Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 62

Chapter 62

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

abunda Sakinan tace, murmushi kawai yayi ya girgiza kai suka bi bayan su… Ba kowa a d’akin sai Mama ita kad’ai tana zaune a kan gadon jinyar tata da littafin addu’o’i rik’e a hannun ta, tana karantawa tana d’an tofawa k’afar da akayiwa d’auri! Tsananin azaba takes sha, shiyasa gaba d’aya jikinta ma rawa yake yi…. Raunukan jikinta sun d’an sab’e, fuskarta ma ta d’an sab’e amman still har yanzu akwai bandej a goshinta wanda aka zagaye kan nata da shi aka d’aure a k’eyarta, ta d’an yafa k’aramin mayafi akan doguwar rigar jikinta saboda masu shige da fice but still kana iya hango dogon gashinta da Ummu ta gama tufke mata shi yanzu ta dunk’ule a k’asan bandej d’in kafin ta fita. Hudan ce ta fara shigowa sai Sakina sai Daddy.. Bata ganeshi sosai ba dan haka ta d’an tsaya tana d’an satar kallonshi A hankali yayi sallama ya shigo, suna had’a ido tayi saurin sunkuyar da kanta sannan ta rintse idanuwanta. Bata gama dawowa dai dai ba taji Daddyn yana yi mata ya jiki, kamar ba zata amsa ba sai kuma ta daure, “Alhamdulillah” kawai ta iya cewa. A hankali su Hudan suka je suka yi hugging d’inta suma suka yi mata ya jiki, da kyar ta iya amsawa. Sannan duk suka nema waje suka zazzauna. Tana jira taga Abba ya fita sai taga shima ya nemi waje ya zauna kafin a hankali muryarshi ta daki dodon kunnenta “Maryam ya jiki?!” Banza tayi da shi! Ya sake maimaitawa Nan ma tayi mishi banza!. Murmushi Daddy yayi kafin yace “Allah yasa kaffara ne, ni bara ni In wuce. Dota sai kun dawo” Allah kiyaye suka yi masa. Sai da yazo fita tukun Mama ta samu k’arfin halin cewa “An gode” Da murmushi yad’an kalleta yace “Allah ya sauwwak’e” daga haka ya fice ya bar Abba a nan zaune wanda bashi da niyya ko ranar tashi dan gyara zama ma suka ga yayi...... Kowa da abunda yake sak’awa a cikin zuciyarshi…..d’akin yayi shiruuu! A haka Ummu ta shigo ta samesu. Da murna suka hau gaisheta bayan sun je sun yi hugging d’inta. Cikin mutantawa suka gaisa ita da Abba Daga nan itama ta nemi waje ta zauna aka ci gaba da zaman kuramen da ita. A haka Baaba Talatu ta shigo ta same su, wadda ta zo tare da jikanta Autan Anty Zainab tsaran Sumayya da Sumayyar. Sumayya tana ganin Sakina taje ta fad’a kanta tana cewa “I miss you” Sai da Hudan ta dungure mata kai tukun ta juyo ta rungume ta tana cewa “Sorry, i miss you more” Dariya duk aka yi, Yaron Anty Zainab kuwa yana gaida Mama da Ummu ya koma gefe ya zauna, daman kaf a y’ay’an nata wadda aka yiwa aure kwanaki (Khadija) ita ce kawai suke shiri amman da babbar da autan duk uwar su sukayo. Tunda Baaba Talatu ta shigo taga Abba ta had’e rai! Hankalinta ba k’aramin tashi yayi ba har sai da su Maman suka lura da hakan. Wani abun mamaki ko gaisuwarshi k’in amsawa ta yi, haka ya yi mata har sau uku a tunaninsa ma shi ko bata ji bane, ganewa da yayi amsawarne ba zata yi ba yasa ya kyaleta. Hudan kuwa abun da taga ana yiwa Abban nata ya k’ular da ita sosai, dan haka ta had’e rai tana gaida Baaba Talatu ta d’auke wuta a d’akin. Su Baaba Talatu basu wani dad’e ba suka tafi. Sai da Abba yayi 3 hours tukunna ya mik’e ya yiwa Mama Allah k’ara sauk’i Ummu ce ta amsa Hudan kuma ta tafi yi mishi rakiya. Har suka je motar ba wanda yace komai. Sai da ya shiga ya zauna, tukun ya d’auko kud’i a cikin motar ya bata yace “ta rik’e, ko suna son siyan wani abun” Godiya tayi ta karb’a. Ganin ta rik’e murfin motar yasa yace “Akwai wani abu ne?”. D’an b’ata fuska tayi kafin tace “Abba In kayi musu magana sau d’aya suka yi shiru kawai ka dinga kyalesu”. Bai san lokacin da murmushi ya sub’uce mishi ba, ya ji matuk’ar dad’i da Hudan ta damu da mutuncinshi haka..dan haka yayi murmushi yace “To shikenan princess, na ji, in shaa Allah. Shikenan? Ko akwai wani abun?” D’an guntun murmushi tayi tace “babu” daganan ta rufe mishi murfin motar, yayi waving d’inta itama haka, ya wuce. Sai da taga fitar motarshi tukun ta koma ciki............ Satin Mama biyu a asibiti aka sallameta. A cikin sati biyun nan ba ranar da zata zo ta wuce Abba bai je ya duba ta ba. Kamar yadda Hudan ta gaya mishi kuwa sau d’aya yake yi mata magana in ta k’i amsawa ya kyaleta Baaba Talatu itama haka! K’arshema idan ya shiga jimla yake yi yace “Ummu sannun ku, ya mai jiki?” Daga nan shikenan… Sau biyu suka had’u da su Madu, dan su Ummu sun rok’esu akan su daina yawan zirga zirga shiyasa ba sosai suke yawan zuwaba! Yayi mamaki dan bai yi tunani idan ya gaishesun za su amsa ba, amman ga mamakinsa sai yaga sun amsa ba yabo ba fallasa! Yadda Baaba Talatu taga sun yi mishi hakan ya sake d’aga mata hankali dan haka suna isa gida ta d’agawa Kaka hankali akan su fito da Usman yazo a maida auren su da Maryam, ko kuma su fad’a mata inda yake taje ta sameshi dan ya kamata ya san halin da ake ciki! Dan ta ga take taken Abba so gara a maida auren su k’arasa rayuwarsu tare tun kafin Abba ya b’ullo da wani abun…. Da farko Kaka a hankali ya fara binta, ganin da yayi ba fahimta za tayi ba sannan kanta ya soma birkicewa ya sanya shima ya birkice mata ya fito mata a mai gidan sa! Yayi mata fata fata!! Tukun ya samu ta sarara mishi dan tayi mugun tsorata da shi. Auwal ma zuwanshi biyar, tun su Ummu basu fahimta ba har Sakina ta tonawa kanta asiri, dan yana shigowa zata had’e rai, ko kulashi ba tayi Hudan kad’ai ke gaidashi. Su su Maman ma dariya take basu, ganin basu ce musu komaiba yasa suka zuba ido kawai dan sun lura Sakinar bata ra’ayin shi kuma sun san da maganar yayan k’awarta Ashraff. Har da Abba aka rakata gida. Tunda aka bud’e gate d’in gidansu gabanta yake fad’uwa, dukda yanzu Shuwa har waya tana yi mata tana jin ya take amman ta san ba lalle ta huce gaba d’aya ba, tunda gashi ko asibiti bata zo ba..tana murnar mutuwar auren Baba a kanta matuk’a amma tana tunanin zaman da za suyi da Shuwa kuma ko ita ta kawo rashin kunya duniya ba zata je tace zata zauna a gidan Kaka ba….. Tana wannan tunanin motocin suka yi parking a harabar gidan, wani sanyi da iska take ji yana shigarta ta koina “gida mai dad’i” Ta fad’i hakan a k’asan ranta wani hawaye yana zubo mata. Abba bai tsaya ba, ana gama kwashe kayan dake motarshi yayi reverse ya fita. Ummu ce ta taimaka mata ta hau kujerar ta, daganan ta tura ta tayi ciki da ita, su kuma su Sakina suka mara musu baya. A parlourn suka tarar da Shuwa, ga mamakin kowa tana gani an shigo da Maryam sai ta fashe da

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});