Chapter 40
Chapter 40
Hudan ba zata auresaba!’ Wai wanne irin rainin wayo ne ma wannan Abba yake yi wanda kika kasa fahimta??? Kina ganifa yadda muka taso muka sha wahalar rayuwa tare, bai tab’a ko da lek’en ta ba, sai yanzu data zama mutum tukunna shine zai nuna ya santa? Inace daa cewa yayi ‘kar ma in fad’a mata sunanshi?’.” Dafe kai Ummu tayi tana shirin yin magana Huda tace “Mama da gaske yake tun ranar anan ya fad’a miki ‘bai san da ni ba!’ Kuma dagaske yake.” Cikin jin haushi Mama tace “k’arya yakeyi!! Na fad’a na sake maimaitawa ‘k’arya yake yi!’ Kinji mai uba! To nuna min shine ya haifeki kinji Huda, hakan yayi kyau! Wato d’an kwana biyun da kika yi tare dasu har an juya miki tunani akaina ko? Bilkisu kinga irinta ko? Ina kuma ga in na barta ta zauna dasu gaba d’aya? Hudan fa ita kad’ai Allah ya bani, amman kalli mugu Abba abinda yayi a cikin kwana biyu kawai!!.” Ta k’arashe maganar tana fashewa da kuka. Da sauri Hudan ta hau lallashinta sannan ta fara basu labarin yadda akayi da Mom da su Ummi da Mammy, har cell d’in da suke ciki a yanzu…. Ummu wani sanyi da proud na Abba take ji, kuma ta sake amincewa zai kula da Huda iya iyawarshi kuma zai yi duk iyakar bakin k’ok’arin shi wajen bata kariya. Amman wani abun mamaki furr!! Mama tak’i amincewa da zancen tace “Makirci ne suka k’ulla da shi da y’an uwan sa, aka yi komai a gaban Huda dan ta yarda dashi asa ta juya mata baya!” Ba Ummu ba hatta Sakina da Huda da basu da shekaru sosai, sai da suka tsorata da lamarin Mama, ga gaskiya nan ana nuna mata amman ta kafe! Tak’i ji taki gani.. Ummu har ce mata tayi “zata je suyi maganar fahimta ita da Abba, ba sai anje kotu ba! Kawai Huda za ta dinga sati sati a hannunsu, har Allah ya kawo mata miji tayi aure Ma’aana taje Gandu tayi sati d’aya sai ta koma Nasarawa tayi sati daganan ta sake dawowa Gandu….haka dai.” Amman nan ma furr!! Mama nace akan ‘attakafur!! Ita sai dai a bata Huda gaba d’aya!’ K’arshema cewa tayi “idan Ummun ba zata tsaya mata ba ta daina yi mata kwana kwana kawai ta fito fili ta fad’a! Ta samu ta fara neman wani lawyer d’in, tun kafin lokaci ya k’ure mata.” Da jin hakan ne yasa Ummu taja bakinta tayi shiru bata sake cewa komai ba! Daganan shiru ya wanzu a wajen…. Hudan ce ta kawo k’arshen shirun ta hanyar cewa “Ya Jalila ma tana gidan” Da sauri duk suka zuba mata idanu… Cikin In Ina tace “Ciki ne ma da ita” A firgice Sakina ta rafka salati haka ma Ummu Mama kuwa daman ta riga ta Sani, amman abunda ya bata mamaki shine ‘me take yi a gidan su Abba’. Ummu ce tace “Me take yi kuma a gidan?” Shiruuu, Hudan tayi, bata san daliliba amman sai ta kasa ce musu cikin na Arshaad ne kawai tace “itama bata sani ba” Tana goge wani hawaye mai zafi daya zubo mata ba tare data bari sun gani ba, kafin ta k’ara da cewa “A gidansu Ya Auwal dai ta ganta, kuma yanzu da suka tashi, Ya Auwal d’in ya kaita wajen Gwaggo Asabe.” Ajiyar zuciya Ummu ta sauk’e kafin tace “Sadiya ta cuci Yarinyar nan har abada wallahi…” Cikin sanyin murya Huda tace “Ummu nace mata ta kwantar da hankalinta zan nema mata mafita, ya za ayi yanzu? Dan wallahi naji tausayinta..” Da sauri Mama tace “Wacce mafitar za ki nema mata?? Meye naki a cikin lamarin ciki, iye?” Ta k’arashe maganar cikin fad’a! Sannan taci gaba “Kin san Allah Huda babu ruwan ki a cikin lamarin nan, mafita Sadiya ta nema mata, wannan maganar tafi k’arfin ki kar inji kar in gani! Ballanta a tsunduma ki a cikin lamarin a yi miki bak’in fenti ke daman mai bak’in jini a idonsu…” Hawayen Hudan ne ya k’aru, ta sa hannu ta shiga gogewa.. Ita kad’ai ta san kalar tuk’uk’in da zuciyarta take yi mata, kawai tunowa da lamarin cikin da tayi And Tana mamakin masifar da Maman nata ta koya.” Ummu ce tace mata “kin dai ji ko Huda? Ki bita da addua kawai, Sadiya ta fiki sanin kalar taimakon da zata yi mata, ba ruwan ki! Dan yanzu za a goga miki fenti taki sai tafi ta kowa tsami!” Cikin katseta Mama tace “Ai gashi irin tarbiyyar Abban da kuke magana akai!! Yanzu kamar Hudan har tana shiga lamarin ciki tana alk’awarin zata nemawa mutum mafita sai kace wata nurse??!” Ajiyar zuciya Ummu ta sauk’e sannan tace “Ki kwantar da hankalinki, ai taji abunda muka ce mata ko Huda? Besides ai basa tare ma yanzu, naji tace tana wajen Gwaggo Asabe ko? Wacece Gwaggo Asaben?” Nan Hudan tace “k’anwar Mommy ce” Sannan ta basu labarin halin da Mommyn take ciki. Kaf a labaran da Huda tazo da su na Mommy ne kawai ya girgiza Mama. Ta ji ba dad’i sosai, gashi ta san matar sun d’an saba dan haka tayi ta jimami…ga shima Aslam wanda dukda kalar rashin kirkin da yayi mata ranar amman har yanzu tana jinsa har cikin ranta….. Kamar ance ta kalli wayar Sakina da message ya shigo yanzu ta d’anyi haske! Wayar na nan akan cinyarta don haka ta samu damar ganin time… Mamakine ya kamata dan har ta shafe wajen awa d’aya da minti ashirin a wajen. Cikin k’arfin hali ta d’an kwanta a jikin Maman, bayan kamar minti uku ta mik’e ta cewa Sakina “tazk ta rakata taje tayi fitsari.” Kamar kuwa Mama ta sani dan tashi d’aya ta fara k’ok’arin mik’ewa tace “bari ta rakata da kanta!” Da kyar Ummu ta lallab’ata, ta hak’ura ta koma ta zauna. Daganan Sakina ta gyara mayafinta suka rik’e hannu suka yi gaba…. Har suka fita daga wajen tana d’an juyowa tana satar kallon inda su Maman suke…..tun kafin suje waje ta fashe da kuka mara sauti suna fita harabar asibitin ta sakeshi mai sauti ya fito, da sauri Sakina wadda tun d’azu taketa ce mata “bafa nan bane hanyar toilet d’in” amman tayi mata shiru sai janta kawai take yi tace “Lafiya Huda mai ya faru kuma?” Waige waige ta hau yi, chaan ta hango motar Abba da suka yi parking d’azu! Daman bata yi tunanin zai tafi ba. Bata b’oyewa Sakina ba, nan ta fad’a mata komai akan yadda suka shirya da Abban nata. D’an k’ura mata ido Sakina tayi….Chaan! Tace “Yanzu sai yaushe kuma? Anyways kinga dai 30 minutes ya baki yanzu kuwa kin kusan awa d’aya ma. Ki kunna wayarki kawai za muyi magana. Mai yasa kika kashe ko kwacewa akayi?” A hankali tace “Charger ne babu. Amman d’azu na siya a online an kawo har na ma jona Ina so ya cika ne kafin In kunna.” “Ok za muyi waya muje in rakaki” Hannun ta Hudan ta ruk’o kafin tace “Sakina kina ganin Mama ba zata ji haushina ba? Me za kice mata idan kin koma ciki?” Ajiyar zuciya Sakina ta sauk’e sannan tace “Haushin ki kam za taji, ba d’aya bama kuwa! Kuma yau Allah yasa ta bar Ummu ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96