Chapter 48
Chapter 48
d’in da Arshaad yake ta zauna kafin tace “Am i missing something here???” Tayi musu maganar tana juyowa ta kalli wannan ta kalli wannan. “Eat!” Arshaad yace sannan yaci gaba da cin abincin shi. Dawowar da Abba yayi ne ya katse mata maganganun da suka taso mata don haka tayi shiru… Luckily aka sake kiran Abba a waya dan haka ya mik’e yace “bara ya shiga wajen Daddy” Ba a jima ba Aslam shima ya mik’e, da sauri Hudan ta mik’e ta mik’a mishi Goron ruwan hannunta Opposite yau ma suke dan haka ya kalle ta yace “thankyou!” a hankali yana kallonta. Bata san daliliba! Dan kwata kwata sam sai ta kasa janye idanunta daga nashi. Tunda Mama ta kawota duniya ko a tv bata tab’a ganin kwayar ido mai kyan nashi ba! Shape d’in Idon kansa abun son ka kalla ne! Komai na idanun nasa masu kyau ne Itakam wata rana zata tambayeshi ‘me yake shafawa eyelid d’insa?’ Dan wani haskene yake fitowa daga wajen ..... Dukda yadda zuciyarta ta tsananta bugu hakan bai sanyata ta d’auke idanunta daga kansa ba kuma baisanya ta sakar mishi robar ruwan da ta mik’a masa ba! “GOOD NIGHT Sakina!!” Suka ji Arshaad ya fad’a da d’an k’arfi! Da sauri Aslam yayi firgigit, ya janye robar da mugun k’arfi, sannan ya juya yayi hanyar fita. Har ya fice daga parlourn bai yarda ya sake juyowa ba. Hudan ita kam kunya ce gaba d’aya ta lullub’eta.. Ashe har Arshaad da Sakina sun mik’e su shuraim kuma suna shirin fara hawa bene ita bata ma sani ba!. Yana shirin barin wajen Sakina tace “pls mana” Tana d’an karkartar da wuyanta. Murmushi yayi yace “she’s busy rn, let it go kawai.” A hankali Sakina tace “Plss” Tana had’e hannuwanta biyu waje d’aya alamun rok’o. Ajiyar zuciya ya sauk’e ya d’an ja ya tsaya. Hudan na ganin wucewar su Shuraim sama ta juya itama zata bar wajen. Hannu Sakina tasa ta rik’eta. Ba tare data juyo ta kalleta ba tace “Sakin mani hannu plss, bacci nake ji” Jin abunda tace ya sake tunzurashi don haka kawai ya fice fuuu!! Ko sauraron Sakina bai sake yi ba. Haushi Sakina taji ta saki mata hannu suka haura sama… Har suka shafa addua suka kwanta suka ja bargo ba wanda ya yiwa d’an uwanshi magana........... BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 44 Tun Asuba Hudan ta sauk’o ta fara kula Sakina, dan ita ta tasheta ma sallar Asuba. Sakina kuwa har suka yi wanka suka shirya, aka je aka yi breakfast aka dawo bata kula Hudan.nKo tayi mata magana ma sai dai tayi mata banza: Hankalin Hudan bai tashi ba, sai da taga Sakina ta saka kayanta waenda tazo dasu chap ta shirya, tace mata “sai sunyi waya”. Da sauri ta shiga gabanta ta tsaya dan har ta kusa k’ofa, kafin tace “Ban gane ‘sai munyi waya’ ba! Me hakan yake nufi?” Ba tare data kalletaba tace “Tafiya zan yi” Cikin rashin jin dad’i Hudan tace “Akan Ya Arshaad kikayi fushi dani haka har kika yanke hukuncin tafiya ki bar ni?? Kin san kuwa me yayi min?” D’ago dara daran idanuwanta Sakina tayi, kafin tace “Nasani Hudan, sanin abunda ya had’akun ne ma har yasa kike fushi dashi hakan ne zai sanya in tafi.. Jiya baki b’ata min rai sosai ba amman dana san dalilin fad’an naku wallahi bakiji yadda raina ya b’aci ba.” Cikin takaici da son fahimtar da ita Huda tace “Sakina Jalila fa yaje........” Cikin katseta Sakinar tace “Na fad’a miki fa, na sani. Jiya mun yi chatting da shi sosai ya fad’amin komai! Haba Huda, kamar baki san wacece Jalila ba? Dan ta fad’a miki magana sai ki hau ki zauna?? Kishi ne ya rufe miki ido ko rashin wayo? A tsakaninki keda Ya Arshaad bai kamata a samu haka ba. Jiya cemin yayi kawai bakya sonshi, maybe akwai wanda kike so yanzu saboda he can recall yadda kikayi calling off engagement d’inku saboda Ya Junaidu kawai don bakya son ki b’ata mishi rai! Amman shi yanzu lokaci d’aya kin murzawa idonki tuka kinata zuba mishi rashin kirki! Ba abunda yafi b’ata mishi rai irin yadda ana fad’a miki kika hau kika zauna, kamar daman tun farko kina zarginshi… Anyways yace yana neman alfarma a wajenki, anjima zai san yadda zai yi ya kawo Jalila nan, akawo AlQurani suyi alwala shi da ita kowa ya rantse akan gaskiya yake fad’a! But yace b4 then dan Allah ki d’au waya ki kira Aaima ki tambayeta waye Auwal ya halinshi yake!” Tunda Sakina ta fara magana jikinta yayi sanyi Sai yanzu take ganin rashin kyautawarta…. Ganin Sakina, tana shirin zagayeta ta fita ne yasa ta kuma tararta ta tare hanyar kafin tace “To kiyi hak’uri ki fasa tafiya, haba Sakina, ko kece kikaji haka fa dole kiji haushi” Da sauri Sakina tace “Hudan zan tafi! Dan ba zan iya tsayawa inga wai Ya Arshaad yana dafa Qur’ani yana rantse miki akan ba shi ne ya yiwa Jalila ciki ba! So that ki yarda kuyi getting back together.. Haba Huda! Ya Arshaad ne fa, wallahi sam bai chanchanci haka daga gareki ba!. But ba zan hanaki ba, ki barshi yayi dan na san tunda kin riga kin saka haka a ranki to in ba rantsuwar yayi miki ba ba zaki tab’a yarda ba!. Amman wallahi kinji dai na rantse miki ba ruwan Ya Arshaad a lamarin nan! Shi wannan Auwal d’in shine yayi aika aikar shi kuma zaki ce na gaya miki, Ya Arshaad ya fad’a min baki tab’a ganinshi ba sai ranar amma yana fad’a miki magana kika hau kika zauna shi kuma da kika sanshi for almost 4 years kika k’i yarda dashi. Hudan Ya Junaidu, kwatar ki yake yi a hannun su Jalila idan suna kimar ki amman kince ba zaki tab’a manta alkairinshi gareka ba Ya arshaad fa? Zaki iya gaya min irin tarin alkairan da yayi miki? Ba ke ba har ni kaina da nake kusa dake sai da alkairinshi ya shafeni.” Ahankali Hudan ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace “Sakina ranar nan fa a gaban ki Mama tace min taji Yaro yazo yace wai Jalila taje inji Arshaad..” Murmushin takaici Sakina tayi kafin tace “kuma a same day da time ne ke da Ya Arshaad d’in kuka yi dogon video call ba! Ba ma voice call ba video call and a d’aki muka ganshi throughout bai fita ba har kuka gama, ba a mota ba!. Kinsan wani abu Huda? Bata jira jin amsarta ba tace “wallahi duk makirci ne, so sukeyi kawai su shiga tsakaninku! That Auwal shi yayi planning komai, ban san mecece agenda d’inshi ba, but na san shine master mind! Ban ganshi ba amman na tsaneshi!. Ni dai shawarata a gareki itace ki bud’e idonki da kyau, ki fahimci gaskiya tun kafin dare yayi miki! Arshaad ya sanki ya soki tun kina Hudan ki! Idan kikace zaki juya mishi baya yanzu gaskiya baki kyauta ba!. Ban hanya in wuce, dan ba zan iya ganin wannan abun takaicin ba.” Rugumeta Huda tayi kafin tace “Shikenan ya wuce Na hak’ura! Dan Allah karki tafi.” “No, Hudan seriously ki bari yayi miki clearing confusion d’inki, saboda kar ki dinga ganinshi da abun
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96