Sadiya taso mu tafi, kai na ciwo yake yi min” Suna shirin mik’ewa suka fara jiyo gud’a daga parlourn Madu sai a sannan ma suka lura Shuwa da Baaba Talatu da wasu y’an tsirrun mutane basa wajen A bakin matan wajen sukaji an fara k’us k’us d’in “Ashe tun d’azu mazan gidan Ango suka zo sun kawo lefe yanzu suka wuce da yake falon Madu yana da k’ofar shiga da fita ta waje, shiyasa har suka zo suka tafi ba wanda ya sani Sai da suka tafi yanzu akace aje a fito da shi” Sunaji anata k’usk’us d’in “ai motocin da suka zo da su ma kansu abun kallo ne! Gasu kana ganinsu kaga manyan mutanen da kud’i ya zaunamawa” Da kyar Umma take iya jan numfashi, dan ji take yi gaba d’aya iskar wajen bata isarta!. Ummu ce ta d’an matsosu kafin tace “Umma kuzo muje a fito da lefen nan kowa ya gani ko?” Anty Zainab ce ta iya ce mata “eh” Itanma da kyar, daga haka ta mik’e ta d’an dafa Umma kana tace “Muje Sadiya” Da kyar ta iya mik’ewa k’afafun ta suna rawa suka jera ita da Anty Zainab suka bi bayan Ummu suka yi parlourn b’aki. Mutane kam wasu basu ma samu damar shiga ba dan akwatunan sun cike parlourn tap! Ganin kowa cirko cirko a tsaye iya y’an k’alilan kuma na a ciki suna mik’owa ana fitowa da shi ne yasa suma suka ja suka tsaya a gefe kai kana ganinsu ka san basa cikin hayyacin su.. Ta gabansu aka fara wucewa da akwatuna nan kuwa suka maida hankali suka hau k’irgawa! Ana wucewa da goma Umma ta nemi d’an dakalin slop ta zauna dan jiri ne taji yaana d’ibarta ba na wasaba! A tunaninta su kenan amman ga mamakinta sai taga ana ta sake fito da wasu! Ganin ta k’irga ashirin da d’aya basu k’are ba ya sanya ta janyo Anty Zainab wadda itama tayi mutuwar tsaye kafin tace “Zainab zo mu bar wajen nan, tabbas kwakwalwa ta ta d’an samu matsala sannan bana gani sosai! Gani nake yi anata wucewa da akwatuna fa har yanzu basu k’are ba.” Da sauri Anty Zainab d’in tad’an dafa ta dan yanda take magana da sauri kuma da k’arfi kamar wata zararra ya sanya mutane har sun fara d’an juyowa ana kallonsu. A hankali tace mata “Ba idonki bane! Ashirin da hud’u ne cass! Gasu chan ragowar ukun Sai kuma waenchan baskets d’in da ban san na menene ba” Bata ida rufe bakinta ba aka fara fito da na Gwaggo da Kawu. Ai kuwa Umma bata san lokacin da ta mik’e tsaye ba tace “Amman dai Maryam sayar da y’ar nan tata tayi ko!? Haba mana wannan abu kuma ai ya zama hauka! Meye hakan? Me sukeso su nuna?” Cikin takaici Anty Zainab tace “Wallahi Sadiya za kiyi hanyarki nima inyi tawa har a tashi daga bikin nan gaskiya! Maganar Allah kenan, haba mana! So kika mu zama abun kwatance? Sai wasu abubuwa kike yi kamar tab’abb’iya? Kiyi controlling kanki mana Haba?” Ta fad’i hakan tana mai wucewa ta barta a tsaye nan dan a yanda take jin zuciyarta yanzu, tsaf zata iya sauk’e ruwan bala’i da fushinta akan matan dake k’ok’arin maidasu telebijin…. Sai da Umma taga an gama fito da kayan an watse daga wajen sannan ta samu da kyar taja y’an k’afafuwanta ta isa harabar tsakar gidan. Banda gud’a da hayaniyar mata ba abunda yake tashi A lokacin har an bud’e akwatunan farko an fara dubawa…. Sai a sannan ne Aslam ya samu ya tatttaro nutsuwar shi da d’an ragowar kuzarinsa ya mik’e tsaye! Yana mik’ewa Ummu da Mommy suka k’arasa wajensu.. D’an b’ata rai yayi kafin yace “Mommy zan wuce wannan bidi’ar bada ni ba gaskiya” Murmushi Mommy tayi ta shafa kanshi kafin ta juyo ta cewa Ummu “Zai iya tafiya?” Murmushi Ummun tayi kafin tace “eh, zai iya ai an gama komai” A hankali yace mata “Sai anjima” Cikin kulawa tace “Mun gode kwarai Aslam, mun gode.” Ajiyar zuciya kawai ya sauk’e daga nan ya ajjiye sandar hannunshi a gefe ya juya dai dai nan su Sudais suma suka mik’e Shuraim yana ta b’ata rai shi ala dole ya gaji.. Ummu da Mommy ne suka yi musu rakiya har waje, shi da Sudais da Shuraim bayan ya kira drivern da zai maida Mommy gida yace masa ya taho yanzun… Mutane in banda kallonsu ba abunda suke yi sunata yaba kyawun Angon Gashi bai wani zak’e ba irin yanda Angwayen yanzu suke yi! Instead shi ya kama kanshi matuk’a, hakan kuwa ba k’aramin burge jamaar wajen yayi ba. Su Mommy suna komawa suka tarar anata ware lefe an yi filla filla ana gani… Tun daga kan atamfofi Umma ta raina kanta… Zata iya cewa tunda Laraba ta kawota duniya bata taba shiga tashin hankali irin na wannan lokacin ba! Hankalinta bai gama tashi ba sai da aka zo kan akwatunan jewelry’s kit kit waenda aka ware guda biyu aka shak’e taff da sark’a da y’an kunne Na farkon fashion ne Na biyun kuwa gold ne zalla! Matar dake gefen ta ce taji tana cewa “Ai dama su
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96