Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 76

Chapter 76

So Da Buri Book 2 Complete Hausa Novel – The Secret That Changed Everything 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya had’asu dan ba zai iya jurar ganinta a wannan halin ba!… Muryarta ce ta dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi, a hankali yaji tace “Ina wuni” Jinjina kai yayi kafin a hankali yace “Alhamdulillah” Sannan ya koma ya zauna ya shiga gaida Dad wanda ya nemi waje shima ya zauna. A k’asa kan kafet Mom ta zauna tana ta sun sunkui da kai! Tausayinta fal zuciyar Mijinta dan ya hango tsantsar nadama da shiryuwa a matar tashi, daman chan shi ya san sharrin shaid’an ne! Ba abunda yafi d’aga mishi hankali irin bak’i da lalacewar da tayi, in shaa Allah nan da 3 days zai shirya musu fita suje ayi mata checkup….. Muryar Dad ce ta katseshi jin yana cewa “Abba ya dawo kuwa?? Inason ganinku ne tare.” “Eh to i don’t think so but bara in kirashi” Daddyn ya fad’a yana mai zaro wayarshi daga aljihun wandonsa......... Da kyar ya iya kai wa 2 yau a waje, duk da tarin aiyukan da suke a kanshi haka nan ya baro su birjiki! Ya dawo gida. Yana d’aki shi kad’ai sallah kawai yake iya fita yayi… Anya bai yi gaggawar aurar da Hudan ba kuwa? Kar yaje garin gudun b’atawa su Yaya da Daddy rai ya cuci kanshi fa! He just knew her amman har ya d’auketa d’ungum ya bama wani kuma bama a Kano kusa da shi da anytime yaso zai je ya ganta za su zauna ba! A Uk za su zauna, sai after 4 ko ma 5 years tukunna za su dawo!. Da k’arfi ya sauk’e ajiyar zuciya A ranshi ya raya zai nemi Alfarmar Arshaad akan su d’an zauna anan gidanshi for some time, ko da ace duniya za tayi mishi kallon the most selfish father ne!! Tsaki ya jaa tunawa da yayi Arshaad d’in har ya biya mak’udan kud’i na course d’inshi da zai yi da kuma karatun da Hudan zata fara… Yana wannan tunanin yaji kira ya shigo wayarshi.. D’auka yayi ba tare da ya kalla sunan ba ya amsa ya kara a kunnenshi, sai da Daddy yace “Abba” Tukun ya fahimci wanene dan haka ya gyara zama yace “Ina wuni, ya aiki?” Amsawa Daddy yayi daganan yace masa “yazo ya samesu ga Dad ya zo yana son ganinsu”. “Ok” kawai yace, sannan ya kashe wayar ya mik’e ya fice jikinshi duk a sanyaye. Ko mintuna hud’u cikakku bai rufa ba, ya k’arasa parlourn. Waje ya nema ya zauna suka sake gaisawa.. Ba tare da b’ata lokaci ba, Dad ya fad’a musu sak’on Granpa! Shi ababa wallahi har k’asan zuciyarshi yama manta da wata halitta wai ita Ummi! A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya, ya koma ya kwantar da kanshi a jikin saman kujerar ba tare da yace da su komai ba! Dan in ya cewa Dad zai iya yin abunda Granpa yace a yanzu dai tou gaskiya k’arya yake yi, sai dai maybe ko in gaba. Mom ce ta katse mishi tunanin shi ta hanyar cewa “Abba Ina mai baka hak’uri game da kuskuren da muka aikata maka! Bisa ga biyewa son zuciyoyinmu, ka yafe mana dan Allah.” Shi sai a lokacin ma ya gane ita ce a wajen. Mik’ewa kawai yayi ya cewa su Dad “Bara inje in sha magani In d’an kwanta kaina yana min ciwo, sai da safe.” Daga nan kawai ya nufi hanyar fita…. .....inda ace Mom ta san tunzurashi d’in da maganar ta tayi, da ba zata soma ba! Kawai wani sabon haushin su ne ya sake lullub’e shi.. Hudan is soppose to get married at this age duk wani uba zai so hakan amman dalilin su ya sanya har yake having second thoughts akan abunda ya san shine farin cikin ta, yakamata ace yana taya ta murna yana sopporting d’inta d’ari bisa d’ari amman because of them gashi har yana son aikata abunda za aganshi kamar selfish, kuma ya san inba da kyar ba, su Yaya za su iya jin haushin sa wanda hakan abunda bai tab’a faruwaba ne… Daddy yana shirin yin magana da sauri Dad ya dakatar dashi ta hanyar d’aga mishi hannu! Har Abba ya fice ba wanda yace komai. Yana fita shima Dad d’in ya mik’e yayi musu sallama ya fice. Mik’ewa Daddy yayi daga inda yake ya koma k’asa wajen Mom. Tun kafin yace wani abun ta fad’a jikinshi ta fashe da kuka tana rok’on shi akan “yayi hak’uri shi da y’an uwanshi, in shaa Allah ba zata sake ba! Sharrin shaid’an ne dan Allah kar ya dinga kallonta da abun ya taimaka mata ya goge komai a ranshi…” Lallashinta ya shiga yi yayi hugging d’inta yana jin tausayin ta na sake shiga zuciyarshi.. Da kyar ya samu tayi shiru daganan yace “tazo taje tayi wanka ta huta” Dan da gani tana buk’atar ta tsaftace jikinta da kuma hutu ba na wasa ba.......... Hatta kujerun personal parlour d’inta na chan sama, sabbi dal Daddy ya saka mata Bedroom ma ya saka mata sabbin furnitures duk don ya dan rage mata zafi. Har k’asa kuwa ta durk’usa ta kama k’afafunshi tayi godiya sannan ta sake bashi hak’uri. Shi kam Daddy tausayinta kawai yake ta ji, yaga duk tayi sanyi ta koma kalar tausayi, sai wani nan nan yake yi da ita.... Ko da Auwal ya dawo bai san da labarin dawowarta ba, gashi kuma ranshi a mugun b’ace yake ga gajiya, dan haka direct side d’inshi ya nufa, yayi wanka yayi sallah ya bi lafiyar gado, da kyar sai da yayi da gaske tukunna hoton Sakina da Ashraff yabar idanuwanshi sannan ya samu bacci ya d’auke shi. Auwal yana ajjiye Arshaad ya shiga gida shima. A mugun gajiye yake dan haka tun a hanyar shiga ya zare suite d’in shi ya rik’eta a hannu kafin ya fara k’ok’arin zare necktie d’in! Kana ganinshi ka san bacci kawai yake buk’ata. Ko kallon cikin parlourn bai yi ba ya nufi side d’inshi…. “Ango!!” Yaji muryar Mammy. Da sauri ya d’ago yana kallon setin inda yaji muryar tata ta fito, “ai kuwa ita d’in ce” ya fad’i hakan a ranshi. Da murna ya k’arasa inda take zaune ita da aiima… Ita kam ko wankan ma bata samu tayi ba! Tana nan a yanda ta fito a cell! Yo ina zata iya wanka, ko sama bata samu ta hau ba tun da Aaima ta fad’a mata mummunaan labari take zaune take jiran dawowar Arshaad. Huggin d’inta yayi kafin ya d’ago yayi kissing forehead d’inta tukun yace “Welcome home Mammy, we miss you.” Murmushin takaici tayi kafin ta mike tsaye, cikin tsananin b’acin rai tace “Ba kayi missing d’ina ba Arshaad, da kayi missing d’ina to da ba zaka yi min yaji ka daina zuwa inda nake ba” Kamar zai yi kuka yace “Mammy bana son ganin b’acin ranki, abunda kike so inyi ne ba zai yi ba, kiyi hak’uri please.” Cikin katseshi tace “Ka san cewa Aslam baya yin kwana uku bai lek’o mu ba? Haka Auwal shima! Daddy kuwa kullum sai ya kira waya an had’ashi da Adama Ummi kam daman kowa ya san Mijinta ba zuwa zai yi ba tunda shi ne ya kulle mu! Kai fa? Arshaad da kai da uban ka laifin me nayi muku, a rayuwa? Anya ni na haifeka

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});