Chapter 56
Chapter 56
kafin ya fara magana “Shikenan zamu gwada mu gani, amman idan mun yi nasara kin dawo wajen Maman naki to inaso kisan cewa Ba a inda take zaki zauna ba sai dai ki zauna a gidana! Saboda Usman ba zai tab’a bari ki ci gaba da zama nasa a gida ba sannan na san ba zai dinga barin itama Maman naki tana zuwa inda kike ba kwata kwata kinga kenan baki zauna da Abba ba kuma baki zauna da Mama ba!” Cikin kuka Mama tace “Abba dan Allah ka dai na, za ka karya mata guiwa” Murmushi ya sake yi kafin yace “Maryam hakan shine gaskiya! Kuyi hak’uri, for the first time nayi miki alk’awari ban cika ba! In dai zan fad’a miki ki ji, tou inaso dan Allah ki bar Yarinyar nan ta koma wajen Mahaifinta kamar yadda ya buk’ata, ko munje kotu ya fimu gaskiya, kuma rashin hankalin da Usman ya sake yi yau d’innan ma wata shaida da point ne Abba ya sake samu. Ki barta ta tafi, za ku dinga waya sannan yace anytime kike son ganinta kije ki ganta, idan ma bakya son zuwa gidan nasa to zai saka ko driver ne ya kaita ko wani park ko restaurant, ku had’u achan amman yace ba zai sake barinta tazo inda kike ba! Har ga Allah Maryam, Abba is trying to be just here.” Da sauri ta d’ago tana kallonshi da jajayen idanunta. D’aga mata kai yayi alamar gasgata mganar shi, kafin Baba Bashir ya d’aura da cewa “Maryam har yanzu zuciyar ki a k’ulle take da zafin abunda Abbas ya aikata miki, shiyasa ba za kiga abinda mu muka ganiba, wanda muma a da bamu ganshiba sai bayan da muka yi k’ok’ari muka goge takaicin shi daga idanuwanmu.” “Mune muka haifeki, baki da masu fad’a miki gaskiya sama da mu, ki tashi ku tafi suyi miki kwatance ki kaisu ki dawo, dama haka rayuwar take, ba komai kake kwallafawa rai kuma ka samu ba, ki bari ko nan da wata biyu ne haka, sai a san abun yi kinji? Yanzu kuje kawai.” Hudan ke kuma idan kin koma, ki san yanda za kiyi mishi magana a samu ya saki Babanku Usman kinji?” Cewar Shuwa. A hankali Mama ta rintse idanuwanta wasu zafafan hawaye suna zubo mata! Ta manta rabon da Shuwa tayi mata magana mai tsayi haka. Bata dawo daga duniyar tunanin da ta tafi ba, taji Sakina ta furta wasu maganganu da suka girgizata matuk’a! Wai “An saka ranar Huda nan da wata biyu da Arshaad!!” Ba Mama kad’ai ba, gaba d’aya parlourn shiru ya d’auka! Chaaan! Shuwa tace “Allah ya sanya albarka” Da sauri Mama ta kalle ta da idanunta hawaye shab’e shab’e! Kasa jurewa Shuwan tayi kawai ta mik’e ta kama hanya ta fice… Baba Bashir ne yace “ku tashi kuje Maryam, za muyi wannan maganar wata rana!” Cikin kuka Mama tace “Kaka, Abba Naji zan barta ta koma amman dan Allah kar ku saka na maida ita, ba zan...” Kukan da ya kufce mata ne yasa ta kasa ci gaba da magana ta mik’e ta fice tayi cikin gidan… Baaba Talatu ce ta bita domin lallashin ta. Wannan shi ake kira isa da mallaka!!! Tayaya zaka sa ranar Yarinya ba tare da tuntub’ar Mahaifiyarta ba? Saboda Allah fa!. Shiruuu, parlourn ya d’auka, chaan Kaka yace “su mik’e su kai su” Ita Sakina tausayi ma y’an tsofaffin suke bata, sun tsufa amman har yau basu huta ba, bayan jigilar case d’in y’an unguwa ga na family…ta tabbatar yanzu suna maida su, police station zasu wuce, akan case d’in Baba……….. A k’ofar tafkeken mansion d’in da suka isa da taimakon kwatancen Sakina suka yi parking, daganan suka yi musu sallama, da d’an Guntun maganganu tukunna suka wuce, su kuma suka shige ciki. A parlourn suka tarar da Abba, Daddy har Dad da Arshaad! Da alamun maganganu suke yi masu mahimmanci. Yadda Hudan ta baro Mama tana kuka yasa ta d’an ji zafin Abba! A hankali suka gaidasu, bayan sun amsa bata tsaya ba kawai ta haye sama! Har sai da Sakina ta d’an yi mata magana bayan sun hau, dan taga kamar basu ji dad’in yadda tayi musu d’in ba. Ko lunch k’in sauk’a tayi, ba yanda Sakina batayi da ita ba amman tak’i sauk’a, gashi Abba sai kira yake a waya tana amsawa tana cewa “Huda sallah take” Kamar minti ashirin haka, suka ji knocking. Sakina ce tace “Come in” A tunanin ta ko maid aka turo ta kawo musu abincin. Turo k’ofar yayi ya shigo, Sakina bata san lokacin da ta fara dariya ba ganin Abba ya shigo har da hular kuku a kanshi da basket d’in abinci a hannunshi. Harararta yayi, ya d’aura yatsanshi akan lips d’inshi alamun tayi shiru! D’aga hannuwanta sama tayi tana gimtse dariyar tata, sannan ta mik’e ta fice da sauri. Sai da ya ajjiye kular, sannan yace “princess” Shiru tayi still tana kwance ta bawa k’ofar baya. Chan taji yace “Hudan” A hankali ta mik’e ta zauna ta juyo tana goge hawayenta, fuskarta tayi jaaa alamun taci kuka, over!! Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya zauna a bakin gadon, yayi hugging d’inta ya fara lallashinta ai kuwa kamar jira take ta saki kukan babu control. Bai hana ta ba, sai da ta gaji dan kanta tayi shiru tukunna a hankali yace “sorry dota, i’m really sorry, ok?” Cikin sheshshek’a tace “Abba Mama na da bp, yanda na baro ta tana kuka, Allah zai iya tashi?” Murmushi yayi yana sakinta kafin ya gyara zamanshi yana kallon k’ofar fita tukun yace “Hudan, na fiki jin zafin kukan da Maman ki take, please don’t question my decision, it’s the right thing.” Ahankali tace “Amman Abba pls...” “Shhhhhhh” Yace ba tare daya kalleta ba, kafin ya juyo ya fara k’ok’arin zuba mata abinci. Omelet d’in da ya soya mata ya saka a gefe, da pizza slice uku da ya d’auko. Da farko k’in ci tayi sai da yayi dagaske, tukun ta d’an karb’a. Bayan ta gama ta sha ruwa, ya d’an dunga janta da magana yana ta faman lallashinta. Hudan bata iya dogon fushi da mutum ba, don haka ta d’an sauk’o, hakan kuwa yayi matuk’ar ragewa Abba kusan 20% na damuwar da yake ciki shiyasa da ta rok’esa akan ya saki Baba ba don halinsa ba sai dam kakanninta da hankalin su yake a tashe! Abban ya amince, a take ma a gabanta yayi waya yace a sake shi. Ta ji dad’i sosai kuwa. Daganan suka d’an ci gaba da maganarsu. Hammar da yaga tanayi ne ya sanya ya fahimci bacci take ji, dan haka yace mata “ta kwanta” Bata yi 10 minutes da kwanciyar ba ta fara bacci…. Ahankali yake kallonta yana tunani kala kala… Sai bayan kusan 1 hour tukun ya rage mata k’arfin ac ya lullub’eta da bargo, sannan ya fita da kayan abincin............... A chan parlourn k’asa kuwa, sam Sakina bata lura da Auwal wanda ya daya dawo break ba, sai da ta kusan k’arasawa dining d’in! Tun kusan sauk’owarta yaji a jikinshi! Addua yake Allah yasa itance, don haka ya k’urawa stairs d’in ido… Ba a hankali take tafiyarta ba ba kuma da sauri ba! Da d’an murmushi a kan fuskarta. Gaba d’aya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96