Chapter 78
Chapter 78
har sai da ya farkar da Sakina da Khadijah amarya y’ar Anty Zainab da suke d’aki d’aya da ita daga bacci. Ganin yanda duk ta rud’e ne yasa Sakina ta shiga tambayarta…. Karb’ar wayar Sakina tayi itama ta shiga kiran sunan shi tana “Are you there? Are u okay??” Amman tsit kake ji ko tari babu. Rikicewa suka yi… Da kyar idea ta fad’owa Sakina hakan yasa da sauri ta d’auki wayarta ta danna kiran Aaima! Sai da kiran ya kusan tsinkewa tukunna aka d’auka, cikin gigita Sakina tace Aaima ina wuni, sorry na tashe ki, Ya Arshaad ne bashi da lafiya, dan Allah ko zaki gayawa Dad in yana gida a duba shi ko kuma ki tura wani wanda yake kusa….” Shiruuu, Sakina taji anyi! Hakan yasa ta sake cewa “Aaima” Ajiyar zuciya taji Aaiman ta sauk’e sannan ta fara magana “Ki turo Hudan mana ta zo ta duba shi! Daga nan ma sai su yi sorting out decision d’in da ya kamata su yanke.. Besides a nan ba wanda zai kulashi saboda rashin lafiyarshi ba zamu iya yi mishi maganinta ba. Spoiler alert!! Bara kiji abunda na san ya jawo mishi ciwon...... Mammy ta dawo d’azu at last ita da su Mom! And tace masa ‘ya hak’ura da auren Huda ko kuma ta tsine mishi!’ Wannan shine abunda ya janyo mishi rashin lafiya na riga da na sani.” Tana gama fad’in haka ta ajjiye wayar. K’amewa Sakina tayi ta kasa cire wayar daga kunnenta! Sai da Hudan ta tab’ota tace “Ya ake ciki Sakina?” Tukunna tayi firgigit ta dawo daga tunanin tashin hankalin data fad’a na y’an sakanni.... ….Dama da ita bata tab’a fadawa kowa ba ne amma haka kurum idan ta tuna Mammy bata san dalili ba sai taji gabanta yana ta fad’uwa! Dan bata san ya tsakaninta da Huda zai kasanceba. Kuma ta lura kamar Arshaad d’in yana ta saurin ayi ayi ai auren su samu su bar k’asar! Tabbas sai yanzu ta fahimci dalilinshi.. To amma mai yasa Ya Arshaad zai so ya had’a ta da surukar da ba zata amsheta ba? Duk kuwa da tsananin k’aunar da suke yiwa juna ai da sun hak’ura!…… “Sakina, akwai matsala ne?” Muryar Hudan cikin rauni, ta katse mata tunaninta…. Juyawa tayi suka had’a ido! A take wani tsananin tausayinta ya rufeta dan bata jin a cikin shekaru ukun nan akwai lokacin da take hango tsantsar k’aunar Arshaad a idanun Hudan kamar wannan lokacin. Da kyar ta iya ce mata “Aaiman bata gida, bara in kira Auwal kawai.” Ta fad’i haka tana me mik’ewa ta fice daga d’akin gaba d’aya. Hudan kwata kwata bata gamsu da maganar tata ba dan haka ta mik’e ta bi bayanta. Suka bar Khadija wadda itama bata wani yarda da maganar Sakinar ba dan ta lura da yanayin da ta shiga tun fara wayarta da wadda suka kira da ‘Aaima’. Tana fita ta samu damar zubar da kwallar da take ta k’ok’arin rik’ewa! Yanzu Ina mafita? Meye abunyi ? Sune tambayoyin da suka toshe mata kwanya sannan ta kasa samun mai bata amsar su. Daman y’an layi har sun fara k’ananan maganganu suna cewa ....Allah dai yasa tarihi kar ya maimaita kanshi Ita maryam bata daddara da family d’in Abba da abunda shi kanshi Abban yayi mata ba shine zata aurawa Huda nephew d’inshi dan kawai taga yana da masifar kud’i! Ga dai Ummu ita da ta auri saffa saffa hankalinta a kwance rayuwarta gwanin ban shaawa amman ita har yau bata samu kwanciyar hankali ba a ta dalilin So da Buri! Ta mannewa mutumin da yafi k’arfin ta nesa ba kusa ba.... Jin k’arar bud’e k’ofar d’akin nasu ne ya sanya Sakina goge hawayenta da sauri, sannan ta lalubo number Auwal ba dan ranta yana so ba ta fara kiranshi…. Bacci bai dad’e da d’aukarsa ba dan bai dad’e da kwanciya ba amman yana fara baccin ya hau mafarkinta............. Yana cikin mafarkin nata k’arar wayarshi ta katse mishi mafarkin…. Kamar ba zai juya ba bayan ya farkan sai kuma yayi tunanin ko Granpa ne dan haka yayi tsaki ya lalubo wayar akan bedside ya amsa ya kara a kunnnen shi ba tare daya duba mai kiran nasa ba. Jin shiru yasa tace “Ya Auwal” A hankali. Bude idanuwansa yayi da kyau kafin ya zaro wayar daga kunnenshi ya kalla sosai ya tabbatar itan ce tukunna ya mayar da wayar kan kunnensa ya mik’e zaune yana adduar ‘Allah yasa lafiya’ dan ya san ba k’aramin abu bane zai sanya Sakina ta kirashi kuma cikin daren nan ba. Sai da ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace “How far” Dan lokaci d’aya ranshi ya b’aci bayan ya tuno ta Ita da Ashraff d’azu. Ba tare da b’ata lokaciba tace mishi “Ya Arshaad ne suke tunanin bashi da lafiya dan yanzu ma kamar suma yayi suna cikin waya da Hudan.” Ta san maybe Hudan ce ta fito d’azun kuma maybe tana tsaye a bayantata dan haka sai ta tak’aita maganar tata sannan tace “Dan Allah yaje ya dubo shi” “Okay” Kawai yace daga nan ya kashe wayar ya mik’e ya fad’a toilet yad’an d’auraye fuskarshi ya chanja zuwa jallabiya tukunna ya fita.......... Sai da ya daddannawa gate man d’in zagi, tukunna ya barshi ya fita A cewar shi (gateman d’in) Daddy ya hana a na barinshi yana fita cikin dare. Sai mita yake yi shi kad’ai a mota haka ya isa gate na estate d’in MT ..a ranshi yana aiyyanawa ‘Da mutane sun san halin da yake ciki to da ko kallonshi ba zasu dinga yi ba! Komai b’ata mishi rai yake yi tun d’azu...’ Allah ya so shi bai samu matsala da mai gadin main estate d’in ba, sai dai ya rok’esa akan ‘ya bi a hankali kar ya bari Granpa ya ganshi dan zai iya cewa a bakin aikin shi’ Jinjina kai kawai yayi ya wuce ciki. Ya dad’e yana knocking jin shiru yasa ya yanke shawarar kiran Aaima yace mata ‘ta kira layin wata a cikin masu aikin gidan tazo ta bud’e mishi k’ofa.......’ Tunda Sakina ta kira ta bacci ya k’aura daga idanunta, tana cikin chatting kiranshi ya shigo wayar tata. Ta dad’e tana kallon number, kasancewar ta dad’e da goge numbershi amman ta na nan a kwakwalwarta bata gogu ba! A take jikinta ya mutu.. Sai da wayar ta kusan tsinkewa tukun ta samu damar amsawa, cikin sanyin jiki ta kara a kunnenta tace “Hello” Ba tare da ya amsa ba yace “Aaima Arshaad is sick, na zo duba halin da yake ciki kuma k’ofan ank’i bud’ewa.. Can you do me a favor ki kira wani wanda kika sani a cikin gidan yazo ya bud’e min? It’s an emergency” Tunda ya fara magana ta lumshe idonta har ya kai aya a hankali tace “to” kawai, ta tsinke kiran. Kamar 5 minutes yaji ana k’ok’arin bud’e k’ofar, ana bud’ewa ya kutsa kai ciki ba tare da ya kalli bayan k’ofar ba inda take, yayi hanyar side d’in Arshaad direct kawai. “Ina wuni” Yaji muryar ta. D’an juyowa yayi ya kalleta a ranshi yace “Ashe ta dawo.” Ba yabo ba fallasa yace “Lafiya” Kawai ya juya ya nufi hanyar part d’in Arshaad. “Ya k’ara haske, sai dai yad’an rame kad’an! Ya k’ara kyau.”
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96