Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 24

Chapter 24

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

juya tana kallon Arshaad kafin a hankali tace “Ya Arshaad dan Allah ka b’oye ni dan Allah.” Tayi maganar tana had’e hannuwanta waje d’aya alamun rok’o, tana kuka. Ganin sun kusan isowa ne yasa Arshaad d’in da sauri ya jata yasa a d’akin mai gadi sannan yace mata “ta shige toilet d’inshi(mai gadin) tayi shiru.” Tana rufe k’ofar toilet d’in su kuma su Abba suna shigowa gidan, dai dai Arshaad yana shirin fita shi kuma, suka yi kicib’is!. Kallon kallo aka tsaya yi, kafin Daddy yace “kunga Hudan?” Aslam yana shirin yin magana Arshaad yace “No” da sauri sannan ya d’ora da “Neman ta ake? ina tayi? Mai ya faru?” Aslam kawai Abba ya k’urawa ido..ganin yak’i had’a ido da shi yasa ya cewa Daddy wanda yake shirin yiwa Arshaad bayani “Mu koma kawai, inaga wajen Gwaggo Asabe tayi. Ma duba ta anjima, lets take care of Granpa, na tabbatr biyotan da muka yi yanzu ma case ne.” 100% Daddy ya yarda da hakan dan haka ya cewa Aslam “ya ci gaba da duba musu Hudan za suyi musu bayani anjima, shi kuma Arshaad yaje Gate yayi confirming in bata fita ba daganan ya sa curfew a estate d’in har su samu su gama meeting da Granpa su fito.” Da “to” suka amsa musu daganan su Abba suka wuce. Suna fita shima Arshaad ya fara k’ok’arin fita a gidan “Kace mata zata iya fitowa.” Shine kawai abinda ya iya cewa Aslam ba tare da ya yarda sun had’a ido ba. Har ya juya yaji Aslam d’in ya ruk’o hannunshi… Da sauri ya runtse idanunsa da k’arfi, sai da ya d’an dedeta fushinsa kafin ya juyo yana kallonshi. Aslam tunda yake bai tab’a jin nervousness irin na yau ba, dan haka ya fara kame kame “Um, I’m sooo sorry a b bout” Da sauri Arshaad ya katseshi ta hanyar cewa “It wasn’t your fault, tayi laifi, so ko baka yi abunda kayi ba dole na san wata rana gaskiya zata fito, kuma za ayi punishing nata. Kawai dai i was disappointed in you ne that’s all” Sai da ya d’anyi shiru yaji hucin da yake yi ya d’an ragu tukunna ya ci gaba da magana “Ko sabon mai aiki aka chanja a gidan nan baka nan Aslam kana Uk but sai na kiraka na fad’a maka! Ya kamata ace lissafinka ya baka ‘if Abba yana da y’a and bai san da ita ba, to dole akwai wani abu a k’asa’!. Da kayi finding out about Huda you should have talk to me first mu samu mu fara bincike first! Because that is wat i’ll definitely have done if i were in your shoes. But you just went ahead and ruin everything. Yanzu because of you Mahaifiyata is there a cell da anty Adama su da basu da laifin komai, they just help a friend.” A hankali yace “i tot we were brothers, best friends.” Cikin katseshi Aslam yace “and yes we still are, yana matsowa kusa dashi da rik’eshi”. Murmushi kawai Arshaad yayi ya zare hannunshi sannan ya zagayeshi ya fara k’ok’arin shiga d’akin mai gadi. Ajiyar zuciya Aslam ya sauk’e kafin yace “Ok, I’m sorry” yana mai sake ruk’o hannunshi. Sai da Aslam d’in ya maimaita sannan Arshaad ya juyo ya kalleshi na y’an seconds kafin yace “Apology accepted.” “Thankyou “ shine abinda Aslam d’in yace kafin ya d’aura da “And about what you just saw, i’m..” Cikin katseshi Arshaad yace “Aslam we’re good fa, komai ya wuce, let me check on her, ta shiga toilet d’in mutumin nan barefoot kuma i don’t even know ko yana ciki dan ban ganshi a d’akin ba.” Yana gama fad’in haka ya zare hannunshi sannan yayi cikin d’akin ya isa bak’in k’ofar toilet d’in yana cewa “Hudan open the door, it’s me, su Abba sun tafi.” A hankali take bud’e k’ofar tana d’an lek’owa.. Sai da ta tabbatar da shi d’inne tukunna ta k’arasa bud’ewa. Murmushi ya d’anyi mata.. Gaba d’aya ta had’a gumi tayi zuru zuru! A hankali yace “matsoraciya kawai” A hankali tayi k’asa da kanta sannan ta fito, Allah ya taimaketa ba kowa a toilet d’in kuma mutumin yanada tsafta dan band’akin tass yake gashi tiles ko ina kuma a bushe. Amman dukda haka sai da Arshaad yayi amfani da ruwan butan da ya gani bayan sun fito ya zuba mata akan k’afafunta. Suna fitowa ya cire takalminshi ya bata ta saka sannan yace “ta zo ta rakashi ya saka takalmi.” A hankali ta fara kuka kafin tace masa “Ita wajen Mama zata je” Gaba d’aya sai yaji wani matsanancin tausayinta ya kama shi. Shiruuu, yai yana tunanin ta yadda zai fita da ita bayan shi aka d’orawa alhakin curfew. Dole ya lallab’ata ta d’an hak’ura ko zuwa gobe ne sai su je. Matsowa yayi yana shirin lallashinta wayarshi ta hau k’ara, ganin sunan Sakina ya sanaya shi ce mata su k’arasa ciki akwai maganar da yake ai suyi da ita, dama. Tukunna sai ya kaita gurin Maman. Ba tare da musu ba ta bishi suka yi hanyar shiga parlourn gidan, Aslam har zai bisu dan still ya lura Arshaad d’in is still mad, saboda da suka fito ko inda yake bai yarda ya kalla ba.. Sai kuma kawai ya chanja shawara ya juya kawai, duba da yayi ba shi kad’ai bane kuma ya lura soyayyar Mahaifiya ta rufe mishi ido, if not tayaya zai ce “ita da Mom basu da laifil!” ko kuma may be bai san story d’in gaba d’aya ba, dai. Da wannan tunanin ya fita a gidan bayan ya yanke shawarar sai nan da 4 to 5 days haka zai nemeshi ya sake bashi hak’uri, by then ya san ya sak’k’o..... Suna shiga parlour ya umarceta da “ta zauna akan kujera” Bayan ta zauna shi kuma ya nufi fridge ya d’auko mata ruwa da glass cup a kan dining ya kawo. Dama kuwa tana buk’ata hakan yasa yana zuba mata ta k’arb’a ta hau sha. Sai da ta shanye tass sannan ta ajjiye tana sauk’e ajjiyar zuciya a jejjere. Kallonta yayi da idanuwanshi da har yanzun basu gama dawowa dede ba sannan a hankali yace “In kara?” Girgiza mishi kai tayi tana y’ar mitsitsiyar gyatsa kafin tace “Alhamdulillah” Sai kuma anhankali ta mik’e tace “Bara inje wajen Aaima” Mik’ewa shima yayi yace “bata nan, bata dawo daga school ba tukun! Mammy kuma tana cell! It’s just me.” Ya fad’i hakan yana tsareta da ido. Saurin yin k’asa tayi da kanta, kafin a hankali tace “Kayi hak’uri dan Allah.” Murmushi ya d’an yi yana kallonta kawai ba tare da yace komai ba. A hankali tace “bara in tafi, nayi tunanin Aaima tana nan ma.” Bata jira jin me zai ce ba ta fara k’ok’arin fita tana cewa “ka d’auko takalmin naka muje mu duba Mama da wuri, ko?”. Dede nan wayarshi ta sake ringing, ganin me kiran ne yasa shi kai mata wayar har bakin k’ofa sannan yace “Na so muyi magana but it’s like kamar tsorona ma kikeji! Gashi ungo, Sakina ta gaya miki, bara in d’auko takalmin nawa” Yana gama fad’an haka ya kara mata a kunne bayan ya amsa kiran daga nan yayi hanyar part d’in nashi. Da sallama ta amsa wayar.. Ajiyar zuciya

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});