Chapter 86
Chapter 86
Sakina suka take musu baya. Hudan, so take ta yakice tunanin Arshaad a kanta amman ta kasa! K’arshema bigewa tayi da adduar Allah yasa tana fita ta ganshi amman yanayin yanda taji an zaunar da ita a doguwar kujerar da aka k’awata domin ita da shi ne yasanya ta fahimci bai zo d’inba. Ummu ce ta fito ta bud’e taro da addua sannan ta fara gabatar da al’ada a Huda, A matsayin uwa. Mama suna parlourn Madu, tun lokacin da Mommy da Aslam suka zo suka buk’aci ganinta har yanzu bata samu damar fitowa ba. Wata distant relative d’in Shuwa wadda zata d’an girmi Shuwan kad’an ce ta k’arasa wajen sannan cewa Ummu “Ina uwar Angon? Ta zo ta zauna a kusa da ke yadda kina gamawa zata karb’a. Sannan ba ayi welcomin Ango ba kuma ba aga shigowarsu ba besides ai dole sai yananan ma tukunna za ayi komai. Na ga bai riga yazo ba amman kin yi wuff kin fara abu haka bayan kuma akwai abubuwa da yawa before wannan.” Karaf! A kunnen umma. Daman neman abun yi suke yi ita da Anty Zainab shiyasa suka zo suka zauna a k’asa gefen kujerar Amarya. Da sauri sannan da d’an k’arfi yadda ta tabbatar kowa zai ji Umman tace “Eh kam tabbas!” Sannan ta mik’e tsaye kafin tace “Uwar Ango! Tana Ina? Ana buk’atar Uwar Ango a nan yanzu yanzu” Da k’arfi ta yadda kowa ya iya jiyota tunda daman wak’ar da aka kunna a low tune yake kuma iya murya ne kawai babu kid’a. Da sauri Ummu tace “Umma meye haka? Idan kin yi min magana ba zan je In kirata baneba? Ko hakan da kika yi kina tunanin shi zai sa ta fito?” Still da k’arfi Umma ta sake cewa “A’a, ai ji nayi kamar kince bata zo ba! Gashi shima Angon shiru. Duk da dai ni ba Shuwa bace ba amman Tabbas na asan cewa Ango da Amarya a tare ake shafa musu lalle, manshanu, da ragowan abubuwa! Dan har yau ina tuno naki, a tare aka shafa muku ke da Muhammadu wanda ya zo wurwuri bai tsaya b’ata lokaciba, Ita kuwa yayarki daman ba a yi mata ba shiyasa gaba d’aya auren nata duk biyun suka tab’arb’are! To kuwa kinga ai ba zan so auren Huda itama ya samu matsala ba ko? Dan haka gara mu jira Angon ya zo ko nan da k’arfe taran dare ne mu masu iya jiransu ne har sai shi da uwarshi sun zo an yi alada yadda ya kamata!”. Ta k’arashe maganar har wani karkarwa jikinta yake yi, wanda kana gani ka san bala’ine kawai yake cinta. Ummu bata ga k’arasowar Sakina ba sai tayi tana cewa “Eh tabbas kam Hajiya Umma kya zauna ai kiyi ta jira tunda daman kallon kwaf da munafurci ne ya kawo ki! Mu nan dukkannin mu munada aikin yi kuma ba mu da lokacin zaman jira har k’arfe taran dare! In dai Ango kike son gani to ki bada nan da awa biyu zaki ganshi sun iso tare shi da iyayenshi maza da za su kawo lefe wanda na tabbatar abunda ya tsaidasu kenan ba wai abunda makirar zuciyarki ta shirya miki ba!” Umma na shirin k’arasowa inda Sakinar take taga Ummu ta d’auke ta da mari! Cikin yaren Shuwa Ummu ta hau yiwa Sakinar fad’a k’asa k’asa yanda ta tabbar ba kowa ne zai ji su, tace “Baki da hankali ashe? A cikin dangi da y’an uwa za ki bud’e baki kina yiwa babbar mata rashin kunya haka? So kike a tafi dake a baki? Wuce! Wuce ki tafi chaan sama d’akin Shuwa ki rufe! Idan ba ni na neme ki ba wallahi kika fito sai ranki yayi mugun b’aci!”. Juyawa kawai Sakina tayi ta wuce tana ji kamar ta had’iye zuciyarta! A kan Umma aka mareta a gaban mutane haka!? Kuma ta tabbatar tunda Umma ta fara wannan maganganun to fa idan taka mata burki aka yi ba ko kuma Arshaad d’in ta gani ba tabbas ba zata tab’a barin mutane su sha ruwa ba. Ita daman tun d’azu da ta ganta tazo da sassafe ta san ba alkhairi ne ya kawota ba. Ita da take da abun fad’a a gindi amma shine har take da audacity d’in yin magana! Wallahi yau da Ummu ta barta da sai ta yiwa Umma zazzagar kwanyo.... Da wannan tunanin ta k’arasa d’akin Shuwa, sai a lokacin hawayen bak’in ciki suka samu nasarar zubo mata… Daga Shuwa sai Baabaa Talatu ne a d’akin suna shirya tukuicin da za a bayar in an kawo lefe. Baaba Talatu tana ganin ta shigo tana kuka ta mik’e tana “Subahanallah, mai ya faru? Ke da waye?” Da sauri ta k’arasa ta hau shafa fuskarta inda hannun Ummu ya fito tarr!! Ya kwanta akan farar fuskarta Cikin fad’a Baaba Talatun tace “Wanne d’an iskan ne ya mare ki??” Fashewa tayi da kuka cikin kukan tace “Umma ce take ta abubuwa a waje, shine Ummu ta mareni wai dan....” Ai bata tsaya jin k’arshen ba, tayi waje. Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina . Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba...........” BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 53 Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar, tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina. Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba.” “To” Kawai Sakina tace, tana mai sake goge fuskarta sannan ta koma gefe ta fara warware laffayar jikinta da d’aurin d’ankwalin dake kanta.. Sai da ya rage daga ita sai long camisole d’inta wadda ta saka a ciki mai dogon hannu yayinda dogon gashinta ya kwanta a gadon bayanta sannan ta fara k’ok’arin kiran Arshaad... Tayi mishi misscalls sun fi ashirin amman shiru. Dan haka nan da nan hankalinta ya sake tashi…. Tun jiya take danne zuciyarta take k’ok’arin kawar da maganar da Aaima ta gaya mata a cikin kwakwalwarta amman kuma attitude d’in Arshaad da k’in zuwanshi a yanzu ya yi matuk’ar bata tsoro. Ba wadda take jin fargabar taji wannan batu irin Hudan shiyasa jiya ta kwana Sallah akan Allah yasa maganar Aaima ta zama k’arya idan kuma gaskiyace Allah yasa su Abba su gyara lamarin cikin sauk’i… Gaba d’aya hankalinta a tashe yake dauriya ce kawai take yi, tana kuma k’ok’arin taga ba wanda ta bari ya ma ji zancen har a samu a gyara lamarin in sha Allah. Ganin arshaad d’in bashi da niyyar amsa ta ne yasa kawai ta kira Auwal dan taji me ke faruwa a ina aka tsaya.. Shi sai a bakinta ma yake jin wai ‘Arshaad d’in bai je ba’ Saboda shi suna asibiti. Ganin kamar bai san me yake faruwa ba ya sanya taja bakinta tayi shiru saboda ance yawan yayata magana kan iya tabbatar da gasgatuwar ta. Dan haka kawai sai tace mishi “ya duba musu Arshaad din pls” Daga haka suka yi sallama. Daman shima yana da shirinshi zai je wajen So yanzu zai duba Arshaad d’in sai su wuce tare kawai dan haka ya cewa Dad “Bara yaje gida, Sakina ta kirashi wai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96